< 1 Chronicles 22 >

1 And David said, “This is the house of God, and this is the altar for the holocaust of Israel.”
Sai Dawuda ya ce, “Gidan Ubangiji Allah zai kasance a nan, haka kuma bagaden hadaya ta ƙonawa don Isra’ila.”
2 And he instructed them to gather all the new converts from the land of Israel. And from these he appointed stoneworkers, to hew stones and to polish them, so that he might build the house of God.
Dawuda kuwa ya umarta a tattara baƙin da suke zama a Isra’ila, daga cikinsu ya sa masu farfasa duwatsu don su shirya duwatsun da aka sassaƙa saboda ginin gidan Allah.
3 Also, David prepared very much iron to use for the nails of the gates, and for the seams and joints, as well as an immeasurable weight of brass.
Ya tanada ƙarfe mai yawa don ƙusoshi saboda ƙyamaren hanyoyin shiga da kuma saboda mahaɗai, da ƙarin tagulla fiye da ƙirge.
4 Also, the cedar trees, which the Sidonians and Tyrians had transported to David, were not able to be counted.
Ya kuma tanada gumaguman al’ul masu yawa fiye da ƙirge, gama Sidoniyawa da mutanen Taya sun kawo su wa Dawuda da yawa.
5 And David said: “My son Solomon is a young and tender boy. But the house that I desire to be built to the Lord ought to be so great that it is renowned in every region. Therefore, I will prepare what will be necessary for him.” And for this reason, before his death, he prepared all the expenses.
Dawuda ya ce, “Ɗana Solomon matashi ne kuma bai gogu ba, kuma gidan da za a gina wa Ubangiji zai zama mai ƙayatarwa ƙwarai, sananne da kuma mai daraja a idon dukan al’ummai. Saboda haka zan yi shirye-shirye saboda shi.” Sai Dawuda ya yi ɗumbun shirye-shirye kafin mutuwarsa.
6 And he called for Solomon, his son. And he instructed him to build a house to the Lord, the God of Israel.
Sa’an nan ya kira ɗansa Solomon ya umarce shi yă gina gida domin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
7 And David said to Solomon: “My son, it was my will that I build a house to the name of the Lord my God.
Dawuda ya ce wa Solomon, “Ɗana, na yi niyya a zuciyata in gina gida saboda Sunan Ubangiji Allahna.
8 But the word of the Lord came to me, saying: ‘You have shed much blood, and you have battled in many wars. You are not able to build a house to my name, so great was the shedding of blood before me.
Amma wannan maganar Ubangiji ta zo mini, ‘Ka zub da jini mai yawa ka kuma yi yaƙe-yaƙe masu yawa. Ba za ka gina gida domin Sunana ba, domin ka zub da jini da yawa a duniya a idona.
9 The son who shall be born to you will be a very quiet man. For I will cause him to have rest from all his enemies on every side. And for this reason, he shall be called Peaceful. And I will grant peace and tranquility to Israel during all his days.
Amma za ka haifi ɗa wanda zai zama mutumin salama da kuma hutu, zan kuma ba shi hutu daga dukan abokan gābansa a kowane gefe. Za a kira shi Solomon, zai kuma kawo wa Isra’ila salama da natsuwa a zamanin mulkinsa.
10 He shall build a house to my name. And he shall be a son to me, and I will be a father to him. And I will establish the throne of his kingdom over Israel unto eternity.’
Shi ne wanda zai gina gida saboda Sunana. Zai zama ɗana, ni kuma zan zama mahaifinsa. Zan kafa kujerar sarautarsa a bisa Isra’ila har abada.’
11 Now then, my son, may the Lord be with you, and may you prosper and build a house to the Lord your God, just as he has spoken concerning you.
“Yanzu, ɗana, Ubangiji ya kasance tare da kai, bari kuma ka yi nasara ka kuma gina gidan Ubangiji Allahnka, kamar yadda ya ce za ka yi.
12 Also, may the Lord give you prudence and understanding, so that you may be able to rule Israel and to guard the law of the Lord your God.
Bari Ubangiji ya ba ka basira da fahimi sa’ad da ya sa ka shugaba a bisa Isra’ila, saboda ka kiyaye dokar Ubangiji Allahnka.
13 For then you will be able to advance, if you keep the commandments and judgments that the Lord instructed Moses to teach to Israel. Be strengthened and act manfully. You should not fear, and you should not dread.
Ta haka za ka yi nasara in ka mai da hankali ga kiyaye ƙa’idodi da dokokin da Ubangiji ya ba wa Musa saboda Isra’ila. Ka yi ƙarfin hali ka kuma ƙarfafa. Kada ka ji tsoro ko ka fid da zuciya.
14 Behold, in my poverty I have prepared the expenses for the house of the Lord: one hundred thousand talents of gold, and one million of talents of silver. Yet truly, there is no measuring the brass and the iron. For their magnitude is beyond numbering. And I have prepared the timber and the stones for the entire project.
“Na sha wahala da yawa don in yi tanadi talentin dubu ɗari na zinariya, talenti miliyon na azurfa, ɗumbun tagulla da ƙarfe da suka wuce ƙirge da katako da dutse saboda haikalin Ubangiji. Za ka iya ƙara su.
15 Also, you have very many artisans: stoneworkers, and builders of walls, and craftsmen of wood, and those most prudent in doing the work of every art,
Kana da ma’aikata masu yawa, masu fafarshe duwatsu, masu gini da masu aikin katako, da kuma gwanaye a kowane irin aikin
16 with gold and silver, and with brass and iron, of which there is no number. Therefore, rise up and act. And the Lord will be with you.”
zinariya da azurfa, tagulla da ƙarfe, masu sana’a waɗanda suka wuce ƙirge. Yanzu ka fara aiki, Ubangiji kuma ya kasance tare da kai.”
17 Also, David instructed all the leaders of Israel, so that they would assist his son Solomon,
Sai Dawuda ya umarta dukan shugabannin Isra’ila su taimake ɗansa Solomon.
18 saying: “You discern that the Lord your God is with you, and that he has given you rest on all sides, and that he has delivered all your enemies into your hands, and that the land has been subdued before the Lord and before his people.
Ya ce musu, “Ba Ubangiji Allahnku yana tare da ku ba? Bai kuma ba ku hutu a kowane gefe ba? Gama ya ba da mazaunan ƙasar gare ni, ƙasar kuma ta Ubangiji ce da mutanensa.
19 Therefore, offer your hearts and your souls, so that you seek the Lord your God. And rise up and build a sanctuary to the Lord God, so that the ark of the covenant of the Lord, and the vessels consecrated to the Lord, may be brought into the house that is built to the name of the Lord.”
Yanzu fa sai ku sa zuciyarku da ranku ga neman Ubangiji Allahnku. Ku fara ginin wuri mai tsarki na Ubangiji Allah, don ku kawo akwatin alkawarin Ubangiji da kayayyaki masu tsarki na Allah a cikin haikalin da za a gina saboda Sunan Ubangiji.”

< 1 Chronicles 22 >