< 1 Samuel 9 >

1 Now there was a man of Benjamin, whose name was Kish, the son of Abiel, the son of Zeror, the son of Becorath, the son of Aphiah, the son of a man of Benjamin, strong and robust.
An yi wani mutum, attajiri daga kabilar Benyamin, sunansa Kish, ɗan Abiyel, jikan Zeror na iyalin Bekorat daga dangin Afiya.
2 And he had a son called Saul, an elect and good man. And there was not a man among the sons of Israel better than he was. For he stood head and shoulders above all the people.
Yana da ɗa mai suna Shawulu, wani kyakkyawan saurayi. A cikin mutanen Isra’ila ba wanda ya fi shi kyau, ya kuma fi kowa tsaye.
3 Now the donkeys of Kish, the father of Saul, had become lost. And Kish said to his son Saul, “Take with you one of the servants, and rising up, go out and seek the donkeys.” And when they had passed through mount Ephraim,
To, ana nan sai jakunan Kish mahaifin Shawulu suka ɓace. Kish ya ce wa ɗansa, “Tashi ka tafi tare da wani daga cikin bayi, ku nemo jakunan.”
4 and through the land of Shalishah, and had not found them, they crossed also through the land of Shaalim, and they were not there, and through the land of Benjamin, and they found nothing.
Suka bi ta ƙasar tudu ta Efraim, suka ratsa ta ƙasar Shalisha amma ba su same su ba. Suka bi ta ƙasar Shalim, a can ma ba su same su ba sai suka bi ta ƙasar Benyamin, a can ma ba su same su ba.
5 And when they had arrived in the land of Zuph, Saul said to the servant who was with him, “Come, and let us return, otherwise perhaps my father may forget the donkeys, and become anxious over us.”
Da suka iso gunduman Zuf, sai Shawulu ya ce wa bawan da yake tare da shi, “Zo mu koma kada mahaifina yă bar damuwa a kan jakuna, yă shiga damuwa game da mu.”
6 And he said to him: “Behold, there is a man of God in this city, a noble man. All that he says, happens without fail. Now therefore, let us go there. For perhaps he may tell us about our way, because of which we have arrived.”
Amma bawan ya amsa ya ce, “Duba, a wannan gari akwai wani mutumin Allah, ana ganin girmansa ƙwarai kuma duk abin da ya faɗa yakan zama gaskiya. Mu tafi can wurinsa wataƙila zai gaya mana hanyar da za mu bi.”
7 And Saul said to his servant: “Behold, let us go. But what will we bring to the man of God? The bread in our sacks has run out. And we have no small gift that we might give to the man of God, nor anything at all.”
Shawulu ya ce wa bawan, “Idan muka isa can, me za mu ba wa mutumin? Ga shi abinci guzurinmu duk ya ƙare, ba mu da wani abin da za mu kai wa mutumin Allahn nan. Me muke da shi?”
8 The servant again responded to Saul, and he said: “Behold, there is found in my hand a coin of the fourth part of a stater. Let us give it to the man of God, so that he may reveal to us our way.”
Bawan ya sāke ce masa, “Duba ina da kwatar azurfar da zan ba wa mutumin Allah don yă gaya mana wace hanya ce za mu bi.”
9 (In past times, in Israel, anyone going to consult God would speak in this way, “Come, and let us go to the seer.” For one who is called a prophet today, in past times was called a seer.)
(A dā a Isra’ila, in wani yana so yă nemi nufin Allah, mutumin yakan ce, “Zo mu tafi wajen mai duba.” Gama wanda ake ce da shi annabi a yanzu, a dā ana kiransa mai duba ne.)
10 And Saul said to his servant: “Your word is very good. Come, let us go.” And they went into the city, where the man of God was.
Shawulu ya ce wa bawansa, “Madalla, zo mu tafi.” Sai suka kama hanya suka nufi birnin da mutumin Allah yake.
11 And as they were ascending the slope to the city, they found some young women going out to draw water. And they said to them, “Is the seer here?”
Sa’ad da suke haura tudun zuwa birnin, sai suka sadu da waɗansu’yan mata sun fito za su ɗiban ruwa. Sai suka tambaye su, suka ce, “Mai duba yana nan?”
12 And responding, they said to them: “He is. Behold, he is ahead of you. Hurry now. For he came into the city today, since there is a sacrifice for the people today, on the high place.
’Yan matan suka ce, “I, yana nan, ai, ga shi ma a gabanku, ku hanzarta. Shigowarsa ke nan a garin, domin yau mutane za su ba da sadaka a bagade a kan tudu.
13 Upon entering the city, you should find him immediately, before he ascends to the high place for the meal. And the people will not eat until he has arrived. For he blesses the victim, and thereafter those who were called will eat. Now therefore, go up. For you will find him today.”
Da zarar kun shiga garin, za ku same shi kafin yă tafi cin abinci a wurin yin sadakar, can kan tudu. Gama jama’a ba za su ci ba, sai ya kai can ya sa albarka a sadakar, sa’an nan waɗanda aka gayyata su ci. Ku haura da sauri, za ku same.”
