< 2 Samuel 6 >

1 Then David again gathered together all the elect men of Israel, thirty thousand.
Dawuda ya sāke tattara zaɓaɓɓun mutanen Isra’ila, dubu talatin.
2 And David arose and went away, with the entire people who were with him from the men of Judah, so that they might lead back the ark of God, over which is invoked the name of the Lord of hosts, who sits upon the cherubim above it.
Shi, da dukan mutanensa suka tashi daga Ba’ala-Yahuda don su hauro da akwatin alkawarin Allah, wanda ake kira da SunanUbangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a tsakanin kerubobin da suke a kan akwatin alkawarin.
3 And they placed the ark of God on a new cart. And they took it from the house of Abinadab, who was in Gibeon. And Uzzah and Ahio, the sons of Abinadab, drove the new cart.
Suka ɗauko akwatin alkawarin Allah a sabuwar keken yaƙi, suka kawo shi daga gidan Abinadab, wanda yake bisa tudu. Uzza da Ahiyo,’ya’yan Abinadab maza, suka bi da keken yaƙin da akwatin alkawarin Allah yake ciki suka bi da keken yaƙin
4 And when they had taken it from the house of Abinadab, who was in Gibeon, Ahio preceded the ark as the keeper of the ark of God.
da akwatin alkawarin Allah yake ciki. Ahiyo kuwa yana tafiya a gaban Abinadab.
5 But David and all of Israel played before the Lord on every kind of musical instrument made of wood, and on harps, and lyres, and timbrels, and bells, and cymbals.
Dawuda da dukan gidan Isra’ila suka yi biki sosai da dukan ƙarfinsu a gaban Ubangiji, da waƙoƙi, da molaye, da garayu, da ganguna, da kacau-kacau da kuma kuge.
6 And after they had arrived at the threshing floor of Nacon, Uzzah extended his hand to the ark of God, and he touched it, because the oxen were kicking and had caused it to tip.
Da suka kai masussukar Nakon, sai Uzza ya miƙa hannu don yă riƙe akwatin alkawarin Allah, gama shanun sun yi tuntuɓe.
7 And the indignation of the Lord was enraged against Uzzah. And he struck him for his temerity. And there he died, beside the ark of God.
Fushin Ubangiji kuwa ya ƙuna a kan Uzza domin aikin rashin bangirma, saboda haka Allah ya buge shi ya kuma mutu a can kusa da akwatin alkawarin Allah.
8 Then David was saddened because the Lord had struck Uzzah. And the name of that place was called: the Striking of Uzzah, even to this day.
Ran Dawuda ya ɓace gama fushin Ubangiji ya ɓarke a kan Uzza. Shi ya sa har wa yau ana kira wurin Ferez Uzza.
9 And David was very fearful of the Lord on that day, saying, “How shall the ark of the Lord be brought to me?”
Dawuda ya ji tsoron Ubangiji a ranar, sai ya ce, “Yaya akwatin alkawarin Ubangiji zai iya zuwa wurina?”
10 And he was not willing to send the ark of the Lord to himself in the city of David. Instead, he sent it into the house of Obededom, the Gittite.
Bai so yă ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji yă kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka sai ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
11 And the ark of the Lord dwelt in the house of Obededom the Gittite, for three months. And the Lord blessed Obededom, and all his household.
Akwatin Alkawarin Ubangiji ya kasance a gidan Obed-Edom mutumin Gat har tsawon wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkace shi da dukan iyalinsa.
12 And it was reported to king David that the Lord had blessed Obededom, and all that was his, because of the ark of God. Therefore, David went and brought the ark of God, from the house of Obededom, into the city of David with joy. And there were with David seven choirs, and calves for victims.
To, sai aka faɗa wa Sarki Dawuda cewa, “Ubangiji ya sa wa gidan Obed-Edom albarka da dukan abin da yake da shi, saboda akwatin alkawarin Allah.” Saboda haka sai Dawuda ya gangara ya hauro da akwatin alkawarin Allah daga gidan Obed-Edom zuwa Birnin Dawuda da farin ciki.
