< 2 Kings 13 >

1 In the twenty-third year of Jehoash, the son of Ahaziah, the king of Judah, Jehoahaz, the son of Jehu, reigned over Israel, in Samaria, for seventeen years.
A shekara ta ashirin da uku ta Yowash ɗan Ahaziya, sarkin Yahuda, Yehoyahaz ɗan Yehu, ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuwa yi mulki shekaru goma sha bakwai.
2 And he did evil before the Lord. And he followed the sins of Jeroboam, the son of Nebat, who caused Israel to sin. And he did not turn aside from these.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji ta wurin bin zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai kuwa guje musu ba.
3 And the fury of the Lord was enraged against Israel, and he delivered them into the hand of Hazael, the king of Syria, and into the hand of Benhadad, the son of Hazael, during all the days.
Saboda haka fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Isra’ila, kuma da daɗewa ya sa su a ƙarƙashin ikon Hazayel sarkin Aram da Ben-Hadad ɗansa.
4 But Jehoahaz petitioned the face of the Lord, and the Lord heeded him. For he saw the anguish of Israel, because the king of Syria had oppressed them.
Sai Yehoyahaz ya nemi tagomashin Ubangiji, Ubangiji kuwa ya saurare shi, domin ya gan irin matsin da sarkin Aram yake yi wa Isra’ila.
5 And the Lord gave a savior to Israel. And they were freed from the hand of the king of Syria. And the sons of Israel lived in their tabernacles, just as yesterday and the day before.
Sai Ubangiji ya tā da mai ceto wa Isra’ila, suka kuma kuɓuta daga ikon Aram. Ta haka Isra’ilawa suka yi zama a gidajensu yadda suka yi a dā.
6 Yet truly, they did not withdraw from the sins of the house of Jeroboam, who had caused Israel to sin. Instead, they walked by them. And there was even a sacred grove still remaining in Samaria.
Sai dai ba su bar yin zunuban gidan Yerobowam ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata; suka ci gaba da yinsu. Haka ma, ginshiƙin Ashera ta kasance a tsaye a cikin Samariya.
7 And there was left to Jehoahaz from the people nothing but fifty horsemen, and ten chariots, and ten thousand foot soldiers. For the king of Syria had killed them, and he had reduced them to become like dust on a threshing floor.
Ba abin da ya rage na rundunar Yehoyahaz sai mahayan dawakai hamsin, kekunan yaƙi goma da kuma sojoji ƙasa dubu goma. Gama sarkin Aram ya hallaka sauran, ya kuma yi kaca-kaca da su kamar ƙura a masussuka.
8 But the rest of the words of Jehoahaz, and all that he did, and his strength, have these not been written in the book of the words of the days of the kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Yehoyahaz, dukan abubuwan da ya yi da kuma nasarorinsa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
9 And Jehoahaz slept with his fathers, and they buried him in Samaria. And Joash, his son, reigned in his place.
Yehoyahaz ya huta da kakanninsa, aka binne shi a Samariya, Yehowash ɗansa kuma ya gāje shi.
10 In the thirty-seventh year of Jehoash, the king of Judah, Joash, the son of Jehoahaz, reigned over Israel, in Samaria, for sixteen years.
A shekaru talatin da bakwai ta Yowash sarkin Yahuda, Yehowash ɗan Yehoyahaz ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekaru goma sha shida.
11 And he did what is evil in the sight of the Lord. He did not turn aside from all the sins of Jeroboam, the son of Nebat, who caused Israel to sin. Instead, he walked by them.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai juya ga barin zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, ya ci gaba da yinsu.
12 But the rest of the words of Joash, and all that he did, and his strength, the manner in which he fought against Amaziah, the king of Judah, have these not been written in the book of the words of the days of the kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Yowash, da dukan abubuwan da ya yi, da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙin da ya yi da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
13 And Joash slept with his fathers. Then Jeroboam sat upon his throne. And Joash was buried in Samaria, with the kings of Israel.
Yowash ya huta da kakanninsa, Yerobowam kuwa ya gāje shi. Aka binne Yehowash a Samariya tare da sarakunan Isra’ila.
14 Now Elisha was sick of the infirmity from which he also died. And Joash, the king of Israel, descended to him. And he was weeping before him, and saying: “My father, my father! The chariot of Israel and its driver!”