14 And they ascended into the city. And as they were walking in the midst of the city, Samuel appeared, advancing to meet them, so that he might ascend to the high place.
Suka haura zuwa birnin, da shigarsu sai ga Sama’ila ya nufo su a hanyarsa ta zuwa kan tudu.
15 Now the Lord had revealed to the ear of Samuel, one day before Saul had arrived, saying:
Kafin zuwa Shawulu, Ubangiji ya riga ya bayyana wa Sama’ila ya ce,
16 “Tomorrow, at the same hour that it is now, I will send to you a man from the land of Benjamin. And you shall anoint him to be the leader over my people Israel. And he will save my people from the hand of the Philistines. For I have looked with favor upon my people, because their outcry has reached me.”
“Gobe war haka zan aiko maka da wani mutum daga ƙasar Benyamin. Ka keɓe shi shugaban mutanena Isra’ila. Shi zai cece mutanena daga hannun Filistiyawa. Na ga azabar mutanena gama kukansu ya hauro wurina.”
17 And when Samuel had caught sight of Saul, the Lord said to him: “Behold, the man about whom I spoke to you. This one shall rule over my people.”
Da Sama’ila ya hangi Shawulu, Ubangiji ya ce masa, “Ga mutumin da na yi maka magana, shi ne zai bi da mutanena.”
18 Then Saul drew near to Samuel, at the middle of the gate, and he said, “Tell me, I beg you: where is the house of the seer?”
Shawulu ya sami Sama’ila a hanyar shiga gari, sai ya tambaye shi ya ce, “Ina roƙonka ka nuna mini gidan mai duba?”
19 And Samuel responded to Saul, saying: “I am the seer. Ascend before me to the high place, so that you may eat with me today. And I will send you away in the morning. And I shall reveal to you everything that is in your heart.
Sama’ila ya ce, “Ni ne mai duban, ka yi gaba zuwa ka tudu, gama yau za ka ci tare da ni, da safe kuma in sallame ka, in gaya muku duk abin da yake a zuciyarku.
20 And concerning the donkeys, which were lost the day before yesterday, you should not be anxious, for they have been found. And all the best things of Israel, for whom should they be? Will they not be for you and for all your father’s house?”
Game da jakunan da suka ɓace kwana uku kuwa, kada ka damu, an same su. Ga wane ne Isra’ila ta sa dukan zuciya, in ba ga kai da kuma dukan iyalin mahaifinka ba?”
21 And responding, Saul said: “Am I not a son of Benjamin, the least tribe of Israel, and are not my kindred the last among all the families from the tribe of Benjamin? So then, why would you speak this word to me?”
Shawulu ya ce, “Ashe, ni ba mutumin Benyamin ba ne daga ƙaramar kabila ta Isra’ila? Dangina kuma ba shi ba ne mafi kakanni a cikin kabilar Benyamin ba? Yaya za ka faɗa mini irin wannan magana.”
22 And so Samuel, taking Saul and his servant, brought them into the dining room, and he gave them a place at the head of those who had been invited. For there were about thirty men.
Sa’an nan Sama’ila ya shiga da Shawulu da baransa ya zaunar da su a gaban waɗanda aka gayyata, mutanen sun kai wajen mutum talatin.
23 And Samuel said to the cook, “Present the portion that I gave to you, and which I instructed you to set apart beside you.”
Sama’ila ya ce wa mai dahuwa, “Kawo naman da na ba ka, wannan da na ce ka ajiye dabam.”
24 Then the cook lifted up the shoulder, and he placed it before Saul. And Samuel said: “Behold, what remains, set it before you and eat. For it was preserved for you intentionally, when I called the people.” And Saul ate with Samuel on that day.
Sai mai dahuwan ya ɗauko cinya da abin da yake bisanta ya kawo ya ajiye a gaban Shawulu. Sama’ila ya ce, “Ga abin da aka ajiye dominka. Ka ci, gama an keɓe shi dominka saboda wannan hidima daga lokacin da na ce, ‘Na gayyaci baƙi.’” Shawulu kuwa ya ci tare da Sama’ila a ranan nan.
25 And they descended from the high place into the town, and he spoke with Saul in the upper room. And he set out a bed for Saul in the upper room, and he slept.
Bayan suka gangaro daga tudu zuwa cikin gari, Sai Sama’ila ya yi magana da Shawulu a ɗakin samansa.
26 And when they had risen in the morning, and it now began to be light, Samuel called to Saul in the upper room, saying, “Rise up, so that I may send you on.” And Saul rose up. And they both departed, that is to say, he and Samuel.
Da asuba sai suka tashi, Sama’ila ya kira Shawulu daga ɗakin sama ya ce, “Ka shirya, zan sallame ka.” Da Shawulu ya shirya, sai Sama’ila da Shawulu suka fita waje tare.
27 And as they were descending to the very limit of the city, Samuel said to Saul: “Tell the servant to go ahead of us, and to continue on. But as for you, stay here a little while, so that I may reveal the word of the Lord to you.”
Suna dab da ƙarshen gari, sai Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Ka ce wa bawanka yă yi gaba, kai ka ɗan dakata a nan tukuna, domin in ba ka saƙo daga Allah.”

< 1 Samuel 9 >