< 2 Kings 11 >

1 Truly, Athaliah, the mother of Ahaziah, seeing that her son was dead, rose up and put to death all the royal offspring.
Da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga ɗanta ya mutu, sai ta shiga hallaka dukan iyalin gidan sarauta.
2 But Jehosheba, the daughter of king Joram, the sister of Ahaziah, taking Jehoash, the son of Ahaziah, stole him away from the midst of the sons of the king who were being killed, out of the bedroom, with his nurse. And she hid him from the face of Athaliah, so that he would not be killed.
Amma Yehosheba,’yar Sarki Yoram,’yar’uwar Ahaziya, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya daga cikin’ya’yan sarkin da ake shiri a kashe, ta ɓoye. Ta ɓoye shi daga Ataliya a wurin mai lura da shi a ɗakin kwana; don kada a kashe shi.
3 And he was with her for six years, hidden in the house of the Lord. But Athaliah reigned over the land.
Ya kasance a ɓoye, shi da mai lura da shi, a haikalin Ubangiji shekara shida yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.
4 Then, in the seventh year, Jehoiada sent for and took centurions and soldiers, and he brought them to himself in the temple of the Lord. And he formed a pact with them. And taking an oath with them in the house of the Lord, he revealed to them the son of the king.
A shekara ta bakwai sai Yehohiyada ya aika a kira komandodin sojoji ɗari-ɗari, da Keretawa, da matsara, ya sa aka kawo masa su a haikalin Ubangiji. Ya ƙulla yarjejjeniya da rantsuwa da su a haikalin Ubangiji, sa’an nan ya nuna musu ɗan sarki.
5 And he commanded them, saying: “This is the word that you must do.
Ya umarce su cewa, “Ga abin da za ku yi sa’ad da kuka zo aiki a Asabbaci, ku raba kanku kashi uku. Kashi ɗaya za su yi gadin gidan sarki,
6 Let one third part of you enter on the Sabbath, and keep watch on the house of the king. And let one third part be at the gate of Sur. And let one third part be at the gate behind the dwelling place of the shield bearers. And you shall keep the watch on the house of Mesha.
kashi ɗaya za su yi gadin Ƙofar Sur, kashi ɗaya kuma za su yi gadin ƙofar da take bayan’yan gadin fada. Dukan waɗannan ƙungiyoyi uku za su yi gadin fadan,
7 Yet truly, let two parts of you, all who depart on the Sabbath, keep watch over the house of the Lord concerning the king.
ku kuma da kuke a sauran ƙungiyoyi biyu da kun saba hutu a Asabbaci, duk za ku yi gadin haikali don sarki.
8 And you shall surround him, having weapons in your hands. But if anyone will have entered the precinct of the temple, let him be killed. And you shall be with the king, entering and departing.”
Ku tsaya kewaye da sarki, kowane mutum da makaminsa a hannu. Duk wanda ya kusace ku, ku kashe shi. Ku manne wa sarki duk inda ya tafi.”
9 And the centurions acted in accord with all the things that Jehoiada, the priest, had instructed them. And taking each one of their men who would enter on the Sabbath, with those who would depart on the Sabbath, they went to Jehoiada, the priest.
Komandodin sojoji suka yi yadda Yehohiyada firist ya umarta. Kowa ya ɗauki mutanensa, waɗanda za su kama aiki Asabbaci da waɗanda za su kama hutun Asabbaci, suka zo wurin Yehohiyada firist.
10 And he gave to them the spears and weapons of king David, which were in the house of the Lord.
Sai ya ba komandodin māsu da garkuwoyi da dā suke na Dawuda, waɗanda suke a cikin haikalin Ubangiji.
11 And they stood, each one having his weapons in his hand, before the right side of the temple, all the way to the left side of the altar and of the shrine, surrounding the king.
Matsaran kuma kowa da makaminsa a hannu, suka tsaya kewaye da sarki, kusa da bagade da kuma haikali, daga gefen kudu zuwa gefen arewa na haikalin.
