< Matthew 21 >

1 When they came near to Jerusalem and came to Bethsphage, to the Mount of Olives, then Jesus sent two disciples,
Da suka yi kusa da Urushalima suka kuma kai Betfaji da yake kan Dutsen Zaitun, sai Yesu ya aiki almajirai biyu,
2 saying to them, “Go into the village that is opposite you, and immediately you will find a donkey tied, and a colt with her. Untie them and bring them to me.
yana ce musu, “Ku je ƙauyen da yake gabanku, nan take za ku ga wata jaka a daure tare da ɗanta kusa da ita, a can. Ku kunce su ku kawo mini.
3 If anyone says anything to you, you shall say, ‘The Lord needs them,’ and immediately he will send them.”
In wani ya yi muku wata magana, ku ce masa Ubangiji yana bukatarsu, zai kuwa mai da su nan da nan.”
4 All this was done that it might be fulfilled which was spoken through the prophet, saying,
Wannan ya faru ne don a cika abin da aka faɗa ta bakin annabin cewa,
5 “Tell the daughter of Zion, behold, your King comes to you, humble, and riding on a donkey, on a colt, the foal of a donkey.”
“Ku ce wa Diyar Sihiyona, ‘Duba, sarkinki yana zuwa gare ki, mai tawali’u yana a kan jaki, a kan aholaki, ɗan jaki.’”
6 The disciples went and did just as Jesus commanded them,
Almajiran suka tafi suka yi kamar yadda Yesu ya umarce su.
7 and brought the donkey and the colt and laid their clothes on them; and he sat on them.
Suka kawo jakar da ɗanta, suka shimfiɗa mayafansu a kansu, Yesu kuma ya zauna a kansu.
8 A very great multitude spread their clothes on the road. Others cut branches from the trees and spread them on the road.
Wani babban taron mutane suka shimfiɗa mayafansu a kan hanya, yayinda waɗansu suka sassari rassan itatuwa suka shisshimfiɗa a kan hanya.
9 The multitudes who went in front of him, and those who followed, kept shouting, “Hosanna to the son of David! Blessed is he who comes in the name of the Lord! Hosanna in the highest!”
Taron mutanen da suke gabansa da kuma waɗanda suke binsa a baya suka yi ihu suna cewa, “Hosanna ga Ɗan Dawuda!” “Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Hosanna a cikin sama!”
10 When he had come into Jerusalem, all the city was stirred up, saying, “Who is this?”
Sa’ad da Yesu ya shiga Urushalima, dukan birnin ya ruɗe, ana ta tambaya, “Wane ne wannan?”
11 The multitudes said, “This is the prophet, Jesus, from Nazareth of Galilee.”
Taron mutane suka amsa, “Wannan shi ne Yesu, annabin nan daga Nazaret a Galili.”
12 Jesus entered into the temple of God and drove out all of those who sold and bought in the temple, and overthrew the money changers’ tables and the seats of those who sold the doves.
Yesu ya shiga filin haikali, ya kuma kori duk masu saya da sayarwa a can. Ya tutture tebur masu canjin kuɗi da kuma kujerun masu sayar da tattabarai.
13 He said to them, “It is written, ‘My house shall be called a house of prayer,’ but you have made it a den of robbers!”
Ya ce musu, “A rubuce yake, ‘Za a ce da gidana, gidan addu’a,’amma kuna mai da shi ‘kogon’yan fashi.’”
14 The lame and the blind came to him in the temple, and he healed them.
Makafi da guragu suka zo wurinsa a haikali, ya kuwa warkar da su.
15 But when the chief priests and the scribes saw the wonderful things that he did, and the children who were crying in the temple and saying, “Hosanna to the son of David!” they were indignant,
Amma da manyan firistoci da malaman dokoki suka ga abubuwan banmamakin da ya yi, yara kuma suna ihu a filin haikali suna cewa, “Hosanna ga Ɗan Dawuda,” sai fushi ya kama su.
16 and said to him, “Do you hear what these are saying?” Jesus said to them, “Yes. Did you never read, ‘Out of the mouth of children and nursing babies, you have perfected praise’?”
Suka tambaye shi suka ce, “Kana jin abin da waɗannan suke faɗa?” Yesu ya amsa ya ce, “I, ba ku taɓa karanta ba cewa, “‘Daga leɓunan yara da jarirai kai, Ubangiji, ka shirya wa kanka yabo’?”
