< 2 Kings 10 >

1 Now Ahab had seventy sons in Samaria. And so Jehu wrote letters, and he sent to Samaria, to the nobles of the city, and to those greater by birth, and to those who had raised Ahab’s sons, saying:
To, akwai’ya’ya maza saba’in na gidan Ahab a Samariya. Saboda haka Yehu ya rubuta wasiƙu, ya aika su Samariya, zuwa ga shugabannin Yezireyel, da kuma ga masu lura da’ya’yan Ahab. Ya ce,
2 “Immediately when you receive these letters, you who have your lord’s sons, and chariots, and horses, and reinforced cities, and weapons,
“Da zarar wasiƙan nan ta sadu da ku, da yake’ya’yan maigidanku suna tare da ku, kuna kuma da kekunan yaƙi da dawakai, da birni mai katanga da makamai,
3 choose him who is better and who pleases you from among the sons of your lord, and set him on the throne of his father, and fight for the house of your lord.”
sai ku zaɓi mafi cancanta a cikin’ya’yan maigidanku ku sa shi a kan kursiyin mahaifinsa. Sa’an nan ku yi yaƙi don gidan maigidanku.”
4 But they were vehemently afraid, and they said: “Behold, two kings were not able to stand before him. So how will we be able to withstand him?”
Amma suka razana suka ce, “Idan sarakuna biyu ba su iya yin tsayayya da shi ba, wane mu?”
5 Therefore, those who were in charge of the house, and the prefects of the city, and those greater by birth, and those who raised the sons, sent to Jehu, saying: “We are your servants. Whatever you will order, we will do. But we will not appoint a king for ourselves. Do whatever pleases you.”
Saboda haka sarkin fada, da gwamnan birnin, da dattawa, da kuma masu lura da’ya’yan suka aika da saƙo ga Yehu, cewa, “Mu bayinka ne, za mu kuma yi duk abin da ka ce. Ba za mu naɗa kowa sarki ba; sai ka yi abin da ka ga ya fi kyau.”
6 Then he again wrote letters to them a second time, saying: “If you are mine, and if you obey me, take the heads of the sons of your lord, and come to me at Jezreel at this same hour tomorrow.” Now the sons of the king, being seventy men, were being raised with the nobles of the city.
Sai Yehu ya sāke rubuta musu wasiƙa ta biyu, ya ce, “In a gefena kuke, to, sai ku yi biyayya da ni, ku fille kawunan’ya’yan maigidanku, ku kawo mini a Yezireyel war haka gobe.” To,’ya’yan sarki, su saba’in, suna tare da manyan birni waɗanda suke lura da su.
7 And when the letters had arrived to them, they took the sons of the king, and they killed the seventy men. And they placed their heads in baskets, and they sent these to him at Jezreel.
Sa’ad da wasiƙar ta iso, sai mutanen nan suka ɗauki dukan’ya’yan sarkin nan saba’in, suka kashe su, suka sa kawunansu cikin kwanduna, suka aika wa Yehu a Yezireyel.
8 Then a messenger arrived and reported to him, saying, “They have brought the heads of the king’s sons.” And he responded, “Place them in two piles, beside the entrance of the gate, until morning.”
Da ɗan saƙon ya iso, sai aka ce wa Yehu, “Sun kawo kawunan’ya’yan sarki.” Sai Yehu ya ce, “Ku ajiye su kashi biyu a ƙofar gari har safiya.”
9 And when it had become light, he went out. And standing there, he said to all the people: “You are just. If I have conspired against my lord, and if I have killed him, who has struck down all of these?
Da gari ya waye, sai Yehu ya fita ya tsaya a gaban dukan jama’a ya ce, “Ba ku da laifi. Ni ne na ƙulla wa maigidana maƙarƙashiya, na kuma kashe shi, amma wa ya karkashe dukan waɗannan?
10 Now therefore, see that none of the words of the Lord has fallen to the ground, which the Lord spoke over the house of Ahab, and that the Lord has done what he spoke by the hand of his servant Elijah.”
Ku sani fa, ba kalmar da Ubangiji ya faɗa game da gidan Ahab da ba za tă cika ba. Ubangiji ya yi abin da ya alkawarta ta bakin bawansa Iliya.”
11 And so, Jehu struck down all who had remained from the house of Ahab in Jezreel, and all his nobles and friends and priests, until no remnant of them was left behind.
Saboda haka Yehu ya kashe duk waɗanda suka rage na iyalin Ahab a Yezireyel, tare da dukan fadawansa da aminansa da firistocinsa, ba a bar masa kowa ba.
