< 2 Chronicles 36 >

1 Then the people of the land took Jehoahaz, the son of Josiah, and they appointed him king in place of his father, in Jerusalem.
Sai mutanen ƙasar suka ɗauki Yehoyahaz ɗan Yosiya suka naɗa shi sarki a Urushalima yă gāji mahaifinsa.
2 Jehoahaz was twenty-three years old when he had begun to reign, and he reigned for three months in Jerusalem.
Yehoyahaz yana da shekara ashirin da uku sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima wata uku.
3 Then the king of Egypt, when he had arrived in Jerusalem, removed him, and condemned the land to one hundred talents of silver and one talent of gold.
Sarkin Masar ya tumɓuke shi a Urushalima, ya tilasta Yahuda su biya haraji talenti ɗari na azurfa da kuma talentin zinariya.
4 And he appointed Eliakim, his brother, as king in his place, over Judah and Jerusalem. And he changed his name to Jehoiakim. Truly, he took Jehoahaz with him, and he led him away to Egypt.
Sarkin Masar ya naɗa Eliyakim, ɗan’uwan Yehoyahaz, sarki a bisa Yahuda da kuma Urushalima, ya kuma canja sunan Eliyakim zuwa Yehohiyakim. Amma Neko ya ɗauki Yehoyahaz ɗan’uwan Eliyakim ya kai Masar.
5 Jehoiakim was twenty-five years old when he had begun to reign, and he reigned for eleven years in Jerusalem. And he did evil before the Lord his God.
Yehohiyakim yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya. Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnsa.
6 Nebuchadnezzar, the king of the Chaldeans, ascended against him, and led him bound in chains to Babylon.
Nebukadnezzar sarkin Babilon ya hauro ya kara da shi. Ya kama shi, ya daure da sarƙoƙin tagulla, ya kuma kai shi Babilon.
7 And to there, he also took away the vessels of the Lord, and he placed them in his temple.
Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kuma kwaso kayayyaki daga haikalin Ubangiji ya sa su a haikalinsa a can.
8 But the rest of the words of Jehoiakim, and his abominations that he worked, and the things that were found in him, are contained in the book of the kings of Judah and Israel. Then his son, Jehoiachin, reigned in his place.
Sauran ayyukan mulkin Yehohiyakim, ayyukan banƙyamar da ya aikata da dukan abubuwan da aka same shi da su, suna a rubuce cikin littafin sarakunan Isra’ila da na Yahuda. Sai Yehohiyacin ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
9 Jehoiachin was eight years old when he had begun to reign, and he reigned for three months and ten days in Jerusalem. And he did evil in the sight of the Lord.
Yehohiyacin yana da shekara goma sha takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima wata uku da kwana goma. Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji.
10 And when the course of a year had turned, king Nebuchadnezzar sent and brought him to Babylon, carrying away, at the same time, the most precious vessels of the house of the Lord. Truly, he appointed his uncle, Zedekiah, as king over Judah and Jerusalem.
Da bazara, Sarki Nebukadnezzar ya aika a kawo Yehohiyacin, aka kuma kawo shi Babilon, tare da kayayyaki masu daraja daga haikalin Ubangiji, sai Sarki Nebukadnezzar ya naɗa kawunsa Zedekiya, sarki a bisa Yahuda da Urushalima.
11 Zedekiah was twenty-one years old when he had begun to reign. And he reigned for eleven years in Jerusalem.
Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya.
12 And he did evil in the eyes of the Lord his God. And he did not show remorse before the face of the prophet Jeremiah, who was speaking to him from the mouth of the Lord.
Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnsa kuma bai ƙasƙantar da kansa a gaban Irmiya annabi, wanda ya yi magana kalmar Ubangiji ba.
13 Also, he withdrew from king Nebuchadnezzar, who had bound him by an oath to God, and he hardened his own neck and his own heart, so that he did not return to the Lord, the God of Israel.
Ya tayar wa Sarki Nebukadnezzar, wanda ya sa ya yi rantsuwa da sunan Allah. Ya zama mai kunnen ƙashi da kuma taurin zuciya, bai kuwa juye ga Ubangiji, Allah na Isra’ila ba.
