< 2 Samuel 1 >

1 Da David efter Sauls Død var vendt tilbage fra Sejeren over Amalek og havde opholdt sig to Dage i Ziklag,
Bayan mutuwar Shawulu, Dawuda ya dawo daga karkashe Amalekawa. Sai ya zauna a Ziklag kwana biyu.
2 kom der Tredjedagen en Mand fra Hæren, fra Saul, med sønderrevne Klæder og Jord på Hovedet, og da han kom hen til David, kastede han sig til Jorden og bøjede sig.
A rana ta uku sai ga wani mutum ya zo daga sansanin Shawulu da yagaggen riga da ƙura a kansa. Da ya zo wurin Dawuda sai ya fāɗi a ƙasa don yă nuna bangirma.
3 David spurgte ham: "Hvor kommer du fra?" Han svarede: "Jeg slap bort fra Israels Hær!"
Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Daga ina ka fito?” Ya amsa ya ce, “Na tsere ne daga sansanin Isra’ila.”
4 David sagde da til ham: "Hvorledes gik det? Fortæl mig det!" Han svarede: "Folket flygtede fra Kampen, og mange af Folket faldt og døde; også Saul og hans Søn Jonatan er døde."
Dawuda ya ce, “Gaya mini, me ya faru?” Sai ya ce, “Mutane sun gudu daga yaƙi, aka kuma karkashe yawancin mutane. Shawulu da ɗansa Yonatan ma sun mutu.”
5 Da sagde David til den unge Mand, som bragte ham Budet: "Hvoraf ved du, at Saul og hans Søn Jonatan er døde?"
Sai Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Yaya ka san cewa Shawulu da ɗansa Yonatan sun mutu?”
6 Den unge Mand, der bragte ham Budet, svarede: "Det traf sig, at jeg var på Gilboas Bjerg, og se, Saul stod lænet til sit Spyd, medens Vognene og Rytterne trængte ham;
Saurayin ya ce, “Ina kan dutsen Gilbowa a lokacin sai na ga Shawulu jingine a māshinsa. Kekunan yaƙi da mahayansu suna matsowa kusa da shi.
7 og da han vendte sig om, fik han Øje på mig og kaldte på mig; og jeg sagde: Her er jeg!
Da ya juya ya gan ni sai ya kira ni, na kuwa ce masa, ‘Ga ni?’
8 Da spurgte han mig: Hvem er du? Og jeg svarede: Jeg er en Amalekit!
“Ya tambaye ni ya ce, ‘Wane ne kai?’ “Na ce, ‘Ni mutumin Amalek ne.’
9 Så sagde han til mig: Kom herhen og giv mig Dødsstødet! Thi Krampen har grebet mig, men jeg lever endnu!
“Sai ya ce mini, ‘Matso kusa ka kashe ni! Ina cikin azabar mutuwa, sai dai har yanzu ina da rai.’
10 Og jeg trådte hen til ham og gav ham Dødsstødet, thi jeg så, at han ikke kunde leve, når han faldt om. Så tog jeg Diademet, han havde på Hovedet, og et Armbånd, han bar på Armen, og dem har jeg med hid til min Herre."
“Saboda haka na matso kusa da shi na kashe shi, domin na san cewa ba zai yi rai ba, da yake ya riga ya fāɗi. Sai na cire rawanin da yake kansa, na kuma cire warwaron hannunsa, na kuwa kawo maka su duka, ranka yă daɗe!”
11 Da tog David fat i sine Klæder og sønderrev dem, og ligeså gjorde alle hans Mænd;
Sai Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka yayyage rigunarsu.
12 og de holdt Klage, græd og fastede til Aften over Saul og hans Søn Jonatan og HERRENs Folk og Israels Hus, fordi de var faldet for Sværdet.
Suka yi makoki, da kuka, da azumi har yamma saboda Shawulu da ɗansa Yonatan, da saboda sojojin Ubangiji, da kuma gidan Isra’ila, gama an karkashe su a yaƙi.
13 Derpå sagde David til den unge Mand, som havde bragt ham Budet: "Hvor er du fra?" Han svarede: "Jeg er Søn af en Amalekit, der bor her som fremmed."
Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Daga ina ka fito?” Ya ce, “Ni ɗan wani baƙo ne, mutumin Amalek.”
