< 1 Chronicles 27 >

1 Now the sons of Israel, according to their number, the leaders of the families, the tribunes, and the centurions, and the chiefs, who were ministering to the king by their companies, entering and departing in each month of the year as they were in charge, were twenty-four thousand.
Wannan shi ne jerin Isra’ilawa, kawunan iyalai, shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, da manyan ma’aikatansu, waɗanda suka yi wa sarki hidima a dukan abin da ya shafi ɓangarorin mayaƙan da suke aiki wata-wata a dukan shekara. Kowane sashe yana da mutane 24,000.
2 Jashobeam, the son of Zabdiel, was in charge of the first company in the first month; and under him were twenty-four thousand.
Wanda yake lura da sashe na fari, na wata na farko, shi ne Yashobeyam ɗan Zabdiyel. Akwai mutane 24,000 a sashensa.
3 He was from the sons of Perez, and he was the leader of all the other leaders in the army, in the first month.
Shi zuriyar Ferez ne kuma babba na dukan shugabannin mayaƙa don wata na farko.
4 The company of the second month had Dodai, an Ahohite; and after him there was another, named Mikloth, who ruled over a portion of the army of the twenty-four thousand.
Wanda yake lura da sashen don wata na biyu shi ne Dodai mutumin Ahowa; Miklot ne shugaban sashensa. Akwai mutane 24,000 a sashensa.
5 Also, the commander of the third company, in the third month, was Benaiah, the son of Jehoiada the priest; and in his division there were twenty-four thousand.
Shugaban mayaƙa na uku, don wata na uku, shi ne Benahiya ɗan Yehohiyada firist. Shi ne babba kuma akwai mutane 24,000 a sashensa.
6 The same is the Benaiah who was strongest among the thirty, and was above the thirty. But his son, Ammizabad, was in charge of his company.
Wannan shi ne Benahiya wanda yake ɗaya daga cikin jarumawa Talatin nan kuma shi ne yake babba a cikin Talatin ɗin. Ɗansa Ammizabad ne yake lura da sashensa.
7 The fourth, for the fourth month, was Asahel, the brother of Joab, and his son Zebadiah after him; and in his company there were twenty-four thousand.
Na huɗu, don wata na huɗu, shi ne Asahel ɗan’uwan Yowab; ɗansa Zebadiya shi ne magājinsa. Akwai mutane 24,000 a sashensa.
8 The fifth leader, for the fifth month, was Shamhuth, an Izrahite; and in his company there were twenty-four thousand.
Na biyar don wata na biyar, shi ne Shamhut mutumin Izhar shugaban mayaƙa. Akwai mutane 24,000 a sashensa.
9 The sixth, for the sixth month, was Ira, the son of Ikkesh, a Tekoite; and in his company there were twenty-four thousand.
Na shida, don wata na shida, shi ne Ira ɗan Ikkesh mutumin Tekowa. Akwai mutane 24,000 a sashensa.
10 The seventh, for the seventh month, was Helez, a Pelonite from the sons of Ephraim; and in his company there were twenty-four thousand.
Na Bakwai, don wata na bakwai, shi ne Helez mutumin Felon, mutumin Efraim. Akwai mutane 24,000 a sashensa.
11 The eighth, for the eighth month, was Sibbecai, a Hushathite from the stock of the Zerahites; and in his company there were twenty-four thousand.
Na takwas, don wata na takwas, shi ne Sibbekai mutumin Husha, mutumin Zera. Akwai mutane 24,000 a sashensa.
12 The ninth, for the ninth month, was Abiezer, an Anathothite from the sons of Benjamin; and in his company there were twenty-four thousand.
Na tara, don wata na tara, shi ne Abiyezer mutumin Anatot, mutumin Benyamin. Akwai mutane 24,000 a sashensa.
13 The tenth, for the tenth month, was Maharai, and he was a Netophathite from the stock of the Zerahites; and in his company there were twenty-four thousand.
Na goma, don wata na goma, shi ne Maharai mutumin Netofa, mutumin Zera. Akwai mutane 24,000 a sashensa.
14 The eleventh, for the eleventh month, was Benaiah, a Pirathonite from the sons of Ephraim; and in his company there were twenty-four thousand.
Na goma sha ɗaya, don wata goma sha ɗaya, shi ne Benahiya mutumin Firaton, mutumin Efraim. Akwai mutane 24,000 a sashensa.
15 The twelfth, for the twelfth month, was Heldai, a Netophathite from the stock of Othniel; and in his company there were twenty-four thousand.
Na goma sha biyu don wata goma sha biyu, shi ne Heldai mutumin Netofa, daga iyalin Otniyel. Akwai mutane 24,000 a sashensa.
