< 2 Kings 12 >

1 In the seventh year of Jehu, Jehoash reigned. And he reigned for forty years in Jerusalem. The name of his mother was Zebiah from Beersheba.
A shekara ta bakwai ta Yehu, Yowash ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima na tsawon shekaru arba’in. Sunan mahaifiyarsa Zibiya ce; daga Beyersheba.
2 And Jehoash did what was right in the sight of the Lord, during all the days that Jehoiada, the priest, taught him.
Yowash ya aikata abin da yake daidai a idon Ubangiji domin Yehohiyada firist ya koya masa.
3 Yet still he did not take away the high places. For the people were still immolating, and burning incense, in the high places.
Amma fa ba a kawar da masujadan kan tuddai ba; mutane suka ci gaba da miƙa hadayu da kuma ƙona turare a kan tuddai.
4 And Jehoash said to the priests: “All of the money for the holy things, which has been brought into the temple of the Lord from those who pass by, which is offered for the price of a soul, and which they bring into the temple of the Lord willingly, from their own free heart:
Yowash ya ce wa firistoci, “Ku tattara dukan kuɗin da ake kawo a matsayin hadayu masu tsarki na haikalin Ubangiji, kuɗin da aka tattara a ƙidaya, kuɗin da aka tattara daga wa’adin da mutum ya yi, da kuma kuɗin da aka kawo na yardan rai a haikali.
5 let the priests, according to their ranks, take and use it in order to repair the surfaces of the house, wherever they see anything in need of repair.”
Bari kowane firist yă karɓi kuɗi daga masu ajiya, sa’an nan a yi amfani da su a gyara duk wani abin da ya lalace a haikali.”
6 And yet, even until the twenty-third year of king Jehoash, the priests did not repair the surfaces of the temple.
Amma har zuwa shekara ta ashirin da uku ta mulkin Yowash, firistocin ba su yi gyara haikalin ba.
7 And king Jehoash called the high priest, Jehoiada, and the priests, saying to them: “Why have you not repaired the surfaces of the temple? Therefore, you may no longer accept money according to your ranks. Instead, return it in order that the temple may be repaired.”
Saboda haka Sarki Yowash ya kira Yehohiyada firist da sauran firistoci ya tambaye su ya ce, “Me ya sa ba kwa gyaran abubuwan da suka lalace a haikali? Kada ku sāke karɓan kuɗi daga masu ajiya, amma a miƙa su domin gyaran haikali.”
8 And so the priests were prohibited from accepting any more money from the people to repair the surfaces of the house.
Firistoci suka yarda cewa ba za su sāke karɓan kuɗi daga mutane ba, kuma ba za su yi gyaran haikalin da kansu ba.
9 And the high priest, Jehoiada, took a certain chest, and he opened a hole in the top, and he placed it beside the altar, to the right of those who were entering the house of the Lord. And the priests who kept the doors put all the money in it which was being brought into the temple of the Lord.
Yehohiyada firist ya ɗauki akwatin ya huda rami a murfinsa. Ya ajiye shi kusa da bagade a hannun dama na haikalin Ubangiji. Firistocin da suke tsaron ƙofar suka zuba dukan kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji a cikin akwatin.
10 And when they saw that there was a great amount of money in the chest, the scribe of the king and the high priest went up and poured it out. And they counted the money that was found in the house of the Lord.
Duk sa’ad da suka ga kuɗin sun ƙaru a akwatin, sai marubucin fada da babban firist, su ƙirga kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji su sa a jakankuna.
11 And they gave it out, by number and measure, to the hands of those who were over the masons of the house of the Lord. And they weighed it out to the carpenters and masons, to those who were working in the house of the Lord
Sa’ad da suka ga kuɗin ya yi yawa, sai su ba wa waɗanda aka zaɓa su lura da aikin haikalin. Da shi suka biya waɗanda suka yi aiki a haikalin Ubangiji, su kafintoci, da magina,
12 and restoring the surfaces, and to those who were cutting stones, and buying timber and stones to be cut, so that the repairs to the house of the Lord might be finished: for all that was needed toward the expenses in order to strengthen the house.
masu gini, da masu fasa duwatsu. Suka sayi katakai da sassaƙaƙƙun duwatsu domin gyaran haikalin Ubangiji, suka kuma biya duk waɗansu kuɗin gyaran haikalin.
13 Yet truly, from the same money, they did not make for the temple of the Lord water pitchers, or small hooks, or censers, or trumpets, or any vessel of gold or silver, from the money that was brought into the temple of the Lord.
Ba a yi amfani da kuɗin da aka kawo a haikali don yin manyan kwanonin azurfa, lagwani, abin yayyafa ruwa, kakaki ko wani abu na zinariya, ko na azurfa domin haikalin Ubangiji ba;
14 For it was given to those who were doing the work, so that the temple of the Lord might be repaired.
an ba ma’aikatan da suka gyara haikalin ne.
15 And they did not ration the money to the men who received it in order to distribute it to the artisans. Instead, they bestowed it with faith.
Ba su bukaci wani bayani daga waɗanda aka ba wa kuɗin don su biya ma’aikatan ba, domin sun yi aikinsu da aminci.
16 Yet truly, the money for offenses and the money for sins, they did not bring into the temple of the Lord, since it was for the priests.
Ba a kawo kuɗi daga hadayun laifi da na hadayun zunubi a haikalin Ubangiji ba, waɗannan na firistoci ne.
17 Then Hazael, the king of Syria, ascended and fought against Gath, and he captured it. And he directed his face, so that he might ascend against Jerusalem.
A wannan lokaci, Hazayel sarkin Aram ya haura, ya kai wa Gat hari, ya kuma ci ta da yaƙi. Sa’an nan ya juya don yă yaƙi Urushalima.
18 For this reason, Jehoash, the king of Judah, took all the sanctified things, which Jehoshaphat, and Jehoram, and Ahaziah, his fathers, the kings of Judah, had consecrated and which he himself had offered, and all the silver that could be found in the treasuries of the temple of the Lord and in the palace of the king, and he sent it to Hazael, the king of Syria. And so he withdrew from Jerusalem.
Amma Yowash sarkin Yahuda ya kwashe tsarkakan kayan da kakanninsa, Yehoshafat, Yehoram da Ahaziya, sarakunan Yahuda suka keɓe, da kyautai da shi kansa ya keɓe, da kuma dukan azurfan da aka samu a ɗakunan ajiya haikalin Ubangiji da na fada, ya aika da su wa Hazayel sarkin Aram, shi kuma ya janye daga Urushalima.
19 Now the rest of the words of Jehoash, and all that he did, have these not been written in the book of the words of the days of the kings of Judah?
Game da sauran ayyukan mulkin Yowash da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
20 Then his servants rose up and conspired among themselves. And they struck down Jehoash, at the house of Millo, on the descent of Silla.
Hafsoshinsa suka yi masa maƙarƙashiya suka kashe shi a Bet Millo, a kan hanyar da ta gangara zuwa Silla.
21 For Jozacar, the son of Shimeath, and Jehozabad, the son of Shomer, his servants, struck him, and he died. And they buried him with his fathers in the city of David. And Amaziah, his son, reigned in his place.
Hafsoshin da suka kashe shi kuwa su ne Yozabad ɗan Shimeyat da Yehozabad ɗan Shomer. Ya mutu, aka kuma binne shi tare da kakanninsa a Birnin Dawuda. Sai Amaziya ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.

< 2 Kings 12 >