< Jób 9 >

1 Felelt Jób és mondta:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Valóban tudom, hogy így van; miképpen is igazulhat Istennel szemben a halandó?
“Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
3 Ha kíván pörölni vele, nem felel neki egyre sem ezer közül.
Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
4 Szívre bölcs, erőre hatalmas! Ki keményítette meg magát ellene és sértetlen maradt?
Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
5 A ki hegyeket mozdít el, s nem is tudják, a melyeket felforgatott haragjában;
Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
6 a ki megreszketteti a földet a helyéről, hogy oszlopai megrendülnek;
Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
7 a ki szól a napnak s nem ragyog fel, s a csillagokra pecsétet tesz;
Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
8 kiterjeszti az eget egymagában s lépdel a tenger magaslatain;
Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
9 teremti a gönczölszekerét, az óriont s a fiastyúkot meg a Délnek kamaráit;
Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
10 a ki nagyokat tesz kikutathatatlanúl, csodásokat, úgy hogy számuk sincsen:
Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
11 lám, elvonul mellettem s nem látom, elhalad s nem veszem észre;
Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
12 ha kit elragad, ki utasítaná vissza, ki szólna hozzá mit mívelsz?
Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
13 Isten nem fordítja el haragját, alatta legörnyedtek Ráháb segítői;
Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
14 hát még hogy felelnék én neki, választanám szavaimat vele szemben!
“Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
15 A ki, ha igazam volna, nem felelnék, az én bírámhoz könyörögnék.
Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
16 Ha szólítanám s felelne nekem, nem hinném, hogy figyel szavamra.
Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
17 A ki viharban rám rohan, hogy sebeimet sokasítsa ok nélkül.
Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
18 Nem enged lélegzetet vennem, hanem jóllakat keserűségekkel.
Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
19 Ha erőn fordul meg: íme a hatalmas, és ha ítéleten: ki idéz meg engem?
In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
20 Ha igazam volna, szájam ítélne el engem; gáncstalan vagyok, fonákká tesz engem.
Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
21 Gáncstalan vagyok, nem ismerem lelkemet, megvetem életemet!
“Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
22 Egyre megy; azért azt mondom: Gáncstalant és gonoszt semmisít ő meg.
Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
23 Ha hirtelen öl az ostor, az ártatlanok elcsüggedésén gúnyolódik.
Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
24 Az ország gonoszok kezébe adatott; bíráinak arczát eltakarja, ha ő nem, ugyan kicsoda?
Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
25 Napjaim pedig gyorsabbak voltak a futárnál, eliramodtak, nem láttak jót.
“Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
26 Tovavonultak akár gyékényhajók, mint sas lecsap az étkére.
Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
27 Ha azt mondtam, hadd felejtem el panaszomat, hagyom abba bánatos arczomat s hadd derülök fel:
‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
28 megfélemedtem mind a fájdalmaimtól, tudtam, hogy nem fogsz engem ártatlannak mondani.
duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
29 Nekem bűnösnek kell lennem – minek fáradozzam hát hiába?
Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
30 Ha megmosakodnám hóvízben s lúggal tisztítanám kezeimet:
Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
31 akkor a verembe mártanál engem, hogy megutálnának ruháim.
duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
32 Mert nem ember ő mint én, bogy felelhetnék neki, hogy együtt mehetnénk be ítéletre.
“Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
33 Nem létezik, ki közöttünk dönt, ki rá tenné kezét mindkettőnkre.
In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
34 Távolítsa el rólam vesszejét, s rettentése ne ijesszen engem:
wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
35 majd beszélnék s nem félnék tőle, mert nem olyan vagyok én magamban.
Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.

< Jób 9 >