< 2 Chronicles 35 >

1 Now Josiah kept the Passover to the Lord in Jerusalem, and it was immolated on the fourteenth day of the first month.
Yosiya ya yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji a Urushalima, aka kuma yanka ɗan ragon Bikin Ƙetarewa a ranar goma sha huɗu ga wata na farko.
2 And he appointed the priests in their offices, and he exhorted them to minister in the house of the Lord.
Ya zaɓi firistoci su yi aikinsu, sai ya ƙarfafa su su yi aikin da kyau a hidimar haikalin Ubangiji.
3 Also, he spoke with the Levites, by whose instruction all of Israel was sanctified to the Lord, saying: “Place the ark in the sanctuary of the temple, which Solomon, the son of David, the king of Israel, built. For never again shall you carry it. Instead, now you shall minister to the Lord your God, and to his people Israel.
Ya ce wa Lawiyawa waɗanda suke koyar da dukan Isra’ila da kuma waɗanda aka tsarkake wa Ubangiji. “Ku sa akwatin alkawari mai tsarki a cikin haikalin da Solomon ɗan Dawuda sarkin Isra’ila ya gina. Ba za a riƙa ɗaukansa a kafaɗa ba. Yanzu ku bauta wa Ubangiji Allahnku da kuma mutanensa Isra’ila.
4 And prepare yourselves by your houses and families, within each division, just as David, the king of Israel, instructed, and just as his son Solomon has written.
Ku shirya kanku iyali-iyali a sassanku, bisa ga umarnan da Dawuda sarkin Isra’ila da kuma ɗansa Solomon suka rubuta.
5 And minister in the sanctuary, by the Levitical families and companies.
“Ku tsaya a tsattsarkan wuri, bisa ga ƙungiyoyin gidajen kakannin’yan’uwanku, waɗanda su ba firistoci ba ne. Kowanne ya sami kashi daga cikin gidan Lawiyawa.
6 And having been sanctified, immolate the Passover. And then prepare your brothers, so that they may be able to act in accord with the words which the Lord has spoken by the hand of Moses.”
Ku yanka ragunan Bikin Ƙetarewa, ku tsarkake kanku, ku kuma shirya raguna domin’yan’uwanku, kuna yin abin da Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.”
7 After this, Josiah gave to all the people, those who had been found there at the solemnity of the Passover, thirty thousand lambs and young goats from the flocks, and other kinds of small cattle, and also three thousand oxen. All these were from the substance of the king.
Yosiya ya tanada wa dukan mutanen da ba firistoci ba ne waɗanda suke a wurin, tumaki da awaki dubu talatin don a yanka saboda hadayun Bikin Ƙetarewa, ya kuma ba su shanu dubu uku. Dukan dabbobin kuwa daga garken sarki ne.
8 Also, his rulers offered what they had vowed freely, as much for the people as for the priests and Levites. Moreover, Hilkiah, and Zechariah, and Jehiel, rulers of the house of the Lord, gave to the priests, in order to observe the Passover, two thousand six hundred small cattle, and three hundred oxen.
Fadawansa su ma suka ba da taimako da yardar rai ga mutane da kuma firistoci da Lawiyawa. Hilkiya, Zakariya da Yehiyel masu aiki a haikalin Allah, suka ba firistoci hadayun Bikin Ƙetarewa dubu biyu da ɗari shida da kuma shanu ɗari uku.
9 And Conaniah, with Shemaiah and Nethanel, his brothers, indeed also Hashabiah and Jeiel and Jozabad, rulers of the Levites, gave to the rest of the Levites, in order to celebrate the Passover, five thousand small cattle, and five hundred oxen.
Haka kuma Konaniya tare da Shemahiya da Netanel, ɗan’uwansa, da Hashabiya, Yehiyel da Yozabad, shugabannin Lawiyawa, suka tanadar da hadayun Bikin Ƙetarewa dubu biyar da kuma bijimai ɗari biyar domin Lawiyawa.
10 And the ministry was prepared. And the priests stood in their office, and the Levites also stood in their companies, according to the order of the king.
Sa’ad da aka shirya kome don Bikin Ƙetarewar, sai Firistoci tare da Lawiyawa suka tsaya wurin tsayawarsu bisa ga umarnin sarki.
11 And the Passover was immolated. And the priests sprinkled the blood with their hand, and the Levites drew away the pelts of the holocausts.
Aka yanka ragunan Bikin Ƙetarewa, firistoci kuma suka yayyafa jinin da aka ba su, yayinda Lawiyawa suna fiɗan dabbobi.
12 And they put these aside, so that they might give them to each one, by their houses and families, and so that they might be offered to the Lord, just as it was written in the book of Moses. And with the oxen, they acted similarly.
Suka keɓe hadayun ƙonawa don su ba da su ga ƙungiyoyin iyalan mutane don su miƙa ga Ubangiji, yadda yake a rubuce a Littafin Musa. Suka yi haka da shanun.
13 And they roasted the Passover above fire, in accord with what was written in the law. Yet truly, the victims of peace offerings they boiled in cauldrons and kettles and pots. And they promptly distributed these to all the common people.
Suka gasa dabbobin Bikin Ƙetarewa a bisa wuta yadda aka tsara, suka dafa hadayu masu tsarki a tukwane, da manyan tukwane, da kuma kwanoni, suka raba su nan da nan ga dukan mutane.
14 Then afterward, they made preparations for themselves and for the priests. Indeed, the priests had been occupied in the oblations of the holocausts and the fat offerings, even until night. Therefore, the Levites made preparations for themselves and for the priests, the sons of Aaron, last.
