< 1 Kings 12 >

1 Then Rehoboam went to Shechem. For in that place, all of Israel had gathered to appoint him as king.
Rehobowam ya tafi Shekem, gama dukan Isra’ila sun je can don su naɗa shi sarki.
2 Yet truly, Jeroboam, the son of Nebat, while he was still in Egypt as a fugitive from the face of king Solomon, hearing of his death, returned from Egypt.
Sa’ad da Yerobowam ɗan Nebat ya ji labari (gama har yanzu yana a Masar, inda ya gudu daga Sarki Solomon), sai ya dawo daga Masar.
3 And they sent and called him. Therefore, Jeroboam went, with the entire multitude of Israel, and they spoke to Rehoboam, saying:
Saboda haka mutane suka aika Yerobowam yă zo, sai shi da dukan taron Isra’ila suka tafi wurin Rehobowam, suka ce masa,
4 “Your father imposed a very harsh yoke upon us. And so, you should now take away a little from the very harsh rule of your father and from his very grievous yoke, which he imposed upon us, and we will serve you.”
“Mahaifinka ya sa mana kaya mai nauyin gaske, amma yanzu ka sassauta wannan aiki mai zafi, da kuma kaya masu nauyin da ya sa a kanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
5 And he said to them, “Go away, until the third day, and then return to me.” And when the people had gone away,
Rehobowam ya amsa, “Ku tafi, bayan kwana uku, ku dawo.” Sai mutane suka watse.
6 king Rehoboam took counsel with the elders who had assisted before his father Solomon while he was still living. And he said, “What counsel do you give to me, so that I may respond to this people?”
Sai Sarki Rehobowam ya nemi shawarar dattawa waɗanda suka yi wa mahaifinsa Solomon, hidima a kwanakinsa. Ya ce, “Wace shawara ce za ku ba ni don in amsa wa waɗannan mutane?”
7 They said to him, “If today you will obey and serve this people, and yield to their petition, and if you will speak lenient words to them, they will be your servants for all days.”
Suka amsa, “In a yau za ka zama bawan waɗannan mutane, ka kuma yi musu hidima, ka ba su amsa mai kyau, kullum za su kasance bayinka.”
8 But he abandoned the counsel of the old men, which they had given to him. And he consulted the young men who had been raised with him, and who were assisting him.
Amma Rehobowam ya ƙi shawarar da dattawan suka ba shi, sai ya nemi shawarar matasa waɗanda suka yi girma tare, waɗanda kuma suke masa hidima.
9 And he said to them: “What counsel do you give to me, so that I may respond to this people, who have said to me: ‘Make light the yoke that your father imposed on us?’”
Ya tambaye su, “Mece ce shawararku? Yaya za mu amsa wa waɗannan mutane masu cewa, ‘Ka sassauta nauyin da mahaifinka ya sa a kanmu’?”
10 And the young men who had been raised with him, said: “You shall speak in this way to this people, who have spoken to you, saying: ‘Your father weighed down our yoke. You should relieve us.’ You shall say this to them: ‘My little finger is thicker than the back of my father.
Matasan, waɗanda suka yi girma tare da shi, suka amsa, “Faɗa wa waɗannan mutanen da suka ce maka, ‘Mahaifinka ya sa kaya masu nauyi a kanmu, amma ka sassauta kayanka.’ Ka ce musu, ‘Ƙaramin yatsana ya fi ƙugun tsohona kauri.
11 And now, my father placed a heavy yoke upon you, but I will add more upon your yoke. My father cut you with whips, but I will beat you with scorpions.’”
Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; ni zan ma sa su fi haka nauyi. Mahaifina ya hore ku da bulala; ni kuwa zan hore ku da kunamai.’”
12 Therefore, Jeroboam and all the people went to Rehoboam on the third day, just as the king had spoken, saying, “Return to me on the third day.”
Bayan kwana uku, Yerobowam da dukan mutane suka dawo wurin Rehobowam yadda sarki ya faɗa, “Ku dawo gare ni cikin kwana uku.”
