< Første Kongebog 1 >

1 Da Kong David var gammel og til års, kunne han ikke blive varm, skønt man dækkede ham til med Tæpper.
Sa’ad da Sarki Dawuda ya tsufa ya kuma ƙara shekaru, ba ya iya jin ɗumi ko an rufe shi da abin rufuwa.
2 Da sagde hans Folk til ham: "Det er bedst, man søger efter en ung Jomfru til min Herre Kongen, for at hun kan være om Kongen og pleje ham; når hun ligger i din Favn, bliver min Herre Kongen varm!"
Saboda haka bayinsa suka ce masa, “Bari mu nemi wata budurwa wadda za tă yi wa ranka yă daɗe, sarki hidima, tă kuma kula da shi. Za tă dinga kwanta kusa da ranka yă daɗe, yă ji ɗumi.”
3 Så søgte de efter en smuk ung Pige i hele Israels Land og fandt Abisjag fra Sjunem og bragte hende til Kongen.
Suka nemi kyakkyawar yarinya cikin fāɗin Isra’ila, sai suka sami Abishag, mutuniyar Shunam, suka kawo ta wa sarki.
4 Hun var en såre smuk Pige: og hun plejede kongen og gik ham til Hånde; men Kongen havde ikke Omgang med hende.
Yarinyar kuwa kyakkyawa ce ƙwarai; ta kuwa lura da sarki, ta kuma yi masa hidima, amma sarki bai yi jima’i da ita ba.
5 Adonija, Haggits Søn, dristede sig til at sige: "Jeg vil være Konge!" Og han skaffede sig Vogne og Heste og halvtredsindstyve Mænd til at løbe foran sig.
Adoniya, wanda mahaifiyarsa ce Haggit, ya fito ya ce, “Zan zama sarki.” Saboda haka ya nemi kekunan yaƙi, ya kuma shirya dawakai, tare da mutane hamsin da za su sha gabansa.
6 Hans Fader havde ingen Sinde irettesat ham og sagt: "Hvorfor bærer du dig således ad?" Han havde et såre smukt Ydre og var den ældste efter Absalom.
(A duk rayuwarsa mahaifinsa bai taɓa tsawata masa yă ce, “Me ya sa kake yin haka ba?” Shi kuwa mai kyan gani ne ƙwarai, shi ne aka haifa bayan Absalom.)
7 Han underhandlede med Joab, Zerujas Søn, og Præsten Ebjatar; de tog Adonijas Parti og støttede ham,
Adoniya ya haɗa baƙi da Yowab ɗan Zeruhiya da kuma Abiyatar firist, suka kuma ba shi goyon baya.
8 mens Præsten Zadok, Jojadas Søn Benaja, Profeten Natan, Sjim i og Re'i og Davids Kærnetropper ikke sluttede sig til Adonija.
Amma Zadok firist, Benahiya ɗan Yehohiyada, annabi Natan, Shimeyi, Reyi da kuma matsara na musamman na Dawuda ba su bi Adoniya ba.
9 Adonija lod nu slagte Små kvæg, Hornkvæg og Fedekvæg ved Slangestenen, der står ved Rogelkilden, og indbød alle sine Brødre, Kongesønnerne, og alle de judæiske Mænd, der stod i Kongens Tjeneste;
Wata rana Adoniya ya tafi Dutsen Zohelet kusa da En Rogel, inda ya yi hadayar tumaki, da shanun noma, da shanun da ake kiwo a gida. Ya kuma gayyaci’yan’uwansa, wato, sauran’ya’yan Sarki Dawuda, tare da dukan dattawan sarki da suka fito daga Yahuda,
10 men Profeten Natan, Benaja, Kærnetropperne og sin Broder Salomo indbød han ikke.
amma bai gayyaci annabi Natan, ko Benahiya, ko wani daga matsara na musamman, ko kuwa ɗan’uwansa Solomon ba.
11 Da sagde Natan til Batseba, Salomos Moder: "Du har vel hørt, at Adonija, Haggits Søn, har opkastet sig til Konge uden vor Herre Davids Vidende?
Sai Natan ya ce wa Batsheba, mahaifiyar Solomon, “Ki san cewa Adoniya, ɗan Haggit, ya zama sarki ba tare da sanin ranka yă daɗe, sarkinmu Dawuda ba?
12 Lad mig nu give dig et Råd, for at du kan redde dit eget og din søn Salomos Liv:
Yanzu bari in ba ki shawara yadda za ki cece ranki da kuma ran ɗanki Solomon.
13 Du skal gå ind til Kong David og sige til ham: Herre konge, du har jo tilsvoret din Trælkvinde: Din Søn Salomo skal være Konge efter mig og sidde på min Trone! Hvorfor har da Adonija opkastet sig til Konge?