12 And he led forth the son of the king. And he placed the diadem on him, and the testimony. And they made him king, and they anointed him. And clapping their hands, they said: “The king lives!”
Sai Yehohiyada ya fito da ɗan sarki ya sa masa rawani a kā; ya ba shi shafin alkawari, ya kuma furta shi sarki. Suka shafe shi da mai, mutane kuma suka yi ta tafi suka ihu, suna cewa, “Ran sarki yă daɗe.”
13 Then Athaliah heard the sound of the people running. And entering to the crowd at the temple of the Lord,
Sa’ad da Ataliya ta ji surutun matsara da na mutane, sai ta tafi wurin mutanen a haikalin Ubangiji.
14 she saw the king standing upon a tribunal, according to custom, and the singers and trumpets near him, and all the people of the land rejoicing and sounding the trumpets. And she tore her garments, and she cried out: “Conspiracy! Conspiracy!”
Da ta duba sai ga sarki, tsaye kusa da ginshiƙi, bisa ga al’ada. Hafsoshi da masu busa suna tsaye kusa da sarki, dukan mutanen ƙasar kuma suna farin ciki suna busa ƙahoni. Sai Ataliya ta keta tufafinta ta tā da murya tana cewa, “Kai! Wannan cin amana ne! Ai, wannan cin amana ne!”
15 But Jehoiada gave orders to the centurions who were over the army, and he said to them: “Lead her away, beyond the precinct of the temple. And whoever will have followed her, let him be struck with the sword.” For the priest had said, “Do not allow her to be killed in the temple of the Lord.”
Yehohiyada ya umarci komandodin sojoji waɗanda suke lura da mayaƙa, ya ce, “Ku fitar da ita daga cikinku, ku kuma kashe duk wanda ya bi ta.” Gama firist ɗin ya ce, “Kada a kashe ta a cikin haikalin Ubangiji.”
16 And they laid hands on her. And they pushed her through the way by which horses enter, beside the palace. And she was killed there.
Saboda haka suka kama ta yayinda ta kai inda dawakai sukan shiga filin fada, a can kuwa aka kashe ta.
17 Then Jehoiada formed a covenant between the Lord, and the king and the people, so that they would be the people of the Lord; and between the king and the people.
Sa’an nan Yehohiyada ya yi alkawari tsakanin Ubangiji da sarki da kuma mutane cewa za su zama mutanen Ubangiji. Ya kuma yi alkawari tsakanin sarki da mutane.
18 And all the people of the land entered the temple of Baal, and they tore down his altars, and they thoroughly crushed the statues. Also, they killed Mattan, the priest of Baal, before the altar. And the priest placed guards in the house of the Lord.
Sai dukan mutanen ƙasar suka tafi haikalin Ba’al suka rushe shi. Suka farfasa bagadai da kuma gumaka, suka kuma kashe Mattan wanda yake firist na Ba’al a gaban bagade. Sa’an nan Yehohiyada firist ya sa matsara a haikalin Ubangiji.
19 And he took the centurions, and the legions of the Cherethites and Pelethites, and all the people of the land, and together they led the king from the house of the Lord. And they went by way of the gate of the shield bearers into the palace. And he sat upon the throne of the kings.
Ya tafi tare da komandodin sojoji, Keretawa, matsara da kuma dukan mutanen ƙasar, tare kuwa suka kawo sarki daga haikalin Ubangiji zuwa cikin fada, ta ƙofar matsara. Sarki kuwa ya ɗauki mazauninsa a bisa kursiyin sarauta,
20 And all the people of the land rejoiced. And the city was quieted. But Athaliah was slain with the sword at the house of the king.
dukan mutanen ƙasar suka yi murna. Birnin ya sami salama don an kashe Ataliya da takobi a fada.
21 Now Jehoash was seven years old when he had begun to reign.
Yowash yana da shekara bakwai sa’ad da ya fara mulki.

< 2 Kings 11 >