< 2 Kings 25 >

1 Then it happened that, in the ninth year of his reign, in the tenth month, on the tenth day of the month, Nebuchadnezzar, the king of Babylon, he and his entire army, arrived against Jerusalem. And they encircled it, and they constructed fortifications all around it.
A rana ta goma ga wata na goma, a shekara ta tara ta mulkin Zedekiya ne Nebukadnezzar sarkin Babilon tare da dukan rundunan yaƙinsa, ya tasam wa Urushalima. Ya yi sansani a bayan birnin, ya kewaye ta da shirin yaƙi.
2 And the city was enclosed and besieged, even until the eleventh year of king Zedekiah,
Haka birnin ta kasance a kewaye har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya.
3 on the ninth day of the month. And a famine prevailed in the city; neither was there bread for the people of the land.
A rana ta tara ta watan huɗu, lokacin da yunwa ta yi tsanani a birnin, babu kuma abinci domin mutane su ci.
4 And the city was breached. And all the men of war fled in the night along the way of the gate which is between the double wall at the garden of the king. Now the Chaldeans were besieging the city on all sides. And so Zedekiah fled along the way which leads to the plains of the wilderness.
Sai aka huda katanga sa’an nan dukan sojoji suka tsere da dare a ƙofa tsakanin katanga biyu da suke kusa da lambun sarki, ko da yake Babiloniyawa sun kewaye birnin. Suka tsere suka nufi Araba.
5 And the army of the Chaldeans pursued the king, and they overtook him in the plains of Jericho. And all the warriors who were with him were dispersed, and they abandoned him.
Amma sojojin Babiloniyawa suka bi sarki, suka cin masa a filayen Yeriko. Dukan sojojinsa kuwa suka rabu da shi suka watse.
6 Therefore, having apprehended him, they led the king to the king of Babylon at Riblah. And he was speaking with him in judgment.
Aka kama shi, aka kai shi gaban sarkin Babilon a Ribla, inda aka yanke masa hukunci.
7 Then he killed the sons of Zedekiah before him, and he dug out his eyes, and he bound him with chains, and he led him away to Babylon.
Suka kashe’ya’yan Zedekiya a gabansa, sa’an nan aka ƙwaƙule idanunsa. Suka daure shi da sarƙar tagulla, suka kai shi Babilon.
8 In the fifth month, on the seventh day of the month, the same is the nineteenth year of the king of Babylon, Nebuzaradan, the leader of the army, a servant of the king of Babylon, went into Jerusalem.
A rana ta bakwai na watan biyar, wadda ta zama shekara ta goma sha tara ta mulkin Sarki Nebukadnezzar na Babilon, Nebuzaradan, babban hafsan matsaran sarki, kuma bafadan sarkin Babilon, ya zo Urushalima
9 And he set fire to the house of the Lord, and to the house of the king. And the houses of Jerusalem, and every great house, he burned with fire.
Ya cinna wa haikalin Ubangiji wuta, da fadan sarki, da kuma dukan gidajen Urushalima. Ya kuma ƙone duk wani gini mai muhimmanci.
10 And the entire army of the Chaldeans, which was with the leader of the military, tore down the walls of Jerusalem all around.
Dukan mayaƙan Babilon a ƙarƙashin umarnin babban hafsan matsaran sarki, suka rushe katangar Urushalima.
11 Then Nebuzaradan, the leader of the military, carried away the rest of the people, who had remained in the city, and the fugitives, who had fled over to the king of Babylon, and the remnant of the common people.
Nebuzaradan babban hafsan matsaran, ya kwashi waɗanda suka rage a cikin birnin, tare da sauran jama’a, da waɗanda suka miƙa kansu ga sarkin Babilon, ya kai su bauta.
12 But he left behind some vinedressers and farmers from the poor of the land.
Amma hafsan ya bar waɗansu daga cikin mafiya talauci na ƙasar don su yi aiki a lambunan inabi da kuma gonaki.
13 Now the pillars of brass which were in the temple of the Lord, and the bases, and the sea of brass, which was in the house of the Lord, the Chaldeans broke apart. And they took all the brass to Babylon.
Babiloniyawan kuma suka sassare ginshiƙan tagulla, da wuraren zama da za a iya matsar da su, da ƙaton kwano mai suna Teku na tagulla da yake a haikalin Ubangiji, suka kwashe tagullan zuwa Babilon.
14 Also, they took away the cooking pots of brass, and the scoops, and the forks, and the cups, and the little mortars, and all the articles of brass with which they were ministering.
Suka ɗauke tukwane, da manyan cokula, da acibalbal, da kwanoni, da dai dukan kayan da aka yi da tagulla don hidima a haikalin Ubangiji.
15 And the leader of the military even took away the censers and the bowls, whatever was of gold for the gold, and whatever was of silver for the silver,
Babban hafsan matsaran sarkin ya kwashe har da kwanoni na kwashe garwashin wuta da sauran kwanoni, dukansu kuwa ƙeran zinariya ko azurfa tsatsa ne.
16 and also the two pillars, the one sea, and the bases which Solomon had made for the temple of the Lord. The brass of all these items was beyond measure.
Tagullar ginshiƙai biyun nan, da ta ƙaton kwanon da ake ce da shi Teku, da ta dukan amalanke masu riƙe ruwa waɗanda Sarki Solomon ya yi domin haikalin Ubangiji, sun fi gaba a auna su.
17 One pillar had eighteen cubits in height. And the head of brass upon it was three cubits in height. And the network and pomegranates upon the head of the pillar were all of brass. And the second pillar had a similar adornment.