Ki shiga wurin Sarki Dawuda ki ce masa, ‘Ranka yă daɗe sarki, ba ka rantse mini ni baiwarka cewa, “Tabbatacce Solomon ɗanka ne zai zama sarki bayana, yă kuma zauna a kujerar sarautar ba”? To, me ya sa Adoniya ya zama sarki?’
14 Og medens du endnu står og taler med Kongen, kommer jeg til og bekræfter dine Ord!"
Yayinda kike can kina magana da sarki, zan shiga in kuma tabbatar da abin da kika faɗa.”
15 Da gik Batseba ind til kongen i hans Værelse - Kongen var meget gammel, og Abisjag fra Sjunem gik ham til Hånde -
Saboda haka Batsheba ta je don tă ga sarki. A yanzu dai sarki ya tsufa, yana nan kuma a cikin ɗakinsa, inda Abishag mutuniya Shunam take masa hidima.
16 og Batseba bøjede sig og kastede sig til Jorden for Kongen. Da sagde Kongen: "Hvad ønsker du?"
Batsheba ta rusuna ta kuma durƙusa a gaban sarki. Sai sarki ya tambaye ta ya ce, “Me kike so?”
17 Hun svarede: "Herre, du har jo tilsvoret din Trælkvinde ved HERREN din Gud: Din Søn Salomo skal være konge efter mig og sidde på min Trone!
Ta ce masa, “Ranka yă daɗe, kai kanka ka rantse mini ni baiwarka da sunan Ubangiji Allahnka cewa, ‘Solomon ɗanka zai zama sarki bayana, zai kuma zauna a kujerar sarautata.’
18 Men se, nu har Adonija opkastet sig til Konge uden dit Vidende, Herre Konge!
Amma yanzu Adoniya ya zama sarki, kai kuwa ranka yă daɗe sarki, ba ka san wani abu game da shi ba.
19 Han har ladet slagte Hornkvæg, Fedekvæg og Småkvæg i Mængde og indbudt alle Kongesønnerne, Præsten Ebjatar og Hærføreren Joab, men din Træl Salomo har han ikke indbudt.
Ya miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa, ya kuma gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da Abiyatar firist, da Yowab shugaban mayaƙa, amma bai gayyaci Solomon bawanka ba.
20 På dig, Herre Konge, er hele Israels Øjne rettet, for at du skal give dem til Kende, hvem der skal være din Efterfølger og sidde på min Herre Kongens Trone.
Ranka yă daɗe sarki, idanun dukan Isra’ila suna a kanka, domin su san wa zai zauna a kujerar ranka yă daɗe sarkina, a bayanka.
21 Ellers gælder det mit og min Søn Salomos Liv, når min Herre Kongen har lagt sig til Hvile hos sine Fædre!"
In ba haka, bayan an binne ranka yă daɗe sarki, tare da kakanninsa, za a wulaƙance ni da Solomon ɗana, kamar masu laifi.”
22 Medens hun endnu talte med Kongen, kom Profeten Natan,
Yayinda take cikin magana tare da sarki, sai annabi Natan ya iso.
23 og det blev meldt Kongen: "Profeten Natan er her!" Så trådte han frem for Kongen og kastede sig på sit Ansigt til Jorden for ham.
Sai aka faɗa wa sarki, “Ga annabi Natan.” Da Natan ya je gaban sarki, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
24 Derpå sagde Natan: "Herre konge, du har vel sagt, at Adonija skal være Konge efter dig og sidde på din Trone?
Natan ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki, ko ka furta cewa Adoniya ne zai zama sarki a bayanka, yă kuma zauna a kujerar sarautarka?
25 Thi han er i Dag draget ned og har ladet slagte Hornkvæg, Fedekvæg og Småkvæg i Mængde og indbudt alle Kongesønnerne, Hærførerne og Præsten Ebjatar, og nu spiser og drikker de sammen med ham og råber: Leve Kong Adonija!
Yau ya gangara, ya kuma miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa. Ya gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da shugaban mayaƙa, da kuma Abiyatar firist. A yanzu haka suna ci, suna sha, tare da shi, suna cewa, ‘Ran Sarki Adoniya yă daɗe!’
26 Men han har hverken indbudt mig, din Træl, eller Præsten Zadok eller Benaja, Jojadas Søn, eller din Træl Salomo!
Amma bai gayyace ni bawanka, da Zadok firist, da Benahiya ɗan Yehohiyada, da kuma bawanka Solomon ba.