13 And when those who were carrying the ark of the Lord had traveled six steps, he immolated an ox and a ram.
Sa’ad da waɗanda suke ɗaukan akwatin alkawarin Ubangiji suka yi tafiya taki shida, sai yă yi hadayar bijimi da saniya mai ƙiba.
14 And David danced with all his ability before the Lord. And David was girded with the linen ephod.
Dawuda, sanye da efod lilin, ya yi ta rawa a gaban Ubangiji da dukan ƙarfinsa,
15 And David, and all the house of Israel, were leading the ark of the testament of the Lord, with jubilation and the sound of the trumpet.
yayinda shi da dukan gidan Isra’ila suka hauro da akwatin alkawarin Ubangiji da sowa da kuma busar ƙahoni.
16 And when the ark of the Lord had entered into the city of David, Michal, the daughter of Saul, looking out through a window, saw king David leaping and dancing before the Lord. And she despised him in her heart.
Sa’ad da akwatin alkawarin Ubangiji ya shiga Birnin Dawuda, sai Mikal’yar Shawulu ta leƙa ta taga ta ga Dawuda sarki yana tsalle, yana rawa a gaban Ubangiji, sai ta rena shi a zuciyarta.
17 And they led in the ark of the Lord. And they set it in its place in the middle of the tabernacle, which David had pitched for it. And David offered holocausts and peace offerings in the sight of the Lord.
Suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji, aka ajiye shi a inda aka shirya masa a cikin tentin da Dawuda ya shirya dominsa. Dawuda kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama a gaban Ubangiji.
18 And when he had completed offering holocausts and peace offerings, he blessed the people in the name of the Lord of hosts.
Bayan ya gama yin hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji Maɗaukaki.
19 And he distributed to the entire multitude of Israel, as much to men as to women, to each one: one loaf of bread, and one piece of roasted beef, and fine wheat flour fried with oil. And all the people went away, each one to his own house.
Sa’an nan ya rarraba abinci, da ƙosai, dabino, da waina ga kowane mutum a cikin dukan jama’ar Isra’ila, maza da mata. Dukan mutane kuwa suka watse zuwa gidajensu.
20 And David returned, so that he might bless his own house. And Michal, the daughter of Saul, going out to meet David, said: “How glorious was the king of Israel today, uncovering himself before the handmaids of his servants, and being unclothed, as if one of the performers were unclothed.”
Da Dawuda ya koma gida don yă sa wa gidansa albarka, sai Mikal’yar Shawulu ta fito don tă tarye shi, sai ta ce, “Tabbas sarkin Isra’ila ya fiffita kansa yau, ya tuɓe a gaban bayinsa’yan mata, kamar yadda duk marar kunya yakan yi!”
21 And David said to Michal: “Before the Lord, who chose me rather than your father, and rather than his entire house, and who commanded me, that I should be the leader over the people of the Lord in Israel,
Dawuda ya ce wa Mikal, “Na yi rawana domin in girmama Ubangiji ne, wanda ya zaɓe ni a maimakon mahaifinki ko wani daga cikin dukan gidansa, shi ne kuma ya sa ni sarki a kan Isra’ila, mutanen Ubangiji, zan yi biki a gaban Ubangiji.
22 I will both play and demean myself, more so than I have done. And I will be little in my own eyes. And with the handmaids, about whom you are speaking, I will appear more glorious.”
Zan ma mai da kaina abin reni fiye da haka, za a kuma zama abin reni a gare ki. Amma waɗannan bayi’yan matan da kika yi magana a kai, za su gan ni da martaba.”
23 And so, there was no child born to Michal, the daughter of Saul, even to the day of her death.
Mikal’yar Shawulu kuwa ba tă haifi ɗa ba har mutuwarta.

< 2 Samuel 6 >