< 1 Chronicles 28 >

1 And so David called together all the leaders of Israel, the rulers of the tribes, and those in charge of the companies, who were ministering to the king, and also the tribunes and centurions, and those in charge of the substance and possessions of the king, and his sons, with the eunuchs and the powerful and those most experienced in the army, at Jerusalem.
Dawuda ya sa aka kira dukan shugabannin Isra’ila su taru a Urushalima, shugabannin kabilu, manyan hafsoshin ɓangarorin hidimar sarki, manyan hafsoshin dubu-dubu da manyan hafsoshin ɗari-ɗari, da kuma shugabanni masu lura da dukan mallaka da dabbobin da suke na sarki da kuma’ya’yansa maza, tare da fadawa, jarumawa da kuma dukan mayaƙa masu kwarjini.
2 And when the king had risen up and was standing, he said: “Listen to me, my brothers and my people. I thought that I would build a house, in which the ark of the covenant of the Lord, the footstool of our God, might rest. And so I prepared everything for its building.
Sarki Dawuda ya miƙe tsaye ya ce, “Ku saurare ni,’yan’uwana da kuma mutanena. Na yi niyya in gina gida a matsayin wurin hutu domin akwatin alkawarin Ubangiji, domin zatin Allahnmu, na kuma yi shiri don in gina shi.
3 But God said to me: ‘You shall not build a house to my name, because you are a man of war, and have shed blood.’
Amma Allah ya ce mini, ‘Ba za ka gina gida domin Sunana ba, saboda kai mayaƙi ne ka kuma zub da jini.’
4 Now the Lord God of Israel chose me, out of the entire house of my father, so that I would be king over Israel forever. For from Judah he chose leaders; then from the house of Judah he chose the house of my father; and from the sons of my father, it pleased him to choose me as king over all of Israel.
“Duk da haka Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya zaɓe ni daga dukan iyalina don in zama sarki bisa Isra’ila har abada. Ya zaɓi Yahuda a matsayin shugaba, kuma daga gidan Yahuda ya zaɓi iyalina, daga’ya’yan mahaifina maza kuwa ya gamsu ya mai da ni sarki bisa dukan Isra’ila.
5 Then too, among my sons (for the Lord has given me many sons) he chose Solomon my son, so that he would sit upon the throne of the kingdom of the Lord, over Israel.
Cikin dukan’ya’yana maza, Ubangiji kuwa ya ba ni su da yawa, ya zaɓi ɗana Solomon yă zauna a kujerar mulkin Ubangiji a bisa Isra’ila.
6 And he said to me: ‘Solomon your son shall build my house and my courts. For I have chosen him to be to me as a son, and I will be to him as a father.
Ya ce mini, ‘Solomon ɗanka shi ne wanda zai gina gidana da filayen da suke kewaye da shi, gama na zaɓe shi yă zama ɗana, ni kuma zan zama mahaifinsa.
7 And I will make firm his kingdom, even unto eternity, if he will persevere in doing my precepts and judgments, as also today.’
Zan kafa mulkinsa har abada in bai kauce ga kiyaye umarnaina da dokokina ba, yadda ake yi a wannan lokaci.’
8 Now therefore, before the entire assembly of Israel, in the hearing of our God, keep and seek all the commandments of the Lord our God, so that you may possess the good land, and may bequeath it to your sons after you, even forever.
“Saboda haka yanzu ina umartanku a gaban dukan Isra’ila da na taron jama’ar Ubangiji, da kuma a kunnuwan Allahnmu. Ku yi hankali ku kiyaye dukan umarnan Ubangiji Allahnku don ku mallaki wannan kyakkyawar ƙasa ku kuma bar wa zuriyarku gādo har abada.
9 And as for you, my son Solomon, know the God of your father, and serve him with a perfect heart and a willing mind. For the Lord searches all hearts, and understands the thoughts of all minds. If you seek him, you will find him. But if you abandon him, he will cast you aside for eternity.
“Kai kuma ɗana Solomon, ka san Allah na mahaifinka, ka kuma yi masa hidima da dukan zuciya da kuma yardar rai, gama Ubangiji yana binciken zuciya, yana kuma gane dukan aniyar tunani. In ka neme shi, za ka same shi; amma in ka yashe shi, zai ƙi ka har abada.
10 Now therefore, since the Lord has chosen you, so that you would build the house of the Sanctuary, be strengthened and accomplish it.”
Ka lura fa, gama Ubangiji ya zaɓe ka don ka gina haikali a matsayin wuri mai tsarki. Ka yi ƙarfin hali ka kuma yi aiki.”