27 Er det virkelig sket efter min Herre Kongens Befaling, uden at du har ladet dine Trælle vide, hvem der skal sidde på min Herre Kongens Trone efter dig?"
Ranka yă daɗe, sarki, ko ka tabbatar da haka, amma ba ka ko faɗa wa fadawanka, cewa ga wanda zai gāje Ranka yă daɗe, sarki ba?”
28 Da svarede Kong David: "Kald mig Batseba hid!" Og hun trådte frem for Kongen og stillede sig foran ham.
Sai Dawuda ya ce, “Kira Batsheba tă shiga.” Sai ta zo gaban sarki ta kuma tsaya a gabansa.
29 Da svor Kongen og sagde: "Så sandt HERREN, der udløste mig af al min Nød, lever:
Sai sarki ya yi rantsuwa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya cece ni daga kowace damuwa,
30 Som jeg tilsvor dig ved HERREN, Israels Gud, at din Søn Salomo skulde være Konge efter mig og sidde på min Trone i mit Sted, således vil jeg handle i Dag!"
tabbatacce a yau zan aikata abin da na yi miki rantsuwa da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila; Solomon ɗanki zai zama sarki bayana, kuma shi zai zauna a kan kujerar sarautata a maimakona.”
31 Da bøjede Batseba sig med sit Ansigt til Jorden og faldt ned for Kongen og sagde: "Måtte min Herre, Kong David, leve evindelig!"
Sai Batsheba ta rusuna da fuskarta har ƙasa, ta kuma durƙusa a gaban sarki ta ce, “Bari ran Sarkina Dawuda yă daɗe, har abada!”
32 Derpå sagde Kong David: "Kald mig Præsten Zadok, Profeten Natan og Benaja, Jojadas Søn, hid!" Og de trådte frem for Kongen.
Sarki Dawuda ya ce, “Ku kira mini Zadok firist, annabi Natan, da Benahiya ɗan Yehohiyada.” Da suka zo gaban sarki,
33 Da sagde Kongen til dem: "Tag eders Herres Folk med eder, sæt min Søn Salomo på mit eget Muldyr og før ham ned til Gihon.
sai ya ce musu, “Ku ɗauki bayin sarki tare da ku, ku kuma sa ɗana Solomon a kan dokina, ku gangara da shi zuwa Gihon.
34 Der skal Præsten Zadok og Profeten Natan salve ham til Konge over Israel, og I skal støde i Hornet og råbe: Leve Kong Salomo!
A can ku sa Zadok firist, da annabi Natan su shafe shi sarki a bisa Isra’ila. Ku busa ƙaho, ku kuma yi ihu, kuna cewa, ‘Ran Sarki Solomon yă daɗe!’
35 Så skal I følge ham herop, og han skal gå hen og sætte sig på min Trone og være Konge i mit Sted; thi det er ham, jeg har udset til Fyrste over Israel og Juda!"
Sa’an nan ku haura tare da shi, zai kuwa zo yă zauna a kujera sarautata, yă yi mulki a maimakona. Na naɗa shi mai mulki a bisa Isra’ila da Yahuda.”
36 Da svarede Benaja, Jojadas Søn, Kongen: "Det ske! Måtte HERREN, min Herre Kongens Gud, gøre således!
Benahiya ɗan Yehohiyada ya amsa wa sarki, ya ce, “Amin! Bari Ubangiji Allah na ranka yă daɗe sarkina, yă tabbatar da haka.
37 Måtte HERREN være med Salomo, som han har været med min Herre Kongen, og gøre hans Trone endnu mægtigere end min Herre kong Davids!"
Kamar yadda Ubangiji ya kasance da ranka yă daɗe, sarki, haka ma bari yă kasance da Solomon, yă kuma mai da kujerar sarautarsa tă fi kujerar sarautar ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, girma!”
38 Derpå drog Præsten Zadok, Profeten Natan og Benaja, Jojadas Søn, og Kreterne og Pleterne ned og satte Salomo på Kong Davids Muldyr og førte ham til Gihon;
Sai Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa suka gangara, suka sa Solomon a kan dokin Sarki Dawuda, suka raka shi zuwa Gihon.
39 og Præsten Zadok tog Oliehornet fra Teltet og salvede Salomo; de stødte i Hornet, og hele Folket råbte: "Leve Kong Salomo!"
Zadok firist ya ɗauki ƙahon mai daga tenti mai tsarki, ya shafe Solomon. Sa’an nan suka busa ƙaho, sai dukan mutane suka yi ihu, suna cewa “Ran Sarki Solomon yă daɗe!”
40 Så fulgte hele Folket ham op og Folket spillede på Fløjter og jublede højt, så at Jorden var ved at revne af deres Råb.
