< 1 Samuel 29 >

1 Then all the troops of the Philistines were gathered together at Aphek. But Israel also made camp, above the spring which is in Jezreel.
Filistiyawa suka tattara dukan rundunoninsu a Afek. Isra’ila kuwa suka yi sansani kusa da maɓulɓular da take Yezireyel.
2 And indeed, the princes of the Philistines advanced by hundreds and by thousands; but David and his men were in the rear with Achish.
Sa’ad da sarakuna Filistiyawa suke wucewa da rundunarsu na mutum ɗari-ɗari da na dubu-dubu. Dawuda da mutanensa suna biye a baya tare da Akish.
3 And the leaders of the Philistines said to Achish, “What do these Hebrews intend to do?” And Achish said to the leaders of the Philistines: “Could you be ignorant about David, who was the servant of Saul, the king of Israel, and who has been with me for many days, even years, and I have not found within him anything, from the day that he fled to me, even to this day?”
Komandodin Filistiyawa suka ce, “Waɗannan Ibraniyawa kuma fa?” Akish ya ce, “Wannan shi ne Dawuda hafsan Shawulu, sarkin Isra’ila. Yana nan tare da ni shekara guda ke nan. Ban kuwa taɓa samunsa da wani lahani ba tun daga ranar da ya bar Shawulu.”
4 Then the leaders of the Philistines became angry against him, and they said to him: “Let this man return, and let him settle in his place, which you appointed for him. But let him not descend with us to battle, lest he become an adversary to us when we begin to fight. For in what other way will he be able to please his lord, except with our heads?
Amma komandodin Filistiyawa suka yi fushi, suka ce, “Ka sa mutumin nan yă koma zuwa wurin da ka ba shi yă zauna. Ba zai bi mu zuwa wurin yaƙi ba. Yana iya juya a kanmu lokacin yaƙin. Zai iya yin amfani da wannan zarafi yă ciccire kawunanmu don yă faranta wa maigidansa rai?
5 Is not this the David, about whom they were singing, while dancing, saying: ‘Saul struck down his thousands, but David his ten thousands?’”
Tuna fa, ba shi ne Dawuda ɗin da ake girmama da rawa da waƙoƙi ana cewa, “‘Shawulu ya kashe dubbai, Dawuda kuwa dubbun dubbai ba’?”
6 Therefore, Achish called David, and he said to him: “As the Lord lives, you are good and righteous in my sight, even in your departure and your return with me in the military camp. And I have not found anything evil in you, from the day that you came to me, even to this day. But you are not pleasing to the princes.
Saboda haka Akish ya kira Dawuda ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, na amince da kai tun daga ranar da ka zo wurina har yă zuwa yau, ban same ka da wani laifi ba, na kuma yi farin ciki in sa ka a cikin sojojina don ka yi mini aiki. Amma masu mulki nawa ba su yarda da kai ba.
7 Therefore, return, and go in peace, so that you do not offend the eyes of the princes of the Philistines.”
Sai ka juya ka koma ka isa lafiya ba tare da ɓata wa masu mulkin Filistiyawa rai ba.”
8 And David said to Achish, “But what have I done, or what have you found in me, your servant, from the day that I was in your sight to this day, so that I may not go out and fight against the enemies of my lord, the king?”
Dawuda ya ce wa Akish, “Me na yi? Ka taɓa samun bawanka da laifi tun daga ranar da na zo har zuwa yanzu? Ina dalilin da ba zan tafi tare da kai in yaƙi maƙiyin ranka yă daɗe, sarki ba?”
9 And in response, Achish said to David: “I know that you are good in my sight, like an angel of God. But the leaders of the Philistines have said: ‘He shall not go up with us to the battle.’
Akish ya ce, “A ganina kai marar laifi ne kamar mala’ikan Allah, duk da haka shugabannin sojojin Filistiyawa sun ce, ‘Ba zai tafi yaƙi tare da mu ba.’
10 And so, rise up in the morning, you and the servants of your lord who came with you. And when you have risen up in the night, as it begins to be light, go forth.”
Ka tashi da sassafe, kai da bayin shugabanka da suka zo tare da kai. Da gari ya waye sai ku kama hanya.”
11 And so David rose up in the night, he and his men, so that they might set out in the morning. And they returned to the land of the Philistines. But the Philistines ascended to Jezreel.
Gari na wayewa tun da sassafe Dawuda da mutanensa suka tashi suka kama hanyar komawa ƙasar Filistiyawa. Filistiyawa kuwa suka haura zuwa Yezireyel.

< 1 Samuel 29 >