< 1 Chronicles 21 >

1 Now Satan rose up against Israel, and he incited David so that he would number Israel.
Sai Shaiɗan ya tashi gāba da Isra’ila, ya zuga Dawuda ya ƙidaya Isra’ila.
2 And David said to Joab and to the leaders of the people: “Go, and number Israel, from Beersheba even to Dan. And bring me the number, so that I may know it.”
Saboda haka Dawuda ya ce wa Yowab da shugabannin mayaƙa, “Ku tafi ku ƙidaya Isra’ilawa daga Beyersheba zuwa Dan. Ku kawo mini labarin saboda in san su nawa ne.”
3 And Joab responded: “May the Lord increase his people a hundred times more than they are. But, my lord the king, are they not all your servants? Why would my lord seek this thing, which may be imputed as a sin to Israel?”
Amma Yowab ya amsa ya ce, “Ubangiji ya riɓaɓɓanya mayaƙansa fiye da sau ɗari. Ranka yă daɗe sarki, dukansu ba bayin shugabana ba ne? Me ya sa ranka yă daɗe yake so yă yi haka? Me zai sa ka kawo laifi a kan Isra’ila?”
4 But the word of the king prevailed instead. And Joab went away, and he traveled around, through all of Israel. And he returned to Jerusalem.
Amma sarki ya nace a kan maganar da ya yi wa Yowab. Sai Yowab ya tashi ya tafi cikin dukan Isra’ila, ya kewaye sa’an nan ya dawo Urushalima.
5 And he gave to David the number of those whom he had surveyed. And the entire number of Israel was found to be one million and one hundred thousand men who could draw the sword; but from Judah, there were four hundred and seventy thousand men of war.
Yowab ya ba labarin yawan mayaƙan wa Dawuda. A cikin Isra’ila akwai mutum miliyon da dubu ɗari ɗaya waɗanda za su iya riƙe takobi, haɗe da dubu ɗari huɗu da saba’in a Yahuda.
6 But Levi and Benjamin he did not number. For Joab executed the orders of the king unwillingly.
Amma Yowab bai haɗa da mutanen Lawi da na Benyamin a ƙidayar ba, domin bai ji daɗin umarnin sarki ba.
7 Then God was displeased with what had been ordered, and so he struck Israel.
Wannan umarnin mugu ne a gaban Allah; saboda haka ya hukunta Isra’ila.
8 And David said to God: “I have sinned exceedingly in doing this. I beg you take away the iniquity of your servant. For I have acted unwisely.”
Sai Dawuda ya ce wa Allah, “Na yi zunubi ƙwarai ta wurin yin wannan. Yanzu, na roƙe ka, ka ɗauke laifin bawanka. Na yi wauta sosai.”
9 And the Lord spoke to Gad, the seer of David, saying:
Sai Ubangiji ya ce wa Gad, mai duba na Dawuda,
10 “Go, and speak to David, and tell him: Thus says the Lord: I give to you the option of three things. Choose the one that you will want, and I will do it to you.”
“Tafi ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina ba ka abubuwa uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata a kanka.’”
11 And when Gad had gone to David, he said to him: “Thus says the Lord: Choose what you will want:
Saboda haka Gad ya tafi wurin Dawuda ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka yi zaɓi,
12 Either three years of famine, or three months for you to flee from your enemies, unable to escape from their sword, or three days for the sword of the Lord and a pestilence to turn within the land, with the Angel of the Lord killing in every part of Israel. Now therefore, see what I should respond to him who sent me.”
shekara uku na yunwa, wata uku na shan ɗibga a gaban abokan gābanka, sa’ad da za su bi suna kakkashe ku, ko kuwa kwana uku na takobin Ubangiji, ranakun annoba a cikin ƙasar, mala’ikan Ubangiji zai hallaka kowane sashe na Isra’ila.’ Yanzu sai ka yanke shawara yadda zan amsa wa wanda ya aiko ni.”
13 And David said to Gad: “There are difficulties pressing upon me from every side. But it is better for me to fall into the hands of the Lord, for his mercies are many, than into the hands of men.”
Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Bari in fāɗa a hannuwan Ubangiji, gama jinƙansa yana da girma sosai; amma kada ka bari in fāɗa a hannuwan mutane.”
14 Therefore, the Lord sent a pestilence upon Israel. And there fell from Israel seventy thousand men.
Sai Ubangiji ya aiko da annoba a kan Isra’ila, mutane duba saba’in na Isra’ila suka mutu.
15 Also, he sent an Angel to Jerusalem, so that he might strike it. And while he was striking, the Lord saw and took pity over the magnitude of the harm. And he commanded the Angel who was striking: “It is enough. Now let your hand cease.” And the Angel of the Lord was standing beside the threshing floor of Ornan the Jebusite.
Allah kuwa ya aiki mala’ika yă hallaka Urushalima. Amma yayinda mala’ikan yana gab da yin haka, sai Ubangiji ya gani ya kuma yi nadama saboda masifar, sai ya ce wa mala’ikan wanda yake hallaka mutane, “Ya isa! Janye hannunka.” Mala’ikan Ubangiji kuwa yana tsaye a masussukar Ornan mutumin Yebus.
16 And David, lifting up his eyes, saw the Angel of the Lord, standing between heaven and earth with a drawn sword in his hand, turned toward Jerusalem. And both he and those greater by birth, being clothed in haircloth, fell prone upon the ground.