17 He left them and went out of the city to Bethany, and camped there.
Sai ya bar su, ya fita daga birnin ya tafi Betani, inda ya kwana.
18 Now in the morning, as he returned to the city, he was hungry.
Kashegari da sassafe, yayinda yake kan hanyarsa ta komawa cikin birni, sai ya ji yunwa.
19 Seeing a fig tree by the road, he came to it and found nothing on it but leaves. He said to it, "Let there be no fruit from you for the age (aiōn g165)!" Immediately the fig tree withered away.
Ganin itacen ɓaure kusa da hanya, sai ya je wajensa amma bai sami kome a kansa ba sai ganye. Sai ya ce masa, “Kada ka ƙara yin’ya’ya!” Nan da nan itacen ya yanƙwane. (aiōn g165)
20 When the disciples saw it, they marveled, saying, “How did the fig tree immediately wither away?”
Sa’ad da almajiran suka ga haka, sai suka yi mamaki suna tambaya, “Yaya itacen ɓauren ya yanƙwane nan da nan haka?”
21 Jesus answered them, “Most certainly I tell you, if you have faith and do not doubt, you will not only do what was done to the fig tree, but even if you told this mountain, ‘Be taken up and cast into the sea,’ it would be done.
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, in kuna da bangaskiya, ba kuwa da wata shakka ba, ba kawai za ku iya yin abin da aka yi wa itacen ɓauren nan ba, amma za ku ma iya ce wa dutsen nan, ‘Je ka, ka jefa kanka cikin teku,’ sai yă faru.
22 All things, whatever you ask in prayer, believing, you will receive.”
In kun gaskata, za ku karɓi duk abin da kuka roƙa a cikin addu’a.”
23 When he had come into the temple, the chief priests and the elders of the people came to him as he was teaching, and said, “By what authority do you do these things? Who gave you this authority?”
Sai Yesu ya shiga filin haikali, yayinda yake koyarwa, sai manyan firistoci da dattawan mutane suka zo wurinsa suka yi tambaya, “Da wane iko kake yin waɗannan abubuwa? Kuma wa ya ba ka wannan iko?”
24 Jesus answered them, “I also will ask you one question, which if you tell me, I likewise will tell you by what authority I do these things.
Yesu ya amsa ya ce, “Ni ma zan yi muku tambaya guda. In kuka ba ni amsa, ni ma zan gaya muku ko da wane iko nake yin waɗannan abubuwa.
25 The baptism of John, where was it from? From heaven or from men?” They reasoned with themselves, saying, “If we say, ‘From heaven,’ he will ask us, ‘Why then did you not believe him?’
Baftismar Yohanna, daga ina ta fito? Daga sama ce, ko daga mutane?” Sai suka tattauna a junansu suka ce, “In muka ce, ‘Daga sama,’ zai ce, ‘To, me ya sa ba mu gaskata shi ba?’
26 But if we say, ‘From men,’ we fear the multitude, for all hold John as a prophet.”
In kuma muka ce, ‘Daga mutane,’ muna tsoron mutane, gama duk sun ɗauka Yohanna annabi ne.”
27 They answered Jesus, and said, “We do not know.” He also said to them, “Neither will I tell you by what authority I do these things.
Saboda haka suka amsa wa Yesu suka ce, “Ba mu sani ba.” Sai ya ce, “Ni ma ba zan gaya muku ko da wane iko nake yin waɗannan abubuwa ba.”
28 But what do you think? A man had two sons, and he came to the first, and said, ‘Son, go work today in my vineyard.’
“Me kuka gani? An yi wani mutum wanda yake da’ya’ya biyu maza. Sai ya je wajen ɗan farin ya ce, ‘Ɗana, yau tafi gonar inabi ka yi aiki.’
29 He answered, ‘I will not,’ but afterward he changed his mind, and went.
“Ya amsa ya ce, ‘Ba zan tafi ba,’ amma daga baya ya sāke tunani, ya tafi.
30 He came to the second, and said the same thing. He answered, ‘I am going, sir,’ but he did not go.
“Sai mahaifin ya tafi waje na biyun ya faɗa masa iri magana guda. Sai ya amsa ya ce, ‘Zan tafi, ranka yă daɗe,’ amma bai tafi ba.
31 Which of the two did the will of his father?” They said to him, “The first.” Jesus said to them, “Most certainly I tell you that the tax collectors and the prostitutes are entering into God’s Kingdom before you.
