< Matthew 22 >

1 Jesus answered and spoke to them again in parables, saying,
Yesu ya sāke yin musu magana da misalai, yana cewa,
2 “The Kingdom of Heaven is like a certain king, who made a wedding feast for his son,
“Mulkin sama yana kama da wani sarki wanda ya shirya bikin auren ɗansa.
3 and sent out his servants to call those who were invited to the wedding feast, but they would not come.
Sai ya aiki bayinsa su kira waɗanda aka gayyata zuwa bikin, amma waɗanda aka ce su zo bikin, suka ƙi zuwa.
4 Again he sent out other servants, saying, ‘Tell those who are invited, “Behold, I have prepared my dinner. My cattle and my fatlings are killed, and all things are ready. Come to the wedding feast!”’
“Sai ya sāke aiken waɗansu bayi ya ce, ‘Ku ce wa waɗanda aka gayyata cewa na shirya abinci. An yanka bijimai da shanun da aka yi kiwo, kome a shirye yake. Ku zo bikin auren mana.’
5 But they made light of it, and went their ways, one to his own farm, another to his merchandise;
“Amma ba su kula ba, suka kama gabansu, ɗaya ya tafi gonarsa, ɗaya kuma ya tafi kasuwancinsa.
6 and the rest grabbed his servants, treated them shamefully, and killed them.
Sauran suka kama bayinsa suka wulaƙanta su, suka kuma kashe su.
7 When the king heard that, he was angry, and sent his armies, destroyed those murderers, and burned their city.
Sai sarkin ya yi fushi. Ya aiki mayaƙansa suka karkashe masu kisankan nan, aka kuma ƙone birninsu.
8 “Then he said to his servants, ‘The wedding is ready, but those who were invited were not worthy.
“Sa’an nan ya ce wa bayinsa, ‘Bikin aure fa ya shiryu, sai dai mutanen da na gayyata ba su dace ba.
9 Go therefore to the intersections of the highways, and as many as you may find, invite to the wedding feast.’
Ku bi titi-titi ku gayyato duk waɗanda kuka gani, su zo bikin.’
10 Those servants went out into the highways and gathered together as many as they found, both bad and good. The wedding was filled with guests.
Saboda haka bayin suka bi titi-titi, suka tattaro duk mutanen da suka samu, masu kirki da marasa kirki, zauren bikin ya cika makil da baƙi.
11 “But when the king came in to see the guests, he saw there a man who did not have on wedding clothing,
“Amma da sarkin ya shigo don yă ga baƙin, sai ya ga wani can da ba ya sanye da kayan auren.
12 and he said to him, ‘Friend, how did you come in here not wearing wedding clothing?’ He was speechless.
Ya yi tambaya ya ce, ‘Aboki, yaya ka shigo nan ba tare da rigar aure ba?’ Mutumin ya rasa ta cewa.
13 Then the king said to the servants, ‘Bind him hand and foot, take him away, and throw him into the outer darkness. That is where the weeping and grinding of teeth will be.’
“Sai sarkin ya ce wa fadawa, ‘Ku daure shi hannu da ƙafa, ku jefar da shi waje, cikin duhu, inda za a yi kuka da cizon haƙora.’
14 For many are called, but few chosen.”
“Gama kirayayu da yawa, amma zaɓaɓɓu kaɗan ne zaɓaɓɓu.”
15 Then the Pharisees went and took counsel how they might entrap him in his talk.
Sai Farisiyawa suka yi waje, suka ƙulla yadda za su yi masa tarko cikin maganarsa.
16 They sent their disciples to him, along with the Herodians, saying, “Teacher, we know that you are honest, and teach the way of God in truth, no matter whom you teach; for you are not partial to anyone.
Suka aiki almajiransu tare da mutanen Hiridus wurinsa. Suka ce, “Malam, mun san kai mutum ne mai mutunci, kuma kana koyar da maganar Allah bisa gaskiya. Mutane ba sa ɗaukan hankalinka, domin ba ka kula ko su wane ne ba.
17 Tell us therefore, what do you think? Is it lawful to pay taxes to Caesar, or not?”
To, ka gaya mana, a ra’ayinka? Ya dace a biya Kaisar haraji ko a’a?”
18 But Jesus perceived their wickedness, and said, “Why do you test me, you hypocrites?
Amma Yesu da yake ya san mugun nufinsu, sai ya ce, “Ku munafukai, don me kuke ƙoƙarin sa mini tarko?
19 Show me the tax money.” They brought to him a denarius.
Ku nuna mini kuɗin da ake biyan haraji da shi.” Sai suka kawo masa dinari,
20 He asked them, “Whose is this image and inscription?”
sai ya tambaye su ya ce, “Hoton wane ne wannan? Kuma rubutun wane ne?”
21 They said to him, “Caesar’s.” Then he said to them, “Give therefore to Caesar the things that are Caesar’s, and to God the things that are God’s.”