13 And the king responded to the people harshly, leaving behind the counsel of the elders that they had given to him.
Sai Sarki ya amsa wa mutane da zafi. Yana ƙin shawarar da dattawa suka ba shi.
14 And he spoke to them according to the counsel of the young men, saying: “My father weighed down your yoke, but I will add more to your yoke. My father cut you with whips, but I will beat you with scorpions.”
Ya bi shawarar matasa, ya ce, “Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; ni zan ma sa su fi haka nauyi. Mahaifina ya hore ku da bulala; ni kuwa zan hore ku da kunamai.”
15 And the king did not acquiesce to the people. For the Lord had turned him away, so that he might raise up his word, which he had spoken by the hand of Ahijah, the Shilonite, to Jeroboam, the son of Nebat.
Saboda haka sarki bai saurare mutane ba, gama wannan abin da ya faru daga wurin Ubangiji ne, don a cika maganar Ubangiji da ya yi wa Yerobowam ɗan Nebat ta wurin Ahiya, mutumin Shilo.
16 And so the people, seeing that the king had not been willing to listen to them, responded to him, saying: “What part do we have in David? Or what inheritance do we have in the son of Jesse? Go to your own tents, O Israel. Now David, see to your own house.” And Israel went away to their own tents.
Da dukan Isra’ila suka ga sarki ya ƙi yă saurare su, sai suka amsa wa sarki, “Ina ruwanmu da Dawuda! Ai! Ba mu da gādo wurin ɗan Yesse. Ya Isra’ila, kowa yă koma tentinsa! Dawuda, sai ka lura da gidanka!” Saboda haka Isra’ilawa suka watse zuwa gida.
17 But over all the sons of Israel who were living in the cities of Judah, Rehoboam reigned.
Amma ga Isra’ilawan da suke zama a garuruwan Yahuda kuwa, Rehobowam ya ci gaba da mulki a kansu.
18 Then king Rehoboam sent Adoram, who was over the tribute. And all of Israel stoned him, and he died. Therefore, king Rehoboam hurrying, climbed into the chariot, and fled to Jerusalem.
Sarki Rehobowam ya aiki Adoniram wanda yake shugaban aikin gandu, amma Isra’ila suka jajjefe shi da dutse har ya mutu. Sarki Rehobowam, ya sullale ya hau keken yaƙinsa ya tsere zuwa Urushalima.
19 And Israel drew away from the house of David, even to the present day.
Tun daga wannan ranar ne mutanen Isra’ila suka shiga gāba da gidan Dawuda har wa yau.
20 And it happened that, when all of Israel had heard that Jeroboam had returned, gathering an assembly, they sent and called him, and they appointed him as king over all of Israel. And no one followed the house of David, except the tribe of Judah alone.
Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ji Yerobowam ya dawo, sai suka aika, suka kira shi zuwa taro, suka kuma naɗa shi sarki bisa dukan Isra’ila. Kabila Yahuda kaɗai ta kasance mai biyayya ga gidan Dawuda.
21 Then Rehoboam went to Jerusalem, and he gathered together the entire house of Judah, and the tribe of Benjamin, one hundred and eighty thousand elect men of war, so that they might fight against the house of Israel, and might bring the kingdom back to Rehoboam, the son of Solomon.
Da Rehobowam ya isa Urushalima, ya tattara dukan gidan Yahuda da kabilar Benyamin, ya sami sun kai mayaƙa dubu da tamanin. Sai aka shirya don su yaƙi gidan Isra’ila, su kuma mayar da masarautar wa Rehobowam ɗan Solomon.
22 But the word of the Lord came to Shemaiah, the man of God, saying:
Amma waɗannan kalmomin Allah suka zo wa Shemahiya, mutumin Allah, cewa,
23 “Speak to Rehoboam, the son of Solomon, the king of Judah, and to all the house of Judah, and to Benjamin, and to the rest of the people, saying:
“Faɗa wa Rehobowam ɗan Solomon, sarkin Yahuda, ka faɗa wa dukan gidan Yahuda da Benyamin, da kuma dukan sauran mutane,
24 ‘Thus says the Lord: You shall not go up, and you shall not make war against your brothers, the sons of Israel. Let each man return to his own house. For this word came from me.’” And they listened to the word of the Lord, and they returned from the journey, as the Lord had instructed them.