Dukan mutane kuwa suka haura suka bi shi, suna busan sarewa, suna farin ciki sosai, har ƙasa ta girgiza saboda sowa.
41 Det hørte Adonija og alle hans Gæster, netop som de var færdige med Måltidet, og da Joab hørte Hornets klang, sagde han: "Hvorfor er der så stort Røre i Byen?"
Adoniya tare da dukan baƙin da suke tare da shi kuwa suka ji wannan sa’ad da suke gama bikinsu. Da jin busan ƙaho, sai Yowab ya yi tambaya, ya ce, “Me ya jawo surutu haka a birni?”
42 Endnu medens han talte, kom Jonatan, Præsten Ebjatars Søn. Adonija sagde: "Kom herhen, thi du er en brav Mand og bringer godt nyt!"
Tun yana cikin magana, sai Yonatan ɗan Abiyatar ya iso. Adoniya ya ce, “Shigo! Ai, mutumin kirki irinka, lalle ka kawo labari mai daɗi ne.”
43 Men Jonatan svarede og sagde til Adonija: "Tværtimod; vor Herre Kong David har gjort Salomo til Konge!
Yonatan ya ce wa Adoniya, “A ina! Ranka yă daɗe, Sarkinmu Dawuda ya naɗa Solomon sarki.
44 Kongen sendte Præsten Zadok, Profeten Natan, Benaja, Jojadas Søn, og Kreterne og Pleterne med ham, og de satte ham på Kongens Muldyr;
Sarki ya aika shi tare da Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa, suka sa shi a kan dokin sarki,
45 og Præsten Zadok og Profeten Natan salvede ham til Konge ved Gihon; derefter drog de under Jubel op derfra, og der blev Røre i Byen; det var den Larm, I hørte.
Zadok firist kuwa da annabi Natan sun shafe shi sarki a Gihon. Daga can suka haura suna kirari, birni kuwa ta ɓarke da sowa. Surutun da kake ji ke nan.
46 Salomo satte sig også på Kongetronen;
Ban da haka ma, Solomon ne sarki yanzu.
47 tilmed kom Kongens Folk og lykønskede vor Herre Kong David med de Ord: Måtte din Gud gøre Salomos Navn endnu herligere end dit og hans Trone mægtigere end din! Og Kongen tilbad på sit Leje;
Yanzu haka, fadawa sun zo suna wa ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, sam barka, suna cewa, ‘Bari Allahnka yă sa sunan Solomon yă zama sananne fiye da naka, bari kuma sarautarsa tă fi taka girma!’ Sarki kuwa ya rusuna, ya yi sujada a kan gadonsa
48 ydermere sagde han: Lovet være HERREN, Israels Gud, som i Dag har ladet en Mand sætte sig på min Trone, endnu medens jeg selv kan se det!"
ya ce, ‘Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bar idanuna suka ga magāji a kan kujerar sarautata a yau.’”
49 Da blev alle Adonijas Gæster skrækslagne og brød op og gik hver sin Vej;
A nan fa, dukan baƙin Adoniya suka taso da rawar jiki suka watse.
50 men Adonija frygtede for Salomo og ilede hen og greb fat om Alterets Horn.
Amma Adoniya, don tsoron Solomon, ya je ya kama ƙahon bagade ya riƙe.
51 Og man meldte Salomo: "Se, Adonija frygter for Kong Salomo, og se, han har grebet fat om Alterets Horn og siger: Kong Salomo skal først sværge mig til, at han ikke vil lade sin Træl slå ihjel med Sværd!"
Sa’ad da aka faɗa wa Solomon cewa, “Adoniya yana tsoron Sarki Solomon, kuma ya manne wa ƙahonin bagade. Yana cewa, ‘Bari Sarki Solomon yă rantse mini a yau cewa ba zai kashe bawansa da takobi ba.’”
52 Da sagde Salomo: "Dersom han opfører sig som en brav Mand, skal der ikke krummes et Hår på hans Hoved; men gribes han i noget ondt, skal han dø!"
Solomon ya amsa ya ce, “In ya nuna kansa mai biyayya, ba gashin kansa da zai fāɗi ƙasa; amma in aka same mugunta a cikinsa, zai mutu.”
53 Derpå sendte Kong Salomo Bud og lod ham hente ned fra Alteret; og han kom og kastede sig ned for Kong Salomo. Da sagde Salomo til ham: "Gå til dit Hjem!"
Sai Sarki Solomon ya aiki mutane, suka kuma sauko da shi daga bagade. Adoniya kuwa ya zo, ya rusuna wa Sarki Solomon, sai Solomon ya ce, “Tafi gidanka.”

< Første Kongebog 1 >