Sai Dawuda ya ɗaga ido ya ga mala’ikan Ubangiji tsaye tsakanin sama da duniya, da takobi a zāre a hannunsa ya miƙa a kan Urushalima. Sai Dawuda da dattawa, saye da rigunan makoki suka fāɗi rubda jiki.
17 And David said to God: “Am I not the one who ordered that the people be numbered? It is I who sinned; it is I who did evil. This flock, what does it deserve? O Lord my God, I beg you to let your hand be turned against me and against the house of my father. But let not your people be struck down.”
Dawuda ya ce wa Allah, “Ba ni ba ne na umarta a ƙidaya mayaƙan? Ni ne wanda ya yi zunubin da kuma abin da ba daidai ba. Waɗannan dai tumaki ne. Me suka yi? Ya Ubangiji Allahna, bari hannunka ya fāɗi a kaina da kuma iyalina, amma kada ka bar wannan annoba ya kasance a kan mutanenka.”
18 Then the Angel of the Lord instructed Gad to tell David that he should ascend and build an altar to the Lord God on the threshing floor of Ornan the Jebusite.
Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya umarci Gad yă faɗa wa Dawuda yă haura yă gina bagade wa Ubangiji a masussukar Ornan mutumin Yebus.
19 Therefore, David ascended, in accord with the word of Gad, which he had spoken to him in the name of the Lord.
Saboda haka Dawuda ya haura cikin biyayya ga maganar da Allah ya yi da sunan Ubangiji.
20 Now when Ornan had looked up and seen the Angel, he and his four sons hid themselves. For at that time, he was threshing wheat upon the floor.
Yayinda Ornan yake sussukar alkama, sai ya juya ya ga mala’ika;’ya’yansa maza guda huɗu da suke tare da shi suka ɓuya.
21 Then, as David was approaching Ornan, Ornan saw him, and he went out from the threshing floor to meet him. And he reverenced him prone on the ground.
Sai Dawuda ya kusato, sa’ad da Ornan ya duba sai ya gan shi, ya bar masussukar ya rusuna a gaban Dawuda da fuskarsa har ƙasa.
22 And David said to him: “Give this place of your threshing floor to me, so that I may build an altar to the Lord upon it. And you shall accept from me as much money as it is worth, so that the plague may cease from the people.”
Dawuda ya ce wa Ornan, “Ka ba ni masussukarka saboda in gina bagade wa Ubangiji, don annobar da take kan mutane tă daina. Ka sayar mini ita a cikakken kuɗinta.”
23 But Ornan said to David: “Take it, and may my lord the king do whatever pleases him. Moreover, I give the oxen also as a holocaust, and the plow for wood, and the wheat for a sacrifice. I will offer all freely.”
Ornan ya ce wa Dawuda, “Ka karɓa! Bari ranka yă daɗe, sarki yă yi duk abin da ya ga ya yi masa kyau. Duba, zan ba da shanu domin hadaya ta ƙonawa, da itacen sussuka, da kuma alkama domin hadaya ta gari. Zan ba da dukan wannan.”
24 And king David said to him: “By no means shall it be so. Instead, I will give money to you, as much as it is worth. For I must not take it from you, and thereby offer to the Lord holocausts that cost nothing.”
Amma Sarki Dawuda ya amsa wa Ornan ya ce, “A’a, na nace zan biya cikakken kuɗinta. Ba zan karɓi abinka kawai don Ubangiji ba, ko in miƙa hadaya ta ƙonawar da ba tă ci mini wani abu ba.”
25 Therefore, David gave Ornan, for the place, the very just weight of six hundred shekels of gold.
Saboda haka Dawuda ya biya Ornan shekel ɗari shida na zinariya saboda wurin.
26 And he built an altar to the Lord there. And he offered holocausts and peace offerings, and he called upon the Lord. And he heeded him by sending fire from heaven upon the altar of the holocaust.
Dawuda ya gina bagade wa Ubangiji a can ya kuma miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, Ubangiji kuwa ya amsa masa ta wurin wuta daga sama a kan bagaden hadaya ta ƙonawa.
27 And the Lord instructed the Angel, and he turned his sword back into its sheath.
Sa’an nan Ubangiji ya yi magana ga mala’ikan, ya kuma mayar da takobinsa a kube.
28 Then, seeing that the Lord had heeded him at the threshing floor of Ornan the Jebusite, David immediately immolated victims there.
A lokacin, sa’ad da Dawuda ya ga cewa Ubangiji ya amsa masa a masussukar Ornan mutumin Yebus, sai ya miƙa hadayu a can.
29 But the tabernacle of the Lord, which Moses had made in the desert, and the altar of holocausts, were at that time on the high place of Gibeon.
Tabanakul na Ubangiji da Musa ya yi a hamada, da kuma bagaden hadaya ta ƙonawa a lokacin suna a tudun Gibeyon.
30 And David was unable to go to the altar, so that he might pray to God there. For he had been struck with an exceedingly great fear, seeing the sword of the Angel of the Lord.
Amma Dawuda bai iya zuwa gabansa don yă yi tambaya ga Allah ba, gama yana jin tsoron takobin mala’ikan Ubangiji.

< 1 Chronicles 21 >