To, Elisha ya kamu da ciwon da ya kashe shi. Yowash sarkin Isra’ila ya gangara don yă gan shi, ya kuma yi kuka dominsa. Ya yi kuka yana cewa, “Babana! Babana, keken yaƙin Isra’ila da mahayan dawakanta!”
15 And Elisha said to him, “Bring a bow and arrows.” And when he had brought a bow and arrows to him,
Elisha ya ce wa Yehowash, “Ka samo baka da kibiyoyi,” ya kuwa yi haka.
16 he said to the king of Israel, “Place your hand upon the bow.” And when he had placed his hand, Elisha placed his own hands over the hands of the king.
Sai ya ce wa Yehowash sarkin Isra’ila, “Ka ɗauki baka a hannunka.” Da ya ɗauka, sai Elisha ya sa hannunsa a hannuwan sarki.
17 And he said, “Open the window toward the east.” And when he had opened it, Elisha said, “Shoot an arrow.” And he shot it. And Elisha said: “It is the arrow of the salvation of the Lord, and the arrow of salvation against Syria. And you shall strike the Syrians at Aphek, until you consume them.”
Ya ce masa, “Ka buɗe taga wajen gabas,” sai ya buɗe. Sai Elisha ya ce, “Ka harba!” Sai ya harba. Elisha ya ce, “Kibiyar nasara ta Ubangiji, kibiyar nasara a kan Aram! Za ka hallaka Arameyawa sarai a Afek.”
18 And he said, “Take the arrows.” And when he had taken them, he then said to him, “Strike an arrow against the ground.” And when he had struck three times, and he had stood still,
Sa’an nan ya ce, “Ka ɗauki kibiyoyi,” sai sarkin ya ɗauko. Sai Elisha ya ce, “Ka caki ƙasa.” Sai ya caka sau uku sa’an nan ya daina.
19 the man of God became angry against him. And he said: “If you had struck five or six or seven times, you would have struck down Syria, even until it was consumed. But now you will strike it three times.”
Sai mutumin Allah ya yi fushi da shi ya ce, “Da a ce ka caki ƙasar sau biyar ko shida; da za ka yi nasara a kan Aram ka kuma hallaka ta sarai. Amma yanzu za ka yi nasara a kanta sau uku ne kawai.”
20 Then Elisha died, and they buried him. And the robbers from Moab came into the land in the same year.
Elisha ya mutu, aka kuma binne shi. To, mahara Mowabawa sun saba kawo hari a ƙasar Isra’ila a kowace bazara.
21 But certain ones who were burying a man saw the robbers, and they cast the dead body into the sepulcher of Elisha. But when it had touched the bones of Elisha, the man revived, and he stood upon his feet.
Wata rana yayinda waɗansu Isra’ilawa suke binne wani mutum, farat ɗaya sai ga mahara; saboda haka suka jefar da gawar mutumin a kabarin Elisha. Da gawar ta taɓa ƙasusuwan Elisha, sai mutumin ya farka, ya tashi ya tsaya da ƙafafunsa.
22 Now Hazael, the king of Syria, afflicted Israel during all the days of Jehoahaz.
Hazayel sarkin Aram ya musguna wa Isra’ila a duk tsawon mulkin Yehoyahaz.
23 But the Lord took pity on them, and he returned to them, because of his covenant, which he had made with Abraham, and Isaac, and Jacob. And he was not willing to destroy them, nor to cast them out completely, even to the present time.
Amma Ubangiji ya nuna musu alheri, ya ji tausayinsu, ya kuma damu da su saboda alkawarinsa da Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Har yă zuwa yau bai yarda yă hallaka su ko yă shafe su daga gabansa ba.
24 Then Hazael, the king of Syria, died. And Benhadad, his son, reigned in his place.
Hazayel sarkin Aram ya mutu, sai Ben-Hadad ɗansa ya gāje shi.
25 Now Joash, the son of Jehoahaz, by a just war, took the cities from the hand of Benhadad, the son of Hazael, which he had taken from the hand of Jehoahaz, his father. Joash struck him three times, and he restored the cities to Israel.
Sa’an nan Yowash ya sāke ƙwato garuruwan da Ben-Hadad ya ci da yaƙi a hannun mahaifinsa Yehoyahaz. Sau uku Yehowash ya yi nasara a kansa, ta haka kuwa ya ƙwace garuruwan Isra’ilawa.

< 2 Kings 13 >