16 Now those who were first over the tribes of Israel were these: over the Reubenites, Eliezer, the son of Zichri, was the ruler; over the Simeonites, Shephatiah, the son of Maacah, was the ruler;
Shugabannin da suke bisa kabilan Isra’ila, bisa mutanen Ruben su ne, Eliyezer ɗan Zikri; bisa mutanen Simeyon shi ne, Shefatiya ɗan Ma’aka
17 over the Levites, Hashabiah, the son of Kemuel; over the Aaronites, Zadok;
bisa mutanen Lawi shi ne, Hashabiya ɗan Kemuwel; bisa mutanen Haruna shi ne, Zadok;
18 over Judah, Elihu, the brother of David; over Issachar, Omri, the son of Michael;
bisa mutanen Yahuda shi ne, Elihu, ɗan’uwan Dawuda; bisa mutanen Issakar shi ne, Omri ɗan Mika’ilu;
19 over the Zebulunites, Ishmaiah, the son of Obadiah; over the Naphtalites, Jeremoth, the son of Azriel;
bisa mutanen Zebulun shi ne, Ishmahiya ɗan Obadiya; bisa mutanen Naftali shi ne, Yerimot ɗan Azriyel;
20 over the sons of Ephraim, Hoshea, the son of Azaziah; over the one half tribe of Manasseh, Joel, the son of Pedaiah;
bisa mutanen Efraim shi ne, Hosheya ɗan Azaziya; bisa rabin kabilar Manasse shi ne, Yowel ɗan Fedahiya;
21 and over the one half tribe of Manasseh in Gilead, Iddo, the son of Zechariah; then over Benjamin, Jaasiel, the son of Abner;
bisa ɗayan rabi kabilar Manasse a Gileyad shi ne, Iddo ɗan Zakariya; bisa mutanen Benyamin shi ne, Ya’asiyel ɗan Abner;
22 yet truly, Azarel, the son of Jeroham, was over Dan. These were the leaders of the sons of Israel.
bisa mutanen Dan shi ne, Azarel ɗan Yeroham. Waɗannan su ne shugabanni a bisa kabilan Isra’ila.
23 But David was not willing to number them from twenty years old and under. For the Lord had said that he would multiply Israel like the stars of heaven.
Dawuda bai ƙirga mutanen da suke’yan shekara ashirin ko ƙasa ba, domin Ubangiji ya yi alkawari zai sa Isra’ila su yi yawa kamar taurari a sararin sama.
24 Joab, the son of Zeruiah, had begun to number, but he did not finish. For because of this, wrath had fallen upon Israel. And therefore the number of those who had been counted was not related in the official records of king David.
Yowab ɗan Zeruhiya ya fara ƙirgan mutanen amma bai gama ba. Hasala ta sauko a kan Isra’ila saboda wannan ƙirge, ba a kuma shigar da adadin a littafin tarihin Sarki Dawuda ba.
25 Now over the storerooms of the king was Azmaveth, the son of Adiel. But Jonathan, the son of Uzziah, was over those storerooms that were in the cities, and in the villages, and in the towers.
Azmawet ɗan Adiyel shi ne mai lura da ɗakuna ajiyar fada. Yonatan ɗan Uzziya shi ne mai lura da ɗakunan ajiya a yankuna, cikin garuruwa, ƙauyuka da kuma hasumiyoyin tsaro.
26 And over the farmlands and the farmers, those who worked the ground, was Ezri, the son of Chelub.
Ezri ɗan Kelub shi ne mai lura da ma’aikatan gona waɗanda suke nome ƙasar.
27 And over the cultivators of vineyards was Shimei, a Ramathite; then over the wine cellars was Zabdi, an Aphonite.
Shimeyi mutumin Ramat shi ne mai lura da gonakin inabi. Zabdi mutumin Shifam shi ne mai lura da amfanin gonakin inabi don matsin ruwan inabi.
28 Now over the olive groves and the fig groves, which were in the plains, was Baal-hanan, a Gederite; and over the oil cellars was Joash.
Ba’al-Hanan mutumin Geder shi ne mai lura da itatuwan zaitun da na al’ul a gindin tuddan yamma. Yowash shi ne mai lura da tanadin man zaitun.
29 Now over the herds that were pastured in Sharon, Shitrai, a Sharonite, was in the first place; and over the oxen in the valleys, there was Shaphat, the son of Adlai.
Shitrai mutumin Sharon shi ne mai lura da garkuna masu kiwo a Sharon. Shafat ɗan Adlai shi ne mai lura da garkuna a kwari.
30 Truly, over the camels was Obil, an Ishmaelite; and over the donkeys was Jehdeiah, a Meronothite.
Obil mutumin Ishmayel shi ne mai lura da raƙuma. Yedehiya mutumin Meronot shi ne mai lura da jakuna.
31 And over the sheep was Jaziz, a Hagarene. All these were leaders over the substance of king David.
Yaziz mutumin Hagiri shi ne mai lura da tumaki. Dukan waɗannan shugabanni ne masu lura da mallakar Sarki Dawuda.
32 Now Jonathan, the uncle of David, was a counselor, a prudent and scholarly man; he and Jehiel, the son of Hachmoni, were with the sons of the king.
Yonatan, kawun Dawuda, shi ne mashawarci, mutum mai hangen nesa kuma marubuci. Yehiyel ɗan Hakmoni ne ya lura da’ya’yan sarki maza.
33 Now Ahithophel was the counselor of the king; and Hushai, the Archite, was the king’s friend.
Ahitofel shi ne mashawarcin sarki. Hushai mutumin Arkitawa shi ne abokin sarki na kud da kud.
34 After Ahithophel was Jehoiada, the son of Benaiah, and Abiathar. But the leader of the army of the king was Joab.
Yehohiyada ɗan Benahiya da Abiyatar ne suka gāji Ahitofel. Yowab shi ne shugaban mayaƙan masarauta.

< 1 Chronicles 27 >