“Wanne cikin yaran nan biyu ya yi abin da mahaifinsa yake so?” Suka amsa, “Na farin.” Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, masu karɓar haraji da karuwai suna riga ku shiga mulkin Allah.
32 For John came to you in the way of righteousness, and you did not believe him; but the tax collectors and the prostitutes believed him. When you saw it, you did not even repent afterward, that you might believe him.
Gama Yohanna Mai Baftisma ya zo wurinku don yă nuna muku hanyar adalci, ba ku gaskata shi ba, amma masu karɓar haraji da karuwai sun gaskata. Har ma bayan kun ga wannan, ba ku tuba kun gaskata shi ba.”
33 “Hear another parable. There was a man who was a master of a household who planted a vineyard, set a hedge about it, dug a wine press in it, built a tower, leased it out to farmers, and went into another country.
“Ku saurari wani misali. An yi wani mai gona wanda ya yi gonar inabi. Ya kewaye ta da katanga, ya haƙa wurin matsin inabi a ciki, ya kuma gina hasumiyar gadi. Sa’an nan ya ba wa waɗansu manoma hayar gonar inabin, ya kuma yi tafiya.
34 When the season for the fruit came near, he sent his servants to the farmers to receive his fruit.
Da lokacin girbi ya yi kusa, sai ya aiki bayinsa wajen’yan hayan, su karɓo masa’ya’yan inabi.
35 The farmers took his servants, beat one, killed another, and stoned another.
“Amma’yan hayan suka kama bayinsa; suka dūke ɗaya, suka kashe ɗaya, suka kuma jajjefi na ukun.
36 Again, he sent other servants more than the first; and they treated them the same way.
Sai ya sāke aiken waɗansu bayi wurinsu, fiye da na dā yawa, amma’yan hayan suka yi musu kamar yadda suka yi wa na farin.
37 But afterward he sent to them his son, saying, ‘They will respect my son.’
A ƙarshe, sai ya aiki ɗansa a wurinsu. Ya ce, ‘Za su girmama ɗana.’
38 But the farmers, when they saw the son, said among themselves, ‘This is the heir. Come, let’s kill him and seize his inheritance.’
“Amma da’yan hayan suka hangi ɗan, sai suka ce wa juna, ‘Wannan shi ne magājin. Ku zo, mu kashe shi, mu ci gādonsa.’
39 So they took him and threw him out of the vineyard, then killed him.
Saboda haka suka kama shi, suka jefar da shi bayan katangar gonar inabin, suka kashe shi.
40 When therefore the lord of the vineyard comes, what will he do to those farmers?”
“To, idan mai gonar inabin ya zo, me zai yi da’yan hayan nan?”
41 They told him, “He will miserably destroy those miserable men, and will lease out the vineyard to other farmers who will give him the fruit in its season.”
Suka amsa suka ce, “Zai yi wa banzan mutanen nan mugun kisa, yă ba da hayar gonar inabin ga waɗansu’yan haya, waɗanda za su ba shi rabonsa na amfanin gona a lokacin girbi.”
42 Jesus said to them, “Did you never read in the Scriptures, ‘The stone which the builders rejected was made the head of the corner. This was from the Lord. It is marvelous in our eyes’?
Yesu ya ce musu, “Ashe, ba ku taɓa karanta a cikin Nassi cewa, “‘Dutsen da magina suka ƙi shi ne ya zama dutsen kusurwar gini. Ubangiji ne ya aikata wannan, kuma abin mamaki ne a idanunmu’?
43 “Therefore I tell you, God’s Kingdom will be taken away from you and will be given to a nation producing its fruit.
“Saboda haka, ina gaya muku cewa za a karɓe mulkin Allah daga gare ku, a ba wa mutanen da za su ba da amfani.
44 He who falls on this stone will be broken to pieces, but on whomever it will fall, it will scatter him as dust.”
Duk wanda ya fāɗi a kan dutsen nan, zai kakkarye. Amma duk wanda dutsen nan ya fāɗi a kansa, za a murƙushe shi.”
45 When the chief priests and the Pharisees heard his parables, they perceived that he spoke about them.
Da manyan firistoci da Farisiyawa suka ji misalan Yesu, sai suka gane cewa da su yake.
46 When they sought to seize him, they feared the multitudes, because they considered him to be a prophet.
Suka nemi hanyar kama shi, amma suka ji tsoron taron, don mutane sun ɗauka shi annabi ne.

< Matthew 21 >