12 And he rose up and went to Samaria. And when he had arrived at the shepherds’ cabin along the way,
Sa’an nan Yehu ya nufi Samariya. Da ya kai Bet-Eked na Makiyaya,
13 he found the brothers of Ahaziah, the king of Judah, and he said to them, “Who are you?” And they responded, “We are the brothers of Ahaziah, and we are going down to greet the sons of the king, and the sons of the queen.”
sai ya gamu da waɗansu daga dangin Ahaziya sarkin Yahuda, sai ya tambaye su, ya ce, “Ku, su wane ne?” Suka ce, “Mu dangin Ahaziya ne, mun kuma zo ne mu gai da iyalan sarki da kuma mahaifiyar sarauniya.”
14 And he said, “Take them alive.” And when they had taken them alive, they cut their throats at the cistern beside the cabin, forty-two men. And he did not leave any of them behind.
Sai ya umarta ya ce, “A kama su da rai!” Aka kuwa kama su aka yayyanka kusa da rijiyar Bet-Eked, su arba’in da biyu. Ba a bar wani da rai ba.
15 And when he had gone away from there, he found Jehonadab, the son of Rechab, coming to meet him, and he blessed him. And he said to him, “Is your heart upright, just as my heart is with your heart?” And Jehonadab said, “It is.” Then he said, “If it is, then give me your hand.” He gave his hand to him. And so he lifted him up to himself in the chariot.
Bayan ya bar wurin, sai ya gamu da Yehonadab ɗan Rekab wanda yake kan hanyarsa don yă sadu da shi. Sai Yehu ya gaishe shi, ya ce, “Ka amince da ni yadda na amince da kai?” Yehonadab ya ce, “I.” Yehu ya ce, “To, in haka ne ka ba ni hannunka.” Sai ya miƙa masa, Yehu kuwa ya ja shi cikin keken yaƙin.
16 And he said to him, “Come with me, and see my zeal for the Lord.” And he gave him a place in his chariot.
Yehu ya ce, “Zo tare da ni ka ga himmata saboda Ubangiji.” Sa’an nan ya sa suka tafi tare cikin keken yaƙinsa.
17 And he led him into Samaria. And he struck down all who were left behind of Ahab in Samaria, even to the last one, in accord with the word of the Lord, which he spoke through Elijah.
Da Yehu ya isa Samariya, sai ya karkashe dukan sauran iyalin Ahab, ya hallaka su, bisa ga maganar da Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya.
18 Then Jehu gathered together the entire people. And he said to them: “Ahab worshipped Baal a little, but I will worship him even more.
Sa’an nan Yehu ya tattara dukan jama’a ya ce musu, “Ahab ya bauta wa Ba’al kaɗan ne kawai; amma Yehu zai bauta masa sosai.
19 Now therefore, summon to me all the prophets of Baal, and all his servants, and all his priests. Let no one be permitted not to come, for great is the sacrifice from me to Baal. Whoever will fail to come, he shall not live.” Now Jehu was doing this treacherously, so that he might destroy the worshippers of Baal.
Yanzu sai ku kira dukan annabawan Ba’al, dukan masu yin masa hidima da kuma dukan firistocinsa. Ku tabbata ba a manta da wani ba, gama zan yi wa Ba’al babbar hadaya. Duk wanda bai zo ba, a bakin ransa.” Amma Yehu yana wayo ne domin yă hallaka masu yi wa Ba’al sujada.
20 And he said: “Sanctify a day of solemnity for Baal.” And he summoned
Yehu ya ce, “Ku kira jama’a don a girmama Ba’al.” Saboda haka suka yi shela.
21 and sent into all the borders of Israel. And all the servants of Baal came. There was left behind not even one who did not arrive. And they entered into the temple of Baal. And the house of Baal was filled, all the way from end to end.
Sa’an nan ya aika saƙo ko’ina a Isra’ila, dukan masu yi wa Ba’al hidima kuwa suka tattaru, ba mutumin da bai zo ba. Suka yi cincirindo a haikalin Ba’al har sai da ya cika makil.
22 And he said to those who were over the vestments, “Bring forth vestments for all the servants of Baal.” And they brought forth vestments for them.
Sai Yehu ya ce wa mai ajiyar tufafi, “Ka kawo riguna domin dukan masu yi wa Ba’al hidima.” Sai ya fito musu da riguna.
23 And Jehu, upon entering the temple of Baal with Jehonadab, the son of Rechab, said to the worshippers of Baal, “Inquire and see that there is no one with you from the servants of the Lord, but only from the servants of Baal.”
