< Jeremias 32 >

1 Det Ord, som kom til Jeramias fra Herren i kong Zedekias af Judas tiende År, det er Nebukadrezars attende.
Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga Ubangiji a shekara ta goma ta Zedekiya sarkin Yahuda, wanda ya kasance shekara ta goma sha takwas ta Nebukadnezzar.
2 Dengang belejrede Babels Konges Hær Jerusalem, og Profeten Jeremas sad fængslet i Vagtforgården i Judas Konges Palads,
Sojojin sarkin Babilon a lokacin suna ƙawanya wa Urushalima annabi Irmiya kuwa yana a tsare a sansanin matsara a fadar Yahuda.
3 hvor Kong Zedekias af Juda havde ladet ham fængsle med de Ord: "Hvor tør du profetere og sige: Så siger HERREN: Se, jeg giver denne By i Babels Konges Hånd, og han skal indtage den;
Zedekiya sarkin Yahuda fa ya sa shi a kurkuku yana cewa, “Don me kake yin annabci? Ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga sarkin Babilon, zai kuwa cinye ta.
4 og Kong Zedekias af Juda skal ikke undslippe Kaldæernes Hånd, men overgives i Babels Konges Hånd, og han skal tale med ham Mund til Mund og se ham Øje i Øje;
Zedekiya sarkin Yahuda ba zai kuɓuta daga hannuwan Babiloniyawa ba amma tabbatacce za a ba da shi ga sarkin Babilon, zai kuwa yi masa magana fuska da fuska ya kuma gan shi da idanunsa.
5 og han skal føre Zedekias til Babel, og der skal han blive, til jeg ser til ham, lyder det fra HERREN; når I kæmper med Kaldæerne, får I ikke Lykke!"
Zai kai Zedekiya Babilon, inda zai zauna har sai ya magance shi, in ji Ubangiji. In ka yi yaƙi da Babiloniyawa, ba za ka yi nasara ba.’”
6 Og Jeremias sagde: HERRENs Ord kom til mig således:
Irmiya ya ce, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
7 Se, Hanamel, din Farbroder Sjallums Søn, kommer til dig og siger: "Køb min Mark i Anatot, thi du har Indløsningsret."
Hananel ɗan Shallum ɗan’uwan mahaifinka zai zo wurinka ya ce, ‘Saya filina a Anatot, domin a matsayinka na dangi na kurkusa hakkinka ne kuma kai ya wajaba ka saye shi.’
8 Så kom Hanamel, min Farbroders Søn, til mig i Vagtforgården, som HERREN havde sagt, og sagde til mig: "Køb min Mark i Anatot i Benjamins Land, thi du har Arveretten, og indløsningsretten er din; køb dig den!" Da forstod jeg, at det var HERRENs Ord.
“Sa’an nan, kamar dai yadda Ubangiji ya faɗa, sai ga Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina ya zo wurina a sansanin matsara ya ce, ‘Saya filina a Anatot a yankin Benyamin. Da yake hakkinka ne ka fanshe shi ka kuma mallake shi, ka sayo shi wa kanka.’ “Sai na gane cewa wannan maganar Ubangiji ce;
9 Og jeg købte Marken i Anatot af Hanamel, min Farbroders Søn, og tilvejede ham Pengene, sytten Sekel Sølv;
saboda haka sai na saye filin a Anatot daga hannun Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina na kuma auna masa shekel goma sha bakwai na azurfa.
10 og jeg skrev Skøde og forseglede det, tilkaldte Vidner og afvejede Pengene på Vægtskål.
Na sa hannu a takarda, na buga hatimi na liƙe, na sami shaidu na kuwa auna shekel a ma’auni.
11 Så tog jeg Skødet, både det forseglede og det åbne,
Na ɗauki takardar ciniki, takardar da aka rubuta sharuɗan a ciki, da kuma takardar da ba a liƙe ba,
12 og overgav Skødet til Baruk, Masejas Søn Nerijas Søn, i Nærværelse af Hanamel, min Farbroders Søn, og Vidnerne, som havde underskrevet Skødet, og alle de Judæee, som var til Stede i Vagtforgården;
na kuma ba wa Baruk ɗan Neriya, ɗan Masehiya, wannan takarda a gaban Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina da kuma a gaban shaidun da suka sa hannu a takardan ciniki da kuma a gaban dukan Yahudawan da suke zaune a sansanin matsaran.
13 og i deres Nærværelse bød jeg Baruk:
“A gabansu na yi wa Baruk waɗannan umarnai cewa,
14 "Så siger Hærskarers HERRE, Israels Gud: Tag disse Skøder, både det forseglede og det åbne, og læg dem i en Lerkrukke, for at de kan holde sig i lange Tider.
‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka ɗauki waɗannan takardun ciniki, wanda aka liƙe da wanda ba a liƙe ba, ka sa su a cikin tulun yumɓu don kada su lalace.
15 Thi så siger Hærskarers HERRE, Israels Gud: End skal der købes Huse, Marker og Vingårde i dette Land!"
Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa za a sāke saye gidaje, filaye da gonakin inabi a wannan ƙasa.’
16 Efter at have overgivet Skødet til Baruk, Nerijas Søn, bad jeg således til HERREN:
“Bayan na ba da takardun ciniki ga Baruk ɗan Neriya, sai na yi addu’a ga Ubangiji na ce,
17 Ak, Herre, HERRE, du har jo skabt Himmelen og Jorden ved din vældige Styrke og din udstrakte Arm, intet er dig for underfuldt,
“A, Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi sammai da duniya ta wurin ikonka mai girma da kuma hannunka mai iko. Ba abin da ya gagare ka.
18 du, som øver Miskundhed mod Tusinder og gengælder Fædres Misgerning på deres Sønner efter dem; du store, vældige Gud, hvis Navn er Hærskarers HERRE,
Kakan nuna ƙauna ga dubbai amma kakan hukunta’ya’ya saboda laifin ubanninsu a bayansu. Ya mai girma da kuma Allah mai iko, wanda sunansa ne Ubangiji Maɗaukaki,
19 rig på Råd og stor i Dåd, hvis Øjne er åbne over alle Menneskebørnenes Veje, for at du kan give enhver efter hans Vej og hans Gerningers Frugt;
manufofinka da girma suke, ayyukanka kuma masu girma ne. Idanunka suna a buɗe ga dukan hanyoyin mutane; kakan sāka wa kowa gwargwadon halinsa yadda ya dace.
20 du, som gjorde Tegn og Undere i Ægypten og gør det den Dag i Dag både i Israel og blandt andre Mennesker og skabte dig det Navn, du har i Dag,
Ka aikata ayyukan banmamaki da kuma al’ajabai a Masar ka kuma ci gaba da su har yă zuwa yau, a Isra’ila da kuma a cikin dukan’yan adam, ka kuma sami sunan da har yanzu yake naka.
21 du, som førte dit Folk Israel ud af Ægypten med Tegn og Undere, med stærk Hånd og udstrakt Arm og stor Rædsel
Ka fitar da mutanenka Isra’ila daga Masar da alamu da abubuwa banmamaki, ta wurin hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi tare da banrazana mai girma.
22 og gav dem dette Land, som du havde svoret deres Fædre at ville give dem, et Land, der flyder med Mælk og Honning;
Ka ba su wannan ƙasa da ka rantse za ka ba wa kakanni kakanninsu, ƙasa mai zub da madara da zuma.
23 og de kom og tog det i Eje; men de hørte ikke din Røst og adlød ikke din Lov; de gjorde intet af, hvad du havde pålagt dem; så lod du al denne Ulykke ramme dem.
Suka shiga suka mallake ta, amma ba su yi maka biyayya ba, ba su kuma bi dokarka ba; ba su yi abin da ka umarce su ba. Saboda haka ka kawo masifa a kansu.
24 Se, Stormvoldene har nået Byen, så den er ved at blive indtaget, og med Sværd, Hunger og Pest er Byen givet i de angribende Kaldæeres Hånd; had du talede, er sket, og du ser det selv.
“Duba yadda aka gina mahaurai don a kame birni. Saboda takobi, yunwa da annoba, za a ba da birnin ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye shi da yaƙi. Abin da ka faɗa ya faru, yadda kake gani yanzu.
25 Og skønt Byen er givet i Kaldæernes Hånd, siger du til mig, Herre, HERRE: "Køb dig Marken for Penge og tag Vidner derpå!"
Ko da yake za a ba da birnin ga Babiloniyawa, kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka ce mini, ‘Saye fili da azurfa ka kuma sa a shaida cinikin.’”
26 Da kom HERRENs Ord til Jeremias således:
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
27 Se, jeg er HERREN, alt Køds Gud; skulde noget være mig for underfuldt?
“Ni ne Ubangiji Allah na dukan’yan adam. Akwai wani abin da ya gagare ni?
28 Derfor, så siger HERREN: Se, jeg giver denne By i kaldæernes og Kong Nebukadrezar af Babels Hånd, og han skal idtage den;
Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga Babiloniyawa da kuma ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, wanda zai yaƙe ta.
29 og Kaldæerne, der angriber denne By, skal komme og sætte Ild på den og afbrænde Husene, på hvis Tage man tændte Offerild for Baal og udgød Drikofre for andre Guder for at krænke mig.
Babiloniyawan da suke yaƙi da wannan birni za su zo ciki su cinna masa wuta; tare da gidaje inda mutane suka tsokane ni na yi fushi ta wurin ƙona turare a rufin ɗakuna wa Ba’al suka zub da hadayun sha wa waɗansu alloli.
30 Thi fra deres Ungdom af har Israeliterne og Judæerne kun gjort, hvad der var ondt i mine Øjne; thi Israeliterne gør ikke andet end krænke mig ved deres Hænders Værk, lyder det fra HERREN.
“Mutanen Isra’ila da na Yahuda ba abin da suka yi sai mugunta a gabana daga ƙuruciyarsu; tabbatacce, mutanen Isra’ila ba su yi kome ba sai dai tsokane ni da abin da hannuwansu suka yi, in ji Ubangiji.
31 Ja, en Kilde til Vrede og Harme har denne By været mig, lige fra den Dag de byggede den og til i Dag, så at jeg må fjerne den fra mit Åsyn
Daga ranar da aka gina ta har zuwa yanzu, wannan birni ta tā da fushina da hasalata da dole a kawar da ita daga gabana.
32 for alt det ondes Skyld, som Israeliterne og Judæerne gjorde for at krænke mig, de deres Konger, Fyrster, Præster og Profefer, Judas Mænd og Jerusalems Borgere.
Mutanen Isra’ila da na Yahuda sun tsokane ni ta wurin dukan muguntar da suka aikata su, sarakunansu da fadawansu, firistocinsu da annabawa, mutanen Yahuda da mutanen Urushalima.
33 De vendte Ryggen og ikke Ansigtet til mig, og skønt jeg advarede dem årle og silde, vilde de ikke høre eller tage ved Lære.
Sun juya mini bayansu ba fuskokinsu ba; ko da yake na koyar da su sau da sau, ba su saurara ko bi horo na ba.
34 De opstillede deres væmmelige Guder i det Hus, mit Navn nævnes over, for at gøre det urent;
Sun kafa gumakansu na banƙyama a cikin haikalina wanda ake kira da sunana, sun kuwa ƙazantar da shi.
35 og de byggede Baals Offerhøje i Hinnoms Søns Dal for at ofre deres Sønner og Døtre til Molok, hvad jeg ikke havde budt dem, og hvad aldrig var i min Tanke, at man skulde gøre så vederstyggelig en Ting for derved at lokke Juda til Synd.
Sun gina masujadai kan tudu wa Ba’al a Kwarin Ben Hinnom don su miƙa’ya’yansu maza da mata hadaya ga Molek, ko da yake ban taɓa umarce su ba, bai kuma zo mini cewa su yi abin banƙyama irin wannan ba ta haka suka sa Yahuda ya yi zunubi.
36 Men nu, så siger HERREN, Israels Gud, om denne By, som I siger er givet i Babels Konges Hånd med Sværd, Hunger og Pest:
“Kana cewa game da wannan birni, ‘Ta wurin takobi, yunwa da annoba za a ba da shi ga sarkin Babilon’; amma ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa
37 Se, jeg vil samle dem fra alle de Lande, som jeg har bortstødt dem til i min Vrede og Harme og i stor Fortørnelse, og føre dem hjem til dette Sted og lade dem bo trygt.
tabbatacce zan tattara su daga dukan ƙasashen da na kore su zuwa cikin fushina da hasalata mai girma; zan komo da su wurin nan in sa su zauna lafiya.
38 De skal være mit Folk, og jeg vil være deres Gud;
Za su zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnsu.
39 og jeg vil give dem eet Hjerte og een Vej, så de frygter mig alle Dage, at det må gå dem og deres Sønner efter dem vel.
Zan ba su zuciya ɗaya da aiki ɗaya, don kullum su ji tsorona domin amfaninsu da kuma amfanin’ya’yansu a bayansu.
40 Jeg slutter en evig Pagt med dem, at jeg ikke vil drage mig tilbage fra dem, men gøre vel itnod dem; og min Frygt lægger jeg i deres Hjerter, så de ikke viger fra mig.
Zan yi madawwamin alkawari da su. Ba zan taɓa barin aikata musu alheri ba, zan kuma iza su su ji tsorona, don kada su ƙara juya daga gare ni.
41 Jeg vil glæde mig over dem og gøre vel imod dem; og jeg planter dem i dette Land i Trofasthed af hele mit Hjerte og hele min Sjæl.
Zan yi farin ciki a yin musu alheri, tabbatacce zan su dasa a wannan ƙasa da dukan zuciyata da dukan raina.
42 Thi så siger HERREN: Som jeg bragte al denne store Ulykke over dette Folk, således vil jeg bringe over dem alt det gode, jeg taler til dem om.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, yadda na kawo dukan wannan masifa a kan wannan mutane, haka zan ba su wadatar da na yi musu alkawari.
43 End skal der købes Marker i det Land, som I siger er en Ørken uden Mennesker og Kvæg og givet i Kaldæernes Hånd;
Za a sāke sayi filaye a wannan ƙasa da kuka ce, ‘Kango ce, ba mutane ko dabbobi, gama an ba da ita ga Babiloniyawa.’
44 man skal købe Marker for Penge og skrive Skøder og forsegle dem og tilkalde Vidner i Benjamins Land, i Jerusalems Omegn, i Judas Byer, i Bjerglandets, Lavlandets og Sydlandets Byer; thi jeg vender deres Skæbne, lyder det fra HERREN.
Za a sayi filaye da azurfa, a kuma sa hannu a takardan ciniki, a liƙe a kuma shaida a yankin Benyamin, a ƙauyukan kewayen Urushalima, a garuruwan Yahuda da kuma a garuruwan ƙasar tudu, na yammancin gindin dutse da na Negeb, domin zan maido da wadatarsu, in ji Ubangiji.”

< Jeremias 32 >