‘Ga abin da Ubangiji ya ce, “Kada ku haura don ku yi yaƙi da’yan’uwanku, Isra’ilawa. Ku koma gida, kowannenku, gama wannan aikina ne.”’” Saboda haka suka yi biyayya da maganar Ubangiji, suka sāke watse zuwa gida, yadda Ubangiji ya umarta.
25 Then Jeroboam built up Shechem, on mount Ephraim, and he lived there. And departing from there, he built up Penuel.
Sai Yerobowam ya ƙara gina Shekem a ƙasar tudu ta Efraim, ya zauna a can. Daga can ya tafi ya gina Fenuwel.
26 And Jeroboam said in his heart: “Now the kingdom will return to the house of David,
Yerobowam ya yi tunani a ransa ya ce, “Mai yiwuwa mulkin yă koma gidan Dawuda.
27 if this people ascend to offer sacrifices in the house of the Lord at Jerusalem. And the heart of this people will be converted to their lord Rehoboam, the king of Judah, and they will put me to death, and return to him.”
In waɗannan mutane sun riƙa haurawa don su miƙa hadayu a haikalin Ubangiji a Urushalima. Za su sāke nuna biyayya ga mai girma, Rehobowam, sarkin Yahuda. Za su kashe ni su kuma koma ga Sarki Rehobowam.”
28 And devising a plan, he made two golden calves. And he said to them: “No longer choose to ascend to Jerusalem. Behold, these are your gods, O Israel, who led you away from the land of Egypt!”
Bayan ya nemi shawara, sai sarki ya yi siffofin’yan maruƙa biyu na zinariya. Ya ce wa mutane, “Kun daɗe kuna haurawa zuwa can Urushalima. Ga allolinku, ya Isra’ila, waɗanda suka fitar da ku daga ƙasar Masar.”
29 And he stationed one in Bethel, and the other in Dan.
Sai ya kafa ɗaya a Betel, ɗaya kuma a Dan.
30 And this word became an occasion of sin. For the people went to adore the calf, even to Dan.
Wannan ya zama zunubi, gama mutane suna tafiya yin wa wannan da yake a Betel sujada, su kuma je har Dan don su yi wa ɗayan sujada.
31 And he made shrines on the high places, and he made priests out of the lowest people, who were not of the sons of Levi.
Yerobowam ya gina masujadai da suke kan tuddai, ya kuma naɗa firistoci barkatai daga cikin mutanen da ba na zuriyar Lawi ba.
32 And he appointed a solemn day in the eighth month, on the fifteenth day of the month, in imitation of the solemnity that was celebrated in Judah. And ascending to the altar, he acted similarly in Bethel, so that he immolated to the calves, which he had made. And in Bethel, he appointed priests of the high places, which he had made.
Ya kafa biki a rana ta goma sha biyar ta watan takwas, kamar bikin da ake yi a Yahuda, ya kuma miƙa hadayu a bisa bagade. Ya yi haka a Betel, yana miƙa wa siffofin maruƙan da ya yi hadayu. A Betel kuma ya naɗa firistoci a wuraren tudun da ya yi.
33 And he ascended to the altar, which he had raised up in Bethel, on the fifteenth day of the eighth month, the day that he had decided in his own heart. And he made a solemnity to the sons of Israel, and he ascended to the altar, so that he might burn incense.
A rana ta goma sha biyar ta watan takwas, watan da ya zaɓa, ya miƙa hadayu a bisa bagaden da ya gina a Betel. Saboda haka ya kafa biki don Isra’ilawa, ya kuma haura zuwa bagade don yă miƙa hadayu.

< 1 Kings 12 >