14 Da sagde David: "Frygtede du dog ikke for at lægge Hånd på HERRENs Salvede og dræbe ham!"
Dawuda ya ce masa, “Yaya ba ka ji tsoro ɗaga hannu ka hallaka shafaffe na Ubangiji ba?”
15 David kaldte så på en af sine Folk og sagde: "Kom herhen og stød ham ned!" Og han slog ham ihjel.
Sai Dawuda ya kira ɗaya daga cikin mutanensa ya ce, “Je ka kashe shi!” Haka kuwa ya buge shi, ya kuwa mutu.
16 Men David sagde til ham: "Dit Blod komme over dit eget Hoved! Thi din egen Mund vidnede imod dig, da du sagde: Jeg gav HERRENs Salvede Dødsstødet!"
Gama Dawuda ya riga ya ce masa, “Alhakin jininka yana bisa kanka tun da yake da bakinka ka ce, ‘Ni ne na kashe shafaffe na Ubangiji.’”
17 Da sang David denne Klagesang over Saul og hans Søn Jonatan.
Dawuda ya rera wannan makoki saboda Shawulu da ɗansa Yonatan.
18 Den skal læres af Judas Sønner; den står optegnet i de Oprigtiges Bog.
Ya umarta a koya wa mutanen Yahuda wannan waƙa mai suna Makokin Baka (tana a rubuce a Littafin Yashar),
19 Din Pryd, Israel, ligger dræbt på dine Høje. Ak, at dog Heltene faldt!
“Ya Isra’ila, an kashe darajarki a kan tuddanki. Ga shi, jarumawa sun fāɗi!
20 Forkynd det ikke i Gat, ej lyde der Glædesbud på Askalons Gader, at ikke Filisternes Døtre skal fryde sig, de uomskårnes Døtre juble!
“Kada a faɗe shi a Gat, kada a yi shelarsa a titunan Ashkelon, don kada’yan matan Filistiyawa su yi murna don kada’yan matan marasa kaciya su yi farin ciki.
21 Gilboas Bjerge! Ej falde Dug og Regn på eder, I Dødens Vange! Thi Heltenes Skjolde vanæredes der; Sauls Skjold er ej salvet med Olie.
“Ya duwatsun Gilbowa, kada a sāke yin ruwa ko raɓa a kanku, balle gonakin da suke ba da hatsin hadaya su ƙara bayarwa. Gama a can ne garkuwoyin manyan sojoji suka kwanta, suka kwanta a wulaƙance. Garkuwar Shawulu kuwa, ba za a ƙara shafa mata mai ba.
22 Uden faldnes Blod, uden Heltes Fedt kom Jonatans Bue ikke tilbage, Sauls Sværd ikke sejrløst hjem.
“Daga jinin waɗanda aka kashe, daga tsokar naman jarumi, bakan Yonatan bai juye baya ba, takobin Shawulu bai komo ba tare da gamsuwa ba.
23 Saul og Jonatan, de elskelige, hulde, skiltes ikke i Liv eller Død; hurtigere var de end Ørne, stærkere var de end Løver!
Shawulu da Yonatan, a raye ƙaunatattu ne da kuma bansha’awa, a mace kuma ba su rabu ba. Sun fi gaggafa sauri, sun fi zaki ƙarfi.
24 O, Israels Døtre, græd over Saul, som klædte eder yndigt i Purpur, satte Guldsmykker på eders Klæder!
“Ya ku’yan matan Isra’ila, ku yi kuka saboda Shawulu, wanda ya suturta ku da jajjayen kayan ado, wanda ya yi wa rigunarku ado da zinariya.
25 Ak, at dog Heltene faldt i Slagets Tummel - dræbt ligger Jonatan på dine Høje!
“Jarumawa sun fāɗi a yaƙi! Ga Yonatan matacce a tuddanku.
26 Jeg sørger over dig, Jonatan, Broder, du var mig såre kær; underfuld var mig din Kærlighed, mere end Kvinders Kærlighed.
Na yi baƙin ciki saboda kai, Yonatan ɗan’uwana; ƙaunatacce kake a gare ni. Ƙaunarka a gare ni abar al’ajabi ce, abar al’ajabi fiye da ta mace.
27 Ak, at dog Heltene faldt, Stridsvåbnene lagdes øde!
“Jarumawa sun fāɗi! Makaman yaƙi sun hallaka!”

< 2 Samuel 1 >