< Yohanna 18 >

1 Bayan Yesu ya fadi wadannan maganganu, ya fita shi da almajiransa zuwa daya barayin kwarin Kidiron, inda wani lambu ya ke, ya kuma shiga da almajiransa.
Après avoir dit ces choses, Jésus s'en alla avec ses disciples au delà du torrent du Cédron; il y avait là un jardin dans lequel il entra, ainsi que ses disciples.
2 Yahuza ma wanda zai bashe shi ya san wurin, domin Yesu ya saba zuwa wurin da almajiransa.
Or, Judