< Jeremias 33 >

1 Herrens ord kom anden gang til Jeremias, medens han endnu sad fængslet i Vagtforgården, således:
Yayinda Irmiya yana a tsare a sansanin matsara, sai maganar Ubangiji ta zo masa sau na biyu cewa,
2 Så siger HERREN, som skabte Jorden og dannede den, idet han grundfæstede den, han, hvis Navn er HERREN:
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci duniya, Ubangiji wanda ya siffanta ta ya kuma kafa ta, Ubangiji ne sunansa.
3 Kald på mig, så vil jeg svare dig og kundgøre dig store og lønlige Ting, du ikke kender.
‘Kira gare ni zan kuwa amsa maka in kuma faɗa maka manyan abubuwan da ba a iya kaiwa, da ba ka sani ba.’
4 Thi så siger HERREN, Israels Gud, om denne Bys Huse og om Judas Kongers Huse, som nedbrødes for at bruges til Volde og Mur,
Gama ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da gidaje a wannan birni da fadodin Yahuda da aka rurrushe domin a yi amfani da su a kan mahaurai da kuma takobi
5 da man gav sig til at stride imod Kaldæerne, og som fyldtes med Ligene af de Mennesker, jeg slog i min Vrede og Harme, og for hvem jeg skjulte mit Åsyn for al deres Ondskabs Skyld:
a yaƙi da Babiloniyawa. ‘Za su cika da gawawwakin mutane waɗanda na kashe da fushina da hasalata. Zan ɓoye fuskata wa wannan birni saboda dukan muguntarsu.
6 Se, jeg vil lade Byens Sår heles og læges, og jeg helbreder dem og oplader for dem en Rigdom af Fred og Sandhed.
“‘Duk da haka, zan kawo lafiya da warkarwa gare ta; zan warkar da mutanena in kuma wadata su da salama da zama lafiya.
7 Jeg vender Judas og Israels Skæbne og opbygger dem som tilforn.
Zan komo da Yahuda da Isra’ila daga bauta zan kuma sāke gina su kamar yadda suke a dā.
8 Jeg renser dem for al deres Brøde, med hvilken de syndede imod mig, og tilgiver alle deres Misgerninger, med hvilke de syndede og forbrød sig imod mig.
Zan tsarkake su daga dukan zunubin da suka yi mini zan kuma gafarta musu dukan zunubansu na yin mini tawaye.
9 Byen skal blive til Glæde, til Pris og Ære blandt alle Jordens Folk; og når de hører om alt det gode, jeg gør den, skal de frygte og bæve over alt det gode og al den Lykke, jeg lader den times.
Sa’an nan birnin nan za tă sa in zama sananne, farin ciki, yabo da girma a gaban dukan al’ummai a duniya da suka ji abubuwa masu kyau da na yi mata; za su kuma yi mamaki su kuma yi rawan jiki saboda yalwar wadata da salamar da na ba ta.’
10 Så siger HERREN: På dette Sted, som I siger er ødelagt, uden Mennesker og Kvæg, i Judas Byer og på Jerusalems Gader, der er lagt øde, uden Mennesker og kvæg,
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Kuna cewa game da wannan wuri, “Kango ne, babu mutane ko dabbobi.” Duk da haka a cikin garuruwan Yahuda da titunan Urushalima da aka yashe, inda ba mutane ko dabbobi, za a sāke jin
11 skal atter høres Fryderåb og Glædesråb, Brudgoms Røst og Bruds Røst, Råb af Folk, som siger: "Tak Hærskarers HERRE; thi HERREN er god, og hans Miskundhed varer evindelig!" og som bringer Takoffer til HERRENs Hus; thi jeg vender Landets Skæbne, så det bliver som tilforn, siger HERREN.
sowa ta farin ciki da murna, muryoyin amarya da na ango, da muryoyin waɗanda suka kawo hadayun salama a gidan Ubangiji suna cewa, “‘“Ku yi godiya ga Ubangiji Maɗaukaki, gama Ubangiji mai alheri ne; ƙaunarsa za tă dawwama har abada.” Gama zan mayar da wadatar ƙasar kamar yadda suke a dā,’ in ji Ubangiji.
12 Så siger Hærskarers HERRE: På dette ødelagte Sted, som er uden Mennesker og Kvæg, og i alle dets Byer skal der atter være Græsgange, hvor Hyrder lader deres Hjorde ligge;
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, ‘A wannan wuri, kango da babu mutane ko dabbobi, cikin dukan garuruwansa za a sāke kasance da wurin kiwo don makiyaya su hutar da garkunansu.
13 i Bjerglandets, Lavlandets og Sydlandets Byer, i Benjamins land, i Jerusalems Omegn og i Judas Byer skal Småkvæget atter gå forbi under Tællerens Hånd, siger HERREN.
A cikin garuruwan ƙasar tudu, garuruwan yammancin gindin dutse da na Negeb, a yankin Benyamin, a cikin ƙauyuka kewayen Urushalima da kuma a cikin garuruwan Yahuda, garkuna za su sāke bi a ƙarƙashin hannun mai ƙidayawa,’ in ji Ubangiji.
14 Se, Dage skal komme, lyder det fra HERREN, da jeg opfylder den Forjættelse, jeg udtalte om Israels og Judas Hus.
“‘Kwanaki suna zuwa,’ in ji Ubangiji, ‘sa’ad da zan cika alkawarin alheri da na yi wa gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
15 I hine Dage og til hin Tid lader jeg en Retfærds Spire fremspire for David, og han skal øve Ret og Retfærd i Landet.
“‘A waɗannan kwanaki da kuma a wannan lokaci zan tā da Reshe mai adalci daga zuriyar Dawuda; zai yi abin da yake daidai da kuma gaskiya a ƙasar.
16 I hine Dage skal Juda frelses og Jerusalem bo trygt, og man skal kalde det: HERREN vor Retfærdighed.
A kwanakin nan zan ceci Yahuda Urushalima kuma za tă zauna lafiya. Sunan da za a kira ta shi ne, Ubangiji Adalcinmu.’
17 Thi så siger HERREN: David skal ikke fattes en Mand til at sidde på Israels Huss Trone.
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Dawuda ba zai taɓa rasa mutumin da zai zauna a gadon sarautar Isra’ila ba,
18 Og Levitpræsterne skal aldrig fattes en Mand til at stå for mit Åsyn og frembære Brændoffer, brænde Afgrødeoffer og ofre Slagtoffer.
ba kuwa firistoci waɗanda suke Lawiyawa za su rasa mutumin da zai ci gaba da tsaya a gabana don miƙa hadayun ƙonawa, ya ƙona hadayun hatsi ya kuma miƙa sadakoki ba.’”
19 Og HERRENs Ord kom til Jeremias således:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
20 Så siger HERREN Hvis min Pagt med Dagen og Natten brydes, så det ikke bliver Dag og Nat, når Tid er inde,
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ka tā da alkawarina na rana da kuma alkawarina na dare, har dare da rana ba za su ƙara bayyana a ƙayyadaddun lokutansu ba,
21 da skal også min Pagt med min Tjener David brydes, så han ikke har nogen Søn til at sidde som Konge på sin Trone, og med Levitpræsterne, som tjener mig.
to, sai a tā da alkawarina da Dawuda bawana da alkawarina da Lawiyawan da suke firistoci masu hidima a gabana, Dawuda kuma ba zai ƙara kasance da zuriyar da za tă yi mulki.
22 Som Himmelens Hær ikke kan tælles og Havets Sand ikke måles, således vil jeg mangfoldiggøre min Tjener Davids Afkom og Leviterne, som tjener mig.
Zan sa zuriyar Dawuda bawana da kuma Lawiyawan da suke hidima a gabana su yi yawa kamar taurarin sararin sama da kuma yashin bakin tekun da ba a iya ƙidaya.’”
23 Og HERRENs Ord kom til Jeremias således:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
24 Har du ikke lagt Mærke til, hvorledes dette Folk siger: "De to Slægter, HERREN udvalgte, har han forkastet!" Og de smæder mit Folk, fordi det i deres Øjne ikke 1ner er et Folk.
“Ba ka lura ba cewa waɗannan mutane suna cewa, ‘Ubangiji ya ƙi masarautai biyu da ya zaɓa’? Saboda haka suka rena mutanena ba sa ƙara ɗaukansu a matsayin al’umma.
25 Så siger HERREN: Hvis jeg ikke har fastsat min Pagt med Dag og Nat, givet Love for Himmel og Jord,
Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ban kafa alkawarina game da rana da kuma game da dare ba in kuma gyara dokokin sama da duniya ba,
26 så vil jeg også forkaste Jakobs Afkom og min Tjener David og ikke af hans Afkom tage Herskere oer Abrabams, Isaks og Jakobs Afkom; thi jeg vender deres Skæbne og forbarmer mig over dem.
to zan ƙi zuriyar Yaƙub da na Dawuda bawana ba zan kuma zaɓi ɗaya daga cikin’ya’yansa maza ya yi mulki a kan zuriyar Ibrahim, Ishaku da Yaƙub ba. Gama zan mayar da wadatarsu in kuma yi musu jinƙai.’”

< Jeremias 33 >