< 1 Samuel 8 >

1 And it happened that, when Samuel had become old, he appointed his sons as judges over Israel.
Da Sama’ila ya tsufa, sai ya naɗa’ya’yansa maza su zama alƙalan Isra’ila.
2 Now the name of his firstborn son was Joel, and the name of the second was Abijah: judges at Beersheba.
Sunan ɗansa na fari Yowel, na biyu kuwa Abiya. Suka yi alƙalanci a Beyersheba.
3 But his sons did not walk in his ways. Instead, they turned aside, pursuing avarice. And they accepted bribes, and they perverted judgment.
Amma’ya’yansa ba su bi hanyar mahaifinsu ba. Suka mai da hankalinsu ga neman kuɗi da cin hanci, suna kuma danne gaskiya.
4 Therefore, all those greater by birth of Israel, having gathered together, went to Samuel at Ramah.
Sai dukan shugabannin Isra’ila suka taru suka zo wurin Sama’ila a Rama.
5 And they said to him: “Behold, you are elderly, and your sons do not walk in your ways. Appoint for us a king, so that he may judge us, just as all the nations have.”
Suka ce masa, “Ka tsufa,’ya’yanka kuma ba sa bin hanyarka, saboda haka sai ka naɗa sarkin da zai bi da mu kamar yadda sauran ƙasashe suke da su.”
6 And the word was displeasing in the eyes of Samuel, for they had said, “Give us a king to judge us.” And Samuel prayed to the Lord.
Amma Sama’ila bai ji daɗi sa’ad da suka ce, “Ka ba mu sarki da zai bi da mu.” Sai ya yi addu’a ga Ubangiji.
7 Then the Lord said to Samuel: “Listen to the voice of the people in all that they are saying to you. For they have not rejected you, but me, lest I reign over them.
Ubangiji kuwa ya ce masa, “Ka saurari dukan maganganun da mutanen suke gaya maka. Ai, ba kai ba ne suka ƙi, ni ne suka ƙi in zama sarkinsu.
8 In accord with all their works, which they have done from the day when I led them away from Egypt, even to this day: just as they have forsaken me, and served foreign gods, so now they also do to you.
Haka suka yi daga tun daga ranar da na fitar da su daga Masar har zuwa yau, suka ƙi ni, suka bauta wa waɗansu alloli, haka ma suke yi maka.
9 Now therefore, hear their voice. Yet truly, testify to them and foretell to them the rights of the king who will reign over them.”
Yanzu ka saurare su amma ka yi musu kashedi sosai, ka sa su san abin da sarkin da zai bi da su zai yi.”
10 And so, Samuel told all the words of the Lord to the people, who had petitioned a king from him.
Sama’ila kuwa ya ce wa mutanen da suke roƙo yă naɗa musu sarki dukan abin da Ubangiji ya faɗa.
11 And he said: “This will be the right of the king who will have authority over you: He will take your sons, and place them in his chariots. And he will make them his horsemen and his runners before his four-horse chariots.
Ya ce musu, “Ga abin da sarkin da zai yi mulkinku zai yi. Zai kwashe’ya’yanku yă sa su yi aiki da kekunan yaƙi da dawakansa, waɗansu za su riƙa gudu a gaban keken yaƙinsa.
12 And he will appoint them to be his tribunes and centurions, and the plowmen of his fields, and the harvesters of the grain, and the makers of his weapons and chariots.
Zai sa waɗansu su zama shugabannin mutum dubu-dubu da kuma na hamsin-hamsin. Waɗansu za su yi masa noma da girbi. Waɗansu za su ƙera masa makaman yaƙi da kayayyaki don keken yaƙinsa.
13 Likewise, your daughters he will take for himself as makers of ointments, and as cooks and bakers.
Zai sa’ya’yanku mata yin aikin turare da dafe-dafe da kuma toye-toye.
14 Also, he will take your fields, and your vineyards, and your best olive groves, and he will give them to his servants.
Zai karɓi gonakinku mafi kyau da gonakin inabinku da gonakin zaitunku yă ba wa ma’aikatansa.
15 Moreover, he will take one tenth of your grain and of the results of your vineyards, so that he may give these to his eunuchs and servants.
Zai kuma karɓi zakan hatsinku da na inabinku yă ba shugabannin fadarsa da sauran masu hidimarsa.
16 Then, too, he will take your servants, and handmaids, and your best young men, and your donkeys, and he will set them to his work.
Zai ƙwace bayinku maza da mata, da shanunku, da jakunanku mafi kyau domin su yi masa aiki.
17 Also, he will take a tenth of your flocks. And you will be his servants.
Zai karɓi zakan dabbobinku, ku kanku za ku zama bayinsa.
18 And you will cry out, in that day, from the face of the king, whom you have chosen for yourselves. And the Lord will not heed you, in that day. For you requested a king for yourselves.”
Sa’ad da ranar ta zo, za ku yi kuka ku nemi a fishe ku daga sarkin da kuka zaɓa, Ubangiji kuwa ba zai ji ku ba.”
19 But the people were not willing to listen to the voice of Samuel. Instead, they said: “By no means! For there shall be a king over us,
Amma mutanen suka ƙi jin Sama’ila, sai suka ce, “A’a, mu dai, muna son sarki yă bi da mu.”
20 and we shall be just like all the Gentiles. And our king will judge us, and he will go out before us, and he will fight our wars for us.”
Ta haka za mu zama kamar sauran ƙasashe, mu kasance da sarkin da zai bi da mu, yă tafi tare da mu zuwa yaƙe-yaƙe.
21 And Samuel heard all the words of the people, and he spoke them to the ears of the Lord.
Da Sama’ila ya ji duk maganganun da mutanen suka faɗa, sai ya mayar wa Ubangiji.
22 Then the Lord said to Samuel, “Listen to their voice, and appoint a king over them.” And Samuel said to the men of Israel, “Let each one go to his own city.”
Ubangiji kuwa ya ce, “Ka saurare su, ka naɗa masu sarki.” Sa’an nan Sama’ila ya ce wa mutanen Isra’ila, “Kowa yă koma garinsa.”

< 1 Samuel 8 >