Tsawon kowane ginshiƙi, ƙafa ashirin da bakwai ne. Hulunan tagullan da suke ƙwalƙwalin kowane ginshiƙi kuma yana da tsawon ƙafa huɗu da rabi. Kuma aka yi masa ado da saƙa da’ya’yan itace kewaye da shi. Bayan ginshiƙin ma haka yake.
18 Also, the leader of the military took away Seraiah, the chief priest, and Zephaniah, the second priest, and three doorkeepers,
Babban hafsan ya kwashi Serahiya babban firist, da Zefaniya na biye da shi a girma, da matsara ƙofofi uku.
19 and from the city, one eunuch, who was in charge of the men of war, and five men out of those who had stood before the king, whom he found in the city, and Sopher, the leader of the army who trained the young soldiers from the people of the land, and sixty men from the common people, who had been found in the city.
Daga cikin waɗanda suka rage a birnin, ya ɗauki hafsa mai kula da dakaru, da kuma mashawartan sarki guda biyar. Ya kuma tafi da magatakarda wanda yake babban jami’in soja mai ɗaukan dukan jama’an ƙasar, tare da mutanensa guda sittin waɗanda aka samu a birnin.
20 Taking them, Nebuzaradan, the leader of the military, led them to the king of Babylon at Riblah.
Nebuzaradan, babban hafsan, ya kwashe su duka ya kawo su wurin sarkin Babilon a Ribla.
21 And the king of Babylon struck them and killed them at Riblah, in the land of Hamath. And Judah was taken away from his land.
A can Ribla, a ƙasar Hamat, sarkin Babilon ya sa aka kashe su. Haka Yahuda ta tafi bauta daga ƙasarta.
22 But over the people who had remained in the land of Judah, whom Nebuchadnezzar, the king of Babylon, had permitted, he appointed as ruler Gedaliah, the son of Ahikam, the son of Shaphan.
Nebukadnezzar sarkin Babilon ya zaɓi Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan yă zama shugaban sauran mutanen da suka rage a Yahuda.
23 And when all the commanders of the military had heard this, they and the men who were with them, specifically, that the king of Babylon had appointed Gedaliah, they went to Gedaliah at Mizpah: Ishmael, the son of Nethaniah, and Johanan, the son of Kareah, and Seraiah, the son of Tanhumeth, the Netophathite, and Jaazaniah, the son of a Maacathite, they and their companions.
Sa’ad da dukan hafsoshin soja tare da mutanensu suka ji cewa sarkin Babilon ya naɗa Gedaliya a matsayin gwamna, sai suka zo wurin Gedaliya a Mizfa. Mutanen da suka zo su ne, Ishmayel ɗan Netaniya, Yohanan ɗan Kareya, Serahiya ɗan Tanhumet mutumin Netofa, Ya’azaniya ɗan mutumin Ma’aka, tare da mutanensu.
24 And Gedaliah swore to them and to their companions, saying: “Do not be afraid to serve the Chaldeans. Remain in the land, and serve the king of Babylon, and it shall be well with you.”
Gedaliya ya tabbatar musu da rantsuwa cewa, “Kada ku ji tsoron jama’ar Babiloniyawa, muddin kun zauna lafiya, kun kuma bauta wa sarkin Babilon, kome zai yi muku kyau.”
25 But it happened that, in the seventh month, Ishmael, the son of Nethaniah, the son of Elishama, of royal offspring, and ten men with him, went and struck Gedaliah, who then died, along with the Jews and the Chaldeans who were with him at Mizpah.
Amma a wata na bakwai, sai Ishmayel, ɗan Netaniya, ɗan Elishama, wanda yake daga gidan sarauta, ya zo tare da mutane goma, suka kashe Gedaliya duk da mutanen Yahuda, da na Babilon da suke tare da shi na Mizfa.
26 And all the people, from small to great, and the leaders of the military, rising up, went away to Egypt, fearing the Chaldeans.
Ganin haka sai dukan mutane, babba da ƙarami, tare da shugabannin sojoji, suka tashi suka gudu zuwa ƙasar Masar, gama suna tsoron mutanen Babilon.
27 Truly, it happened that, in the thirty-seventh year of the transmigration of Jehoiachin, the king of Judah, in the twelfth month, on the twenty-seventh day of the month, Evilmerodach, the king of Babylon, in the year when he had begun to reign, lifted up the head of Jehoiachin, the king of Judah, from prison.
A shekara ta talatin da bakwai ta bautar Yehohiyacin sarkin Yahuda, a shekaran da Ewil-Merodak ya ci sarautan Babilon, sai ya saki Yehohiyacin daga jaru, ya sake shi a rana ashirin da bakwai ga watan goma sha biyu.
28 And he spoke kindly to him. And he set his throne above the throne of the kings who were with him at Babylon.
Ya yi wa Yehohiyacin maganar alheri, ya kuma ɗaukaka shi sama da sauran sarakunan da suke tare da shi a Babilon.
29 And he changed his garments that he had worn in prison. And he ate bread before him always, during all the days of his life.
Don haka Yehohiyacin ya tuɓe kayan fursuna. Kowace rana kuwa yakan ci abinci a teburin sarki har iyakar ransa.
30 Also, he appointed to him an allowance without ceasing, which also was given to him by the king, for each day, during all the days of his life.
Sarki kuma ya yanka masa kuɗin da za a dinga ba shi, kowace rana muddin ransa.

< 2 Kings 25 >