Suka amsa, “Na Kaisar ne.” Sai ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba wa Allah abin da yake na Allah.”
22 When they heard it, they marveled, and left him and went away.
Da suka ji haka, sai suka yi mamaki. Saboda haka suka ƙyale shi, suka yi tafiyarsu.
23 On that day Sadducees (those who say that there is no resurrection) came to him. They asked him,
A ranan nan Sadukiyawa, waɗanda suke cewa babu tashin matattu, suka zo wurinsa da tambaya.
24 saying, “Teacher, Moses said, ‘If a man dies, having no children, his brother shall marry his wife and raise up offspring for his brother.’
Suka ce “Malam, Musa ya faɗa mana cewa in mutum ya mutu ba shi da’ya’ya, dole ɗan’uwansa yă auri gwauruwar yă kuma haifar wa ɗan’uwan’ya’ya.
25 Now there were with us seven brothers. The first married and died, and having no offspring left his wife to his brother.
A cikinmu an yi’yan’uwa guda bakwai. Na fari ya yi aure, ya mutu, da yake bai sami’ya’ya ba, sai ya bar matarsa wa ɗan’uwansa.
26 In the same way, the second also, and the third, to the seventh.
Haka ya faru da ɗan’uwa na biyu da na uku, har zuwa na bakwai.
27 After them all, the woman died.
A ƙarshe, macen ta mutu.
28 In the resurrection therefore, whose wife will she be of the seven? For they all had her.”
To, a tashin matattu, matar wa a cikinsu bakwai ɗin nan za tă zama, da yake dukansu sun aure ta?”
29 But Jesus answered them, “You are mistaken, not knowing the Scriptures, nor the power of God.
Yesu ya amsa ya ce, “Kun ɓata, domin ba ku san Nassi ko ikon Allah ba.
30 For in the resurrection they neither marry nor are given in marriage, but are like God’s angels in heaven.
Ai, a tashin matattu, mutane ba za su yi aure ko su ba da aure ba; za su zama kamar mala’iku a sama.
31 But concerning the resurrection of the dead, have not you read that which was spoken to you by God, saying,
Amma game da tashi daga matattu na waɗanda suka mutu ba ku karanta abin da Allah ya ce muku ba ne,
32 ‘I am the God of Abraham, and the God of Isaac, and the God of Jacob’? God is not the God of the dead, but of the living.”
‘Ni ne Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub’? Ai, shi ba Allah na matattu ba ne, shi Allah na masu rai ne.”
33 When the multitudes heard it, they were astonished at his teaching.
Da taro suka ji haka, sai suka yi mamakin koyarwarsa.
34 But the Pharisees, when they heard that he had silenced the Sadducees, gathered themselves together.
Da jin Yesu ya ƙure Sadukiyawa, sai Farisiyawa suka tattaru.
35 One of them, a lawyer, asked him a question, testing him.
Ɗaya daga cikinsu, wani masanin Doka, ya gwada shi da wannan tambaya.
36 “Teacher, which is the greatest commandment in the law?”
“Malam, wace doka ce mafi girma a cikin dokoki?”
37 Jesus said to him, “‘You shall love the Lord your God with all your heart, with all your soul, and with all your mind.’
Yesu ya amsa ya ce, “‘Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka da dukan ranka da kuma dukan hankalinka.’
38 This is the first and great commandment.
Wannan, ita ce doka ta fari da kuma mafi girma.
39 A second likewise is this, ‘You shall love your neighbor as yourself.’
Ta biye kuma kamar ta farkon take. ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’
40 The whole law and the prophets depend on these two commandments.”
Dukan Doka da Annabawa suna rataya ne a kan waɗannan dokoki biyu.”
41 Now while the Pharisees were gathered together, Jesus asked them a question,
Yayinda Farisiyawa suke a tattare wuri ɗaya, sai Yesu ya tambaye su,
42 saying, “What do you think of the Christ? Whose son is he?” They said to him, “Of David.”
“Me kuke tsammani game da Kiristi? Ɗan wane ne shi?” Suka amsa suka ce, “Ɗan Dawuda.”
43 He said to them, “How then does David in the Spirit call him Lord, saying,
Ya ce musu, “To, ta yaya Dawuda ya yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki, ya kira shi ‘Ubangiji’? Gama ya ce,
44 ‘The Lord said to my Lord, sit on my right hand, until I make your enemies a footstool for your feet’?
“‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”’
45 “If then David calls him Lord, how is he his son?”
To, in Dawuda ya kira shi ‘Ubangiji,’ yaya zai zama ɗansa?”
46 No one was able to answer him a word, neither did any man dare ask him any more questions from that day forward.
Ba wanda ya iya tanka masa, daga wannan rana kuwa ba wanda ya sāke yin karambanin yin masa wata tambaya.

< Matthew 22 >