Bayan wannan, suka shirya wa kansu da kuma wa firistoci, saboda firistoci, zuriyar Haruna, suna miƙa hadayun ƙonawa da sashen kitse daga safe har dare. Saboda haka Lawiyawa suka shirya wa kansu da kuma wa firistocin daga zuriyar Haruna.
15 Now the singers, the sons of Asaph, were standing in their order, according to the instruction of David, and of Asaph and Heman and Jeduthun, the prophets of the king. Truly, the porters kept watch at each gate, so as not to depart from their ministry even for one moment. And for this reason, their brothers, the Levites, prepared foods for them.
Mawaƙa zuriyar Asaf, suna a wuraren da Dawuda, Asaf, Heman da Yedutun mai duba na sarki suka tsara. Bai zama lalle matsaran ƙofofi a kowace ƙofa su bar wuraren aikinsu ba, domin’yan’uwansu Lawiyawa sun yi shiri dominsu.
16 And so, the entire worship ritual of the Lord was completed on that day, so that they observed the Passover and offered holocausts upon the altar of the Lord, in accord with the precept of king Josiah.
Ta haka fa aka yi dukan hidimar Ubangiji a wannan rana, domin su kiyaye Bikin Ƙetarewa, domin kuma su miƙa hadayu na ƙonawa a bisa bagaden Ubangiji, yadda sarki Yosiya ya umarta.
17 And the sons of Israel, who had been found there, kept the Passover at that time, with the solemnity of unleavened bread, for seven days.
Isra’ilawan da suka kasance a can suka yi Bikin Ƙetarewa a wannan rana, suka kuma kiyaye Bikin Burodi Marar Yisti kwana bakwai.
18 There was no Passover similar to this one in Israel, from the days of Samuel the prophet. And neither did anyone, out of all the kings of Israel, keep such a Passover as did Josiah, the priests and Levites, and all those of Judah and Israel who had been found, and the inhabitants of Jerusalem.
Ba a taɓa yin Bikin Ƙetarewa haka ba tun zamanin annabi Sama’ila; kuma babu sarkin Isra’ilan da ya taɓa yin irin Bikin Ƙetarewa kamar yadda Yosiya ya yi, tare da firistoci, Lawiyawa da kuma dukan Yahuda da Isra’ila, waɗanda suke can tare da mutanen Urushalima.
19 In the eighteenth year of the reign of Josiah, this Passover was celebrated.
An yi wannan Bikin Ƙetarewa a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yosiya.
20 After Josiah had repaired the temple, Neco, the king of Egypt, ascended to fight at Carchemish, beside the Euphrates. And Josiah went out to meet him.
Bayan wannan duka, sa’ad da Yosiya ya shirya haikali, Neko sarkin Masar ya haura don yă yi yaƙi a Karkemish a Yuferites, sai Yosiya ya fita don yă fafata da shi a yaƙi.
21 But he sent messengers to him, saying: “What is there between me and you, O king of Judah? I have not come against you today. Instead, I am fighting against another house, to which God instructed me to go promptly. Refrain from acting against God, who is with me, otherwise he may kill you.”
Amma Neko ya aiki’yan saƙo ga Yosiya, yana cewa, “Me ya gama ni da kai, ya Sarkin Yahuda? Ban zo in yi yaƙi da kai ba. Na zo ne in yi yaƙi da gidan da yake gāba da ni! Ka ƙyale ni! Allah ne ya riga ya faɗa mini in hanzarta. Kada ka yi gāba da Allah, wanda yake tare da ni, don kada yă hallaka ka.”
22 Josiah was not willing to return. Instead, he prepared for war against him. Neither would he agree to the words of Neco from the mouth of God. In truth, he traveled so that he might do battle in the field of Megiddo.
Yosiya fa, bai juya daga gare shi ba, amma ya ɓad da kama don yă yi yaƙin. Bai saurari abin da Neko ya faɗa bisa ga umarnin Allah ba, amma ya tafi ya yaƙe shi a filin Megiddo.
23 And there, having been wounded by archers, he said to his servants: “Lead me away from the battle. For I have been severely wounded.”
Maharba suka harbi Yosiya, sai ya ce wa hafsoshinsa, “Ku ɗauke ni ku fita da ni daga nan; gama an yi mini mummunan rauni.”
24 And they took him from the chariot, into another chariot which was following him, as was the custom of kings. And they transported him to Jerusalem. And he died, and he was buried in the mausoleum of his fathers. And all of Judah and Jerusalem mourned for him,
Saboda haka suka ɗauke shi a keken yaƙin, suka fitar da shi, suka sa shi a wata keken yaƙin da yake da shi, suka kawo shi Urushalima, inda ya mutu. Aka binne shi a makabartar kakanninsa, sai dukan Yahuda da Urushalima suka yi makoki dominsa.
25 most of all Jeremiah. All the singing men and women repeat his lamentations over Josiah, even to the present day. And this has become like a law in Israel. Behold, it is found written in the Lamentations.
Annabin Irmiya ya tsara waƙoƙin makoki domin Yosiya, wanda har wa yau mawaƙa maza da mata suke rera game da Yosiya. Suka sa waɗannan su zama al’ada a Isra’ila, suna kuma a rubuce cikin Littafin Makoki.
26 Now the rest of the words of Josiah, and his mercies, which were instructed by the law of the Lord,
Sauran ayyukan mulkin Yosiya da kuma kyawawan abubuwan da ya yi, bisa ga abin da aka rubuta a Dokar Ubangiji,
27 and also his works, the first and the last, have been written in the book of the kings of Judah and Israel.
dukan ayyukan, daga farko har zuwa ƙarshe, suna a rubuce cikin littafin sarakunan Isra’ila da na Yahuda.

< 2 Chronicles 35 >