14 Then too, all the leaders of the priests, with the people, transgressed iniquitously, in accord with all the abominations of the Gentiles. And they polluted the house of the Lord, which he had sanctified to himself in Jerusalem.
Bugu da ƙari, dukan shugabannin firistoci da mutane suka ƙara zama marasa aminci, suna bin dukan abubuwan banƙyama na al’ummai, suka ƙazantar da haikalin Ubangiji, wanda ya tsarkake a Urushalima.
15 Then the Lord, the God of their fathers, sent to them, by the hand of his messengers, rising in the night and daily admonishing them. For he was lenient to his people and to his habitation.
Sai Ubangiji Allah na kakanninsu, ya yi ta aika da magana gare su ta wurin’yan saƙonsa sau da sau, domin ya ji tausayi mutanensa da mazauninsa.
16 But they ridiculed the messengers of God, and they gave little weight to his words, and they mocked the prophets, until the fury of the Lord ascended against his people, and there was no remedy.
Amma suka yi wa’yan saƙon Allah ba’a, suka rena maganarsa, suka yi wa annabawansa dariyar reni, har sai da fushin Ubangiji ya tasar a kan mutanensa babu makawa.
17 For he led over them the king of the Chaldeans. And he put to death their young men by the sword, in the house of his sanctuary. There was no pity for adolescents, nor virgins, nor the elderly, nor even for the disabled. Instead, he delivered them all into his hands.
Ya bashe su ga sarkin Babiloniyawa wanda ya karkashe samarinsu da takobi a wuri mai tsarki, bai yi juyayin saurayi, ko budurwa, ko tsoho, ko gajiyayye ba. Allah ya bashe su duka ga Nebukadnezzar.
18 And all the vessels of the house of Lord, as much the greater as the lesser, and the treasures of the temple, and of the king and the rulers, he carried away to Babylon.
Nebukadnezzar ya kwashe dukan kayayyaki daga haikalin Allah, babba da ƙarami, da ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin sarki da na fadawansa zuwa Babilon.
19 The enemies set fire to the house of God, and they destroyed the wall of Jerusalem. They burned down all the towers. And whatever was precious, they demolished.
Suka cinna wa haikalin Allah wuta, suka rurrushe katangar Urushalima; suka ƙone dukan fada, suka kuma lalace kome mai amfani da yake can.
20 If anyone had escaped from the sword, he was led into Babylon. And he served the king and his sons, until the king of Persia would command,
Waɗanda ba a kashe ba kuwa Nebukadnezzar ya kwashe su, ya kai Babilon, suka zama bayinsa da na’ya’yansa maza har zuwa kahuwar mulkin Farisa.
21 and the word of the Lord by the mouth of Jeremiah would be fulfilled, and the land would celebrate her Sabbaths. For during all the days of the desolation, she kept a Sabbath, until the seventy years were completed.
Ƙasar ta more hutun Asabbacinta; a dukan lokacin zamanta kango ta huta, har sai da shekaru saba’in nan suka cika bisa ga maganar Ubangiji da Irmiya ya faɗi.
22 Then, in the first year of Cyrus, the king of the Persians, in order to fulfill the word of the Lord, which he had spoken by the mouth of Jeremiah, the Lord stirred up the heart of Cyrus, the king of the Persians, who commanded this to be proclaimed throughout his entire kingdom, and also in writing, saying:
Don a cika maganar da Ubangiji ya yi ta wurin Irmiya, a shekara farko ta Sairus sarkin Farisa, sai Ubangiji ya motsa zuciyar Sairus na Farisa don yă yi shela a dukan masarautarsa, ya kuma sa shi a rubuce cewa,
23 “Thus says Cyrus, the king of the Persians: The Lord, the God of heaven, has given to me all the kingdoms of the earth. And he has instructed me that I should build for him a house in Jerusalem, which is in Judea. Who among you is from his entire people? May the Lord his God be with him, and let him ascend.”
“Ga abin da Sairus sarkin Farisa ya ce, “‘Ubangiji Allah na sama, ya ba ni dukan mulkokin duniya, ya kuma naɗa ni in gina masa haikali a Urushalima a Yahuda. Duk wani na mutanensa a cikinku, bari yă haura yă tafi, bari kuma Ubangiji Allahnsa yă kasance tare da shi.’”

< 2 Chronicles 36 >