Sa’an nan Yehu da Yehonadab ɗan Rekab, suka shiga haikalin Ba’al. Yehu ya ce wa masu yi wa Ba’al sujada, “Ku dudduba ku tabbatar cewa babu wani bawan Ubangiji a nan tare da ku, sai masu hidimar Ba’al kawai.”
24 Then they entered, so that they might offer victims and holocausts. But Jehu had prepared for himself eighty men outside. And he had said to them, “If anyone escapes from among these men, whom I have led into your hands, your life will take the place of his life.”
Saboda haka suka shiga don su miƙa hadayu da kuma hadaya ta ƙonawa. To, Yehu ya riga ya ba wa mutane takwas wannan kashedi a waje cewa, “In waninku ya bar ɗaya daga cikin mutanen nan da nake danƙa a hannunku ya tsere, to, a bakin ransa.”
25 Then it happened that, when the holocaust had been completed, Jehu ordered his soldiers and officers, saying: “Enter and strike them down. Let no one escape.” And the soldiers and officers struck them down with the edge of the sword, and they cast them out. And they went into the city of the temple of Baal,
Nan da nan sa’ad da Yehu ya gama yin hadayar, sai ya umarci masu gadin da hafsoshi, “Ku shiga ku karkashe su; kada ku bar wani yă tsere.” Saboda haka suka karkashe su da takobi. Masu gadin da hafsoshin suka wuwwurga gawawwakinsu waje, suka kuma shiga ciki cikin haikalin Ba’al ɗin,
26 and they took away the statue from the shrine of Baal, and they burned it up
suka fitar da dutsen tsafi daga haikalin Ba’al, suka kuma ƙone shi.
27 and crushed it. They also tore down the temple of Baal, and they made it into a latrine, even to this day.
Suka farfasa dutsen tsafin Ba’al, suka kuma rushe haikalin, mutane suka mai da wurin salga har yă zuwa yau.
28 And thus did Jehu wipe away Baal from Israel.
Ta haka Yehu ya hallaka butar Ba’al a Isra’ila.
29 Yet truly, he did not turn away from the sins of Jeroboam, the son of Nebat, who caused Israel to sin. Neither did he forsake the golden calves, which were in Bethel and Dan.
Duk da haka, bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba, wato, yin sujada ga siffofin maruƙa na zinariya a Betel da kuma Dan.
30 Then the Lord said to Jehu: “Since you have diligently carried out what was right and pleasing in my eyes, and since you have accomplished, against the house of Ahab, all that was in my heart, your sons shall sit upon the throne of Israel, even to the fourth generation.”
Ubangiji ya ce wa Yehu, “Tun da yake ka aikata abin da yake mai kyau a idanuna, ka kuma yi wa gidan Ahab dukan abin da yake a zuciyata, ina yin maka alkawari cewa zuriyarka za su yi mulkin Isra’ila har tsara ta huɗu.”
31 But Jehu did not take care, so that he might walk in the law of the Lord, the God of Israel, with all his heart. For he did not withdraw from the sins of Jeroboam, who had caused Israel to sin.
Duk da haka, Yehu bai mai da hankali ya kiyaye dokokin Ubangiji, Allah na Isra’ila da dukan zuciyarsa ba. Bai rabu da zunubin Yerobowam, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba.
32 In those days, the Lord began to be weary of Israel. And Hazael struck them throughout all the parts of Israel,
A kwanakin sai Ubangiji ya fara rage girman Isra’ila, Hazayel ya yi nasara a bisa Isra’ila a ko’ina a yankinsu
33 from the Jordan opposite the eastern region, in all the land of Gilead, and Gad, and Reuben, and Manasseh, from Aroer, which is above the torrent Arnon, in both Gilead and Bashan.
gabas da Urdun, cikin dukan ƙasar Gileyad (yankin Gad, da na Ruben, da na Manasse), daga Arower wajen Kwarin Arnon ya ratsa Gileyad zuwa Bashan.
34 But the rest of the words of Jehu, and all that he did, and his strength, have these not been written in the book of the words of the days of the kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Yehu, da dukan abin da ya yi, a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
35 And Jehu slept with his fathers, and they buried him in Samaria. And Jehoahaz, his son, reigned in his place.
Yehu ya huta tare da kakanninsa, aka binne shi a Samariya. Yehoyahaz kuma ya ci sarauta bayansa.
36 Now the days during which Jehu reigned over Israel, in Samaria, were twenty-eight years.
Yehu ya yi sarautar Isra’ila a Samariya shekara ashirin da takwas.

< 2 Kings 10 >