11 Then David gave to his son Solomon a description of the portico, and the temple, and the storerooms, and the upper floor, and the innermost rooms, and the house of propitiation,
Sa’an nan Dawuda ya ba ɗansa Solomon tsari domin shirayin haikalin, gine-ginensa, ɗakunan ajiyarsa, ɓangarorin bisansa, ɗakunan cikinsa da kuma wurin kafara.
12 and indeed also of all the courts that he had planned, and the outer rooms on all sides, for the treasuries of the house of the Lord, and for the treasuries of the holy things,
Ya ba shi tsarin dukan abin da Ruhu ya sa a zuciyarsa saboda filayen haikalin Ubangiji da ɗakunan kewaye, da ma’ajin haikalin Allah da kuma baitulmali na kayayyakin da aka keɓe.
13 and for the divisions of the priests and the Levites: concerning all the works of the house of the Lord and all the items in the ministry of the temple of the Lord.
Ya ba shi tsari game ɓangarori na firistoci da Lawiyawa, da game dukan aikin hidima a cikin haikalin Ubangiji, da kuma game da dukan kayayyakin da za a yi amfani da su a hidima.
14 There was gold by weight for every vessel of the ministry, and also silver by weight for the diversity of vessels and equipment.
Ya kimanta yawan zinariya don dukan kayayyakin zinariyar da za a yi amfani a kowane irin hidima, da yawan azurfa don dukan kayayyakin azurfan da za a yi amfani a kowace irin hidima.
15 Then too, he distributed gold for the lampstands and their lamps, according to the measure of each of the lampstands with their lamps. Similarly also, he distributed silver by weight for the silver lampstands with their lamps, according to the diversity of their measure.
Da yawan zinariya don wurin ajiye fitilan fitilu da fitilunsu, da yawan zinariyan da za a yi amfani don kowace fitila da wurin ajiye fitilanta; da kuma yawan azurfa don kowane wurin ajiye fitila da fitilunsa bisa ga yadda za a yi amfani da kowane wurin ajiye fitila;
16 Also, he gave gold for the tables of the presence, according to the diversity of the tables; similarly too, he gave silver for the other tables of silver.
yawan zinariya don kowane tebur saboda burodi mai tsaki; da kuma yawan azurfa saboda teburin azurfa;
17 Also, he distributed from the purest gold for the small hooks and the bowls and the censors, as well as for the little lions of gold, in accord with the precise measure of the weight, for lion after lion. Similarly too, for the lions of silver, he set aside a different weight of silver.
yawan zinariya zalla, don cokula masu yatsu, kwanonin yayyafawa ruwa da kuma tuluna; yawan zinariya don kowane kwanon zinariya; yawan azurfa don kowane kwanon azurfa;
18 Then, for the altar on which the incense was burned, he gave the purest gold. And from the same he made the likeness of the chariot of the Cherubim, with extended wings, which is veiling the ark of the covenant of the Lord.
da kuma yawan tacecciyar zinariya don bagaden turare. Ya kuma ba shi tsari don keken yaƙi, wato, kerubobin zinariyar da suka miƙe fikafikansu suka inuwantar da akwatin alkawarin Ubangiji.
19 “All these things,” he said, “came to me written by the hand of the Lord, so that I would understand all the works of the pattern.”
Dawuda ya ce, “Dukan wannan, ina da shi a rubuce daga hannun Ubangiji zuwa gare ni, ya kuma ba ni ganewa cikin dukan tsarin fasalin, filla-filla.”
20 David also said to his son Solomon: “Act manfully, and be strengthened, and carry it out. You should not be afraid, and you should not be dismayed. For the Lord my God will be with you, and he will not send you away, nor will he abandon you, until you have perfected the entire work of the ministry of the house of the Lord.
Dawuda ya kuma ce wa Solomon ɗansa, “Ka yi ƙarfin hali, ka kuma yi aikin. Kada ka ji tsoro ko ka fid da zuciya, gama Ubangiji Allah, Allahna, yana tare da kai. Ba zai bari ka ji kunya ko yă yashe ka ba, sai an gama dukan aikin saboda hidimar haikalin Ubangiji.
21 Behold, the divisions of the priests and the Levites, for every ministry of the house of the Lord, are standing before you. And they have been prepared, and so they know, both the leaders and the people, how to carry out all your precepts.”
Sassan firistoci da na Lawiyawa suna a shirye domin dukan aiki a haikalin Allah, kuma kowane gwani mai niyya a kowace sana’a, zai taimake ka a cikin dukan aikin. Shugabanni da dukan mutane za su yi biyayya da kowane umarninka.”

< 1 Chronicles 28 >