< 2 Samuel 5 >

1 And all the tribes of Israel went to David in Hebron, saying: “Behold, we are your bone and your flesh.
Dukan kabilar Isra’ila suka zo wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu nama da jininka ne.
2 Moreover, yesterday and the day before, when Saul was king over us, you were the one leading out and leading back Israel. Then the Lord said to you, ‘You shall pasture my people Israel, and you shall be the leader over Israel.’”
A dā da Shawulu yake sarauta a bisanmu, kai ne kake bi Isra’ilawa zuwa yaƙe-yaƙensu. Ubangiji kuwa ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayi mutanena Isra’ila, za ka kuma zama sarkinsu.’”
3 Also, the elders of Israel went to the king at Hebron, and king David struck a pact with them at Hebron in the sight of the Lord. And they anointed David as king over Israel.
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, sarki ya yi yarjejjeniya da su a gaban Ubangiji, suka kuwa naɗa Dawuda sarki bisa Isra’ila.
4 David was a son of thirty years, when he had begun to reign, and he reigned for forty years.
Dawuda yana da shekara talatin ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara arba’in.
5 In Hebron, he reigned over Judah for seven years and six months. Then in Jerusalem, he reigned for thirty-three years over all of Israel and Judah.
A Hebron ya yi mulki a bisa Yahuda shekara bakwai da wata shida, a Urushalima kuma ya yi mulki a bisa Isra’ila da Yahuda shekara talatin da uku.
6 And the king, and all the men who were with him, went away to Jerusalem, to the Jebusites, the inhabitants of the land. And it was said to David by them, “You shall not enter here, unless you will take away the blind and the lame, who say, ‘David shall not enter here.’”
Sarki da mutanensa suka tafi Urushalima don su kai wa Yebusiyawan da suke zaune a can hari, Yebusiyawa suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba; ko makafi da guragu kaɗai ma za su kore ka.” Suka yi tsammani suna cewa, “Dawuda ba zai iya shiga can ba.”
7 But David seized the stronghold of Zion; the same is the city of David.
Duk da haka, Dawuda ya kame kagarar Sihiyona, wadda ta zama Birnin Dawuda.
8 For David had proposed, on that day, a reward to him who had struck the Jebusites and who had reached to the gutters of the rooftops, and who had taken away the blind and the lame that hated the soul of David. Therefore, it is said in the proverb, “The blind and the lame shall not enter into the temple.”
A ranar, Dawuda ya ce, “Duk wanda zai kame Yebusiyawa, dole yă yi amfani da wuriyar ruwa don yă kai ga waɗannan ‘guragu da makafi’ waɗanda suke abokan gāban Dawuda.” Shi ya sa suka ce, “‘Makafi da guragu’ ba za su shiga fadan sarki ba.”
9 Then David lived in the stronghold, and he called it: the City of David. And he built it up on all sides, from Millo and inward.
Sai Dawuda ya zauna a kagarar, ya kuma kira ta Birnin Dawuda. Ya gina wuraren da suke kewaye da ita, tun daga madogaran gini zuwa ciki.
10 And he advanced, prospering and increasing, and the Lord, the God of hosts, was with him.
Ya yi ta ƙara ƙarfi, gama Ubangiji Allah Maɗaukaki yana tare da shi.
11 Also, Hiram, the king of Tyre, sent messengers to David, with cedar wood, and with builders of wood and builders of stone, in order to make walls. And they built a house for David.
To, Hiram sarkin Taya ya aiki manzanni wurin Dawuda tare da gumaguman itacen al’ul, da kafintoci, da kuma maginan duwatsu, suka kuwa gina wa Dawuda fada.
12 And David knew that the Lord had confirmed him as king over Israel, and that he had exalted his kingdom over his people Israel.
Dawuda kuwa ya gane Ubangiji ya naɗa shi sarki bisa Isra’ila, ya kuma ɗaukaka masarautarsa saboda mutanensa Isra’ila.
13 Then David took more concubines and wives from Jerusalem, after he had arrived from Hebron. And other sons as well as daughters were born to David.
Bayan ya bar Hebron, Dawuda ya ƙara ɗauko wa kansa waɗansu ƙwarƙwarai da mata a Urushalima. Aka haifa masa’ya’ya maza da mata.
14 And these are the names of those who were born to him in Jerusalem: Shammua, and Shobab, and Nathan, and Solomon,
Waɗannan su ne sunayen’ya’yan da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
15 and Ibhar, and Elishua, and Nepheg,
Ibhar, Elishuwa, Nefeg, Yafiya,
16 and Japhia, and Elishama, and Eliada, and Elipheleth.
Elishama, Eliyada da Elifelet.
17 Then the Philistines heard that they had anointed David as king over Israel. And they all ascended, so that they might seek David. And when David had heard of it, he descended to a stronghold.
Da Filistiyawa suka ji labari an shafe Dawuda sarki a bisa Isra’ila, sai suka haura da ƙarfi sosai don su nema shi, amma Dawuda ya ji labarin sai ya gangara zuwa mafaka.
18 Now the Philistines, arriving, spread themselves out in the Valley of Rephaim.
To, fa, Filistiyawa suka zo suka baje ko’ina a cikin Kwarin Refayim;
19 And David consulted the Lord, saying: “Shall I ascend to the Philistines? And will you give them into my hand?” And the Lord said to David: “Ascend. For I will certainly give the Philistines into your hand.”
saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji ya ce, “In tafi in kai wa Filistiya hari? Za ka bashe su a hannuna?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Je ka, gama tabbatacce zan bashe Filistiyawa a hannunka.”
20 Therefore, David went to Baal-perazim. And he struck them there. And he said, “The Lord has divided my enemies before me, just as the waters are divided.” Because of this, the name of that place was called Baal-perazim.
Saboda haka Dawuda ya tafi Ba’al-Ferazim, a can ya ci su da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa yakan fasu, haka Ubangiji ya kakkarya abokan gābana a gabana.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
21 And in that place they left behind their graven images, which David and his men took away.
Filistiyawa suka bar gumakansu a can, Dawuda da mutanensa kuwa suka kwashe su.
22 And the Philistines continued still, so that they ascended and spread themselves out in the Valley of Rephaim.
Har yanzu Filistiyawa suka sāke haurawa suka bazu a Kwarin Refayim;
23 Then David consulted the Lord, “Shall I ascend against the Philistines, and will you deliver them into my hands?” And he responded: “You shall not ascend against them; instead, circle behind their back. And you shall come to them from the side opposite the balsam trees.
saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya kuwa ce, “Kada ka haura kai tsaye, amma ka kewaya ta bayansu ka fāɗa musu a gaban itatuwan balsam.
24 And when you hear the sound of something going forth from the tops of the balsam trees, then you shall begin the battle. For then the Lord will go forth, before your face, so that he may strike the army of the Philistines.”
Da zarar ka ji tafiya kamar na takawar sojoji tana a bisan itatuwan balsam, sai ka yi maza, gama wannan alama ce cewa Ubangiji ya sha gabanka don yă karkashe sojojin Filistiyawa.”
25 And so, David did just as the Lord had instructed him. And he struck down the Philistines, from Gibeon until you arrive at Gezer.
Saboda haka Dawuda ya aikata yadda Ubangiji ya umarce shi, ya kuma karkashe Filistiyawa tun daga Geba har zuwa Gezer.

< 2 Samuel 5 >