< 1 Kings 15 >

1 Then, in the eighteenth year of the reign of Jeroboam, the son of Nebat, Abijam reigned over Judah.
A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yerobowam ɗan Nebat, Abiyam ya zama sarkin Yahuda,
2 He reigned for three years in Jerusalem. The name of his mother was Maacah, the daughter of Abishalom.
ya kuma yi mulki a Urushalima shekara uku. Sunan mahaifiyarsa Ma’aka ne,’yar Abisalom.
3 And he walked in all the sins of his father, which he had done before him. Neither was his heart perfect with the Lord his God, as was the heart of David, his father.
Shi ma ya aikata dukan irin zunubai da tsohonsa ya yi. Zuciyarsa ba tă bi Ubangiji Allahnsa, kamar yadda zuciyar Dawuda kakansa ta yi ba.
4 But for the sake of David, the Lord his God gave to him a lamp in Jerusalem, so that he might raise up his son after him, and so that he might establish Jerusalem.
Duk da haka, saboda Dawuda Ubangiji Allahnsa ya ba shi fitila a Urushalima ta wurin ta da wani da ya gāje shi, ta wurinsa kuma Urushalima ta yi ƙarfi.
5 For David had done what was right in the eyes of the Lord, and he had not declined from all of the things that he had instructed to him, during all the days of his life, except the matter of Uriah, the Hittite.
Gama Dawuda ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, bai kuma fasa kiyaye wani daga umarnan Ubangiji ba dukan kwanakinsa, sai dai a batun Uriya mutumin Hitti.
6 Now there was war between Rehoboam and Jeroboam during the entire time of his life.
Aka yi yaƙi tsakanin Rehobowam da Yerobowam a duk kwanakin Abiya.
7 And the rest of the words of Abijam, and all that he did, were these not written in the book of the words of the days of the kings of Judah? And there was fighting between Abijam and Jeroboam.
Game da sauran ayyukan mulkin Abiyam kuwa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. Aka yi yaƙi tsakanin Abiyam da Yerobowam.
8 And Abijam slept with his fathers, and they buried him in the city of David. And Asa, his son, reigned in his place.
Sai Abiyam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Asa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
9 Then, in the twentieth year of Jeroboam, the king of Israel, Asa reigned as king of Judah.
A shekara ta ashirin ta Yerobowam sarkin Isra’ila, Asa ya zama sarkin Yahuda,
10 And he reigned for forty-one years in Jerusalem. The name of his mother was Maacah, the daughter of Abishalom.
ya yi mulki a Urushalima shekara arba’in da ɗaya. Sunan mahaifiya mahaifiyarsa, Ma’aka ne’yar Abisalom.
11 And Asa did what was right before the sight of the Lord, just as his father David did.
Asa ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar yadda kakansa Dawuda ya yi.
12 And he took away the effeminate from the land. And he purged all the filth of the idols, which his fathers had made.
Ya kori dukan maza karuwai na masujadai daga ƙasar, ya kuma yi waje da dukan gumakan da mahaifinsa ya yi.
13 Moreover, he also removed his mother, Maacah, from being the leader in the sacrifices of Priapus, and in his sacred grove which she had consecrated. And he destroyed his grotto. And he shattered the very indecent idol, and he burned it at the torrent Kidron.
Ya tuɓe mahaifiya mahaifiyarsa Ma’aka daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, gama ta gina ƙazantaccen ginshiƙin Ashera. Asa ya yanke ginshiƙin, ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
14 But the high places, he did not take away. Yet truly, the heart of Asa was perfect with the Lord during all his days.
Ko da yake bai cire masujadai da suke kan tuddai ba, zuciyar Asa ta kasance da aminci ɗungum ga Ubangiji dukan kwanakinsa.
15 And he brought the things that his father had sanctified and vowed back to the house of the Lord: the silver, and the gold, and the vessels.
Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyakin da shi da mahaifinsa suka keɓe a haikalin Ubangiji.
16 Now there was war between Asa and Baasha, the king of Israel, during all their days.
Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
17 And Baasha, the king of Israel, ascended against Judah. And he built up Ramah, so that no one would be able to exit or enter from the side of Asa, the king of Judah.
Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura, ya yi yaƙi da Yahuda, ya kuma gina Rama don yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa, sarkin Yahuda.
18 And so, Asa took all the silver and the gold which had remained in the treasuries of the house of the Lord, and in the treasuries of the house of the king, and he gave it into the hands of his servants. And he sent them to Benhadad, the son of Tabrimmon, the son of Hezion, the king of Syria, who was living in Damascus, saying:
Sai Asa ya ɗauki dukan azurfa da kuma zinariyar da suka rage a ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma nasa fadan, ya ba da su ga wani shugabansa, ya kuma aika da su zuwa ga Ben-Hadad ɗan Tabrimmon, ɗan Heziyon, sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
19 “There is a pact between me and you, and between my father and your father. For this reason, I have sent to you gifts of silver and of gold. And I ask you to go and break your pact with Baasha, the king of Israel, so that he may withdraw from me.”
Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakanina da kai, kamar yadda ta kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Duba, ina aika maka kyautai na azurfa da na zinariya. Yanzu fa sai ka janye yarjejjeniyarka da Ba’asha sarkin Isra’ila, don yă janye daga gare ni.”
20 Benhadad, acquiescing to king Asa, sent the leaders of his army against the cities of Israel. And they struck Ijon, and Dan, and Abel, the house of Maacah, and all of Chinneroth, that is, all the land of Naphtali.
Ben-Hadad ya yarda da maganar Sarki Asa, ya kuma aika shugabannin sojojin mayaƙansa ya yi yaƙi da garuruwan Isra’ila. Ya kame Iyon, Dan, Abel-Bet-Ma’aka da dukan Kinneret, haɗe da Naftali.
21 And when Baasha had heard this, he ceased from fortifying Ramah, and he returned to Tirzah.
Da Ba’asha ya ji haka, sai ya daina ginin Rama, ya janye zuwa Tirza.
22 Then king Asa sent an announcement to all of Judah, saying, “Let no one be excused.” And they took away the stones from Ramah, and its timber, with which Baasha had fortified it. And from these things, king Asa built up Geba of Benjamin and Mizpah.
Sai Sarki Asa ya ba da umarni ga dukan Yahuda, kuma babu wanda aka ware, kowa yă taimaka a kwashe duwatsu da katakan da Ba’asha yake amfani da su daga Rama. Da duwatsu da katakan ne Sarki Asa ya gina Geba a Benyamin da kuma Mizfa.
23 Now all the rest of the words of Asa, and his entire strength, and all that he did, and the cities that he built, were these not written in the book of the words of the days of the kings of Judah? Yet truly, in the time of his old age, he was afflicted in his feet.
Game da sauran ayyukan mulkin Asa, dukan nasarorinsa, dukan abin da ya yi, da kuma biranen da ya gina, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. A tsufansa, sai ƙafafunsa suka kamu da cuta.
24 And he slept with his fathers, and he was buried with them in the city of David, his father. And Jehoshaphat, his son, reigned in his place.
Sai Asa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a birnin kakansa Dawuda. Sai Yehoshafat ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
25 Yet truly, Nadab, the son of Jeroboam, reigned over Israel, in the second year of Asa, the king of Judah. And he reigned over Israel for two years.
Nadab ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a shekara ta biyu ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila shekara biyu.
26 And he did what is evil in the sight of the Lord. And he walked in the ways of his father and in his sins, by which he caused Israel to sin.
Ya yi mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin mahaifinsa da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
27 Then Baasha, the son of Ahijah, from the house of Issachar, set an ambush against him, and he struck him down at Gibbethon, which is a city of the Philistines. For indeed, Nadab and all of Israel were laying siege to Gibbethon.
Ba’asha ɗan Ahiya na gidan Issakar ya yi maƙarƙashiya gāba da shi, ya buge shi a Gibbeton, a wani garin Filistiyawa, yayinda Nadab da dukan Isra’ila suke wa garin kwanto.
28 And so Baasha killed him in the third year of Asa, the king of Judah, and he reigned in his place.
Ba’asha ya kashe Nadab a shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma gāje shi a matsayin sarki.
29 And when he had reigned, he struck down the entire house of Jeroboam. He did not leave behind even one soul from his offspring, until he had wiped him away, in accord with the word of the Lord, which he had spoken by the hand of Ahijah, the Shilonite,
Nan da nan da ya fara mulki, sai ya kashe dukan iyalin Yerobowam. Bai bar wa Yerobowam wani da rai ba, amma ya hallaka su duka, bisa ga maganar Ubangiji da ya ba wa bawansa Ahiya, mutumin Shilo.
30 because of the sin of Jeroboam, which he had committed, and by which he had caused Israel to sin, and because of the offense by which he had provoked the Lord, the God of Israel.
Wannan abu ya faru saboda zunuban da Yerobowam ya yi, ya kuma sa Isra’ila ya yi, kuma saboda ya tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya yi fushi.
31 But the rest of the words of Nadab, and all that he did, were these not written in the book of the words of the days of the kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Nadab da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
32 And there was war between Asa and Baasha, the king of Israel, during all their days.
Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
33 In the third year of Asa, the king of Judah, Baasha, the son of Ahijah, reigned over all of Israel, at Tirzah, for twenty-four years.
A shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, Ba’asha ɗan Ahiya ya zama sarkin dukan Isra’ila a Tirza, ya kuma yi sarauta shekara ashirin da huɗu.
34 And he did evil in the sight of the Lord. And he walked in the ways of Jeroboam, and in his sins, by which he caused Israel to sin.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin Yerobowam da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.

< 1 Kings 15 >