< 1 John 5 >

1 Whoever believes that Jesus is the Christ has been born of God. Whoever loves the Father also loves the child who is born of him.
Kowa ya gaskata cewa Yesu shi ne Kiristi, shi haifaffe na Allah ne, kuma duk mai ƙaunar mahaifi kuwa, yakan ƙaunaci ɗansa ma.
2 By this we know that we love the children of God, when we love God and keep his commandments.
Ga yadda muka san cewa muna ƙaunar’ya’yan Allah. Muna yin haka ta wurin ƙaunar Allah da kuma aikata umarnansa.
3 For this is loving God, that we keep his commandments. His commandments are not grievous.
Ƙaunar Allah ita ce, a yi biyayya da umarnansa. Umarnansa kuwa ba masu nauyi ba ne;
4 For whatever is born of God overcomes the world. This is the victory that has overcome the world: your faith.
domin duk haifaffe na Allah yana cin nasara a kan duniya. Bangaskiyarmu kuwa ita ce ta ba mu wannan nasara a kan duniya.
5 Who is he who overcomes the world, but he who believes that Jesus is the Son of God?
Wa ya cin nasara a kan duniya? Sai wanda ya gaskata cewa Yesu Ɗan Allah ne.
6 This is he who came by water and blood, Jesus Christ; not with the water only, but with the water and the blood. It is the Spirit who testifies, because the Spirit is the truth.
Ga wanda ya zo ta wurin ruwa da jini, wato, Yesu Kiristi. Bai zo ta wurin ruwa kaɗai ba, sai dai ta wurin ruwa da kuma jini. Ruhu ne kuwa yake ba da shaida, gama Ruhu shi ne gaskiya.
7 For there are three who testify:
Akwai shaidu uku, wato,
8 the Spirit, the water, and the blood; and the three agree as one.
Ruhu, da ruwa, da kuma jini; waɗannan uku kuwa manufarsu ɗaya ce.
9 If we receive the witness of men, the witness of God is greater; for this is God’s testimony which he has testified concerning his Son.
Tun da yake mukan yarda da shaida mutane, ai, shaidar Allah ta fi ƙarfi. Wannan ita ce shaidar Allah, wato, ya shaidi Ɗansa.
10 He who believes in the Son of God has the testimony in himself. He who does not believe God has made him a liar, because he has not believed in the testimony that God has given concerning his Son.
Duk wanda ya gaskata da Ɗan Allah, yana da shaidan nan a zuciyarsa. Duk wanda bai gaskata da Allah ba kuwa ya mai da shi maƙaryaci, domin bai gaskata shaidar da Allah ya bayar game da Ɗansa ba.
11 The testimony is this, that God gave to us consummate (aiōnios g166) life, and this life is in his Son.
Wannan kuwa ita ce shaidar; cewa Allah ya ba mu rai madawwami, wannan rai kuwa yana cikin Ɗansa. (aiōnios g166)
12 He who has the Son has the life. He who does not have God’s Son does not have the life.
Duk wanda yake da Ɗan, yana da rai; wanda kuwa ba shi da Ɗan Allah, ba shi da rai.
13 These things I have written to you who believe in the name of the Son of God, that you may know that you have consummate (aiōnios g166) life.
Ina rubuta waɗannan abubuwa gare ku, ku da kuka gaskata sunan Ɗan Allah domin ku san kuna da rai madawwami. (aiōnios g166)
14 This is the boldness which we have toward him, that if we ask anything according to his will, he listens to us.
Wannan shi ne ƙarfin halin da muke da shi sa’ad da muke zuwa a gaban Allah, gama mun san cewa kome muka roƙa bisa ga nufinsa, yakan saurare mu.
15 And if we know that he listens to us, whatever we ask, we know that we have the petitions which we have asked of him.
In kuwa muka san cewa yana sauraranmu, ko mene ne muka roƙa, mun sani, mun riga mun sami abin da muka roƙa daga gare shi ke nan.
16 If anyone sees his brother sinning a sin not leading to death, he shall ask, and God will give him life for those who sin not leading to death. There is sin leading to death. I do not say that he should make a request concerning this.
Kowa ya ga ɗan’uwansa yana yin zunubin da bai kai ga mutuwa ba, sai yă yi masa addu’a. Ta dalilin mai addu’an nan kuwa, Allah zai ba da rai ga mai yin zunubin da bai kai ga mutuwa ba. Akwai zunubin da yakan kai ga mutuwa. Ban ce a yi addu’a domin wannan ba.
17 All unrighteousness is sin, and there is sin not leading to death.
Duk rashin adalci, zunubi ne, amma akwai waɗansu zunuban da ba sa kai ga mutuwa.
18 We know that whoever is born of God does not sin, but he who was born of God keeps himself, and the evil one does not touch him.
Mun san cewa kowane haifaffe na Allah ba ya cin gaba da yin zunubi; kasancewarsa haifaffe na Allah ita takan kāre shi, mugun kuwa ba zai iya cuce shi ba.
19 We know that we are of God, and the whole world lies in the power of the evil one.
Mun san cewa mu’ya’yan Allah ne, duniya duka kuwa tana hannun Mugun.
20 We know that the Son of God has come, and has given us an understanding, that we know the true one, and we are in the true one, in his Son, Jesus Christ. This is the true God and consummate (aiōnios g166) life.
Mun san cewa Ɗan Allah ya zo duniya, ya kuma ba mu ganewa domin mu san shi wanda yake na gaskiya. Mu kuwa muna cikinsa, shi da yake Allah na gaskiya wato, cikin Ɗansa Yesu Kiristi. Shi ne Allah na gaskiya da kuma rai na har abada. (aiōnios g166)
21 Little children, keep yourselves from idols.
’Ya’yana ƙaunatattu, ku yi nesa da gumaka.

< 1 John 5 >