< Amos 5 >

1 Listen to this word, which I lift over you in lamentation. The house of Israel has fallen, and it will no longer rise again.
Ku ji wannan magana, ya gidan Isra’ila, ina makokin nan dominku.
2 The virgin of Israel has been thrown onto her land, there is no one who can raise her up.
“Budurwa Isra’ila ta fāɗi, ba za tă ƙara tashi ba, an yashe ta a ƙasarta, ba wanda zai ɗaga ta.”
3 For thus says the Lord God: In the city from which a thousand departed, a hundred will remain, and in that from which a hundred departed, ten will remain, in the house of Israel.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Birnin da ta fitar da masu ƙarfi dubbai don Isra’ila guda ɗari kaɗai za su dawo; garin da ya fitar da masu ƙarfi ɗari kuwa goma kaɗai za su dawo.”
4 For thus says the Lord to the house of Israel: Seek me and you will live.
Ga abin da Ubangiji ya ce wa gidan Isra’ila. “Ku neme ni ku rayu;
5 But do not be willing to seek Bethel, and do not be willing to enter Gilgal, and you will not cross into Beer-sheba. For Gilgal will be led into captivity, and Bethel will be useless.
kada ku nemi Betel, kada ku je Gilgal, kada ku yi tafiya zuwa Beyersheba. Gama ba shakka Gilgal za tă tafi bauta, za a kuwa mai da Betel ba kome ba.”
6 Seek the Lord and live. Otherwise, the house of Joseph may be destroyed with fire, and it will devour, and there will be no one who can extinguish Bethel.
Ku nemi Ubangiji ku kuma rayu, ko kuwa zai ratsa yă share gidan Yusuf kamar wuta; zai cinye Betel kuwa ba zai sami wanda zai kashe ta ba.
7 You turn judgment into wormwood, and you abandon justice on earth.
Ku ne masu mai da gaskiya ta koma ɗaci ku kuma zubar da adalci.
8 The Maker of Arcturus and Orion, who turns darkness into daybreak and who changes day into night; who calls forth the waters of the sea and who pours them out over the face of the earth: The Lord is his name.
(Shi wanda ya yi Taurarin nan da ake ce Kaza da’Ya’yanta da kuma Mai Farauta da Kare, wanda ya mai da duhu ya zama haske ya kuma baƙanta rana ta zama dare, yakan kwashe ruwan teku ya zubar a ƙasa, Ubangiji ne sunansa,
9 It is he who smiles destruction on the healthy, and who brings pillaging upon the powerful.
yakan kawo hallaka a mafaka mai ƙarfi yakan kuma mai da birnin mai katanga ya zama kufai).
10 They held hatred for the one who corrects at the gate, and they have abhorred the one who speaks perfectly.
Ba ku son mai yin gaskiya a ɗakin shari’a kuna ƙin mai faɗar gaskiya.
11 Therefore, on his behalf, because you have torn apart the poor and stolen choice prey from him: you will build houses with square stones and you will not dwell in them; you will plant the most delightful vineyards, and you will not drink wine from them.
Kuna matsa wa matalauta kuna sa su dole su ba ku hatsi. Saboda haka, ko da yake kun gina gidajen duwatsu, ba za ku zauna a cikinsu ba; ko da yake kun nome gonaki masu kyau, ba za ku sha ruwan inabinsu ba.
12 For I know your many wicked deeds and the strength of your sins, you enemies of the just, accepting bribes, and depriving the poor at the gate.
Gama na san yawan laifofinku da kuma girman zunubanku. Kuna danne masu adalci kuna kuma cin hanci kuna kuma hana a yi wa matalauta shari’ar adalci a majalisa.
13 Therefore, the prudent will be silent at that time, for it is an evil time.
Saboda haka mai hankali yakan yi shiru a lokuta kamar haka, gama lokutan mugaye ne.
14 Seek good and not evil, so that you may live. And the Lord God of hosts will be with you, just as you have asked.
Ku yi nagarta, ba mugunta ba; don ku rayu sa’an nan Ubangiji Allah Maɗaukaki zai kasance da ku, kamar yadda kuka ce zai yi.
15 Hate evil and love good, and establish judgment at the gate. Perhaps then the Lord God of hosts may have mercy on the remnant of Joseph.
Ku ƙi mugunta, ku ƙaunaci nagarta; ku dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunan shari’a. Mai yiwuwa Ubangiji Allah Maɗaukaki zai ji tausayin raguwar Yusuf.
16 Therefore, thus says the Lord God of hosts, the Sovereign: In all the streets, there will be wailing. And in every place where they are outdoors, they will say, “Woe, woe!” And they will call the farmer to mourn, and those who know mourning to lamentation.
Saboda haka ga abin da Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Za a yi kururuwa a dukan tituna a kuma yi kuka don azaba a dukan wuraren da jama’a sukan taru. Za a yi kira ga manoma su yi kuka masu makoki kuma su yi kuka.
17 And in all the vineyards there will be wailing. For I will cross through your midst, says the Lord.
Za a yi kuka a dukan gonakin inabi, gama zan ratsa a cikinku,” in ji Ubangiji.
18 Woe to those who desire the day of the Lord. What is it to you? The day of the Lord is this: darkness and not light.
Kaitonku masu son ganin ranar Ubangiji! Don me kuke son ganin ranar Ubangiji? Za a duhunta ranan nan, ba haske ba.
19 It is as if a man flees from the face of a lion, only to have a bear meet him; or, he enters a house and leans with his hand against the wall, only to have a snake bite him.
Za ku zama kamar mutanen da suka guje wa zaki sai suka fāɗa a hannun beyar, ko kuma kamar wanda ya shiga gida ya dāfa hannu a bango sai maciji ya sare shi.
20 Will not the day of the Lord be darkness and not light, and gloom with no brightness in it?
Ashe, ranar Ubangiji ba duhu ba ce, a maimakon haske, duhu wuluk, ba tare da ko ɗan haske ba.
21 I hate and have rejected your feasts; and I will not accept the odor from your gatherings.
“Na ƙi, ina kuma ƙyamar bukukkuwanku na addini; ba na son ganin tarurrukanku.
22 For if you offer me holocausts and your gifts, I will not receive them; and I will not look upon the vows of your fatness.
Ko da kun kawo mini hadayu na ƙonawa da kuma hadayu na hatsi, ba zan karɓa ba. Ko da kun kawo zaɓaɓɓun hadayu na zumunta, ba zan ɗauke su a bakin kome ba.
23 Take away from me the tumult of your songs, and I will not listen to the canticles of your lyre.
Ku tashi daga nan da surutan waƙoƙinku! Ba zan saurari kaɗe-kaɗe da bushe bushenku ba.
24 And judgment will be revealed like water, and justice like a mighty torrent.
Amma bari gaskiya ta kwararo kamar kogi, adalci kuma kamar rafin da ba ya taɓa bushewa!
25 Was it you who offered victims and sacrifices to me in the desert for forty years, house of Israel?
“Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in a cikin jeji, ya ku gidan Isra’ila?
26 And you carried a tabernacle for your Moloch and the image of your idols: the star of your god, which you made for yourselves.
Kun ɗaga masujadar sarkinku, siffofin gumakanku, tauraron allahnku, wanda kuka yi wa kanku.
27 And I will cause you to go into captivity across Damascus, says the Lord. The God of hosts is his name.
Saboda haka zan tura ku zaman bauta gaba da Damaskus,” in ji Ubangiji, wanda sunansa ne Allah Mai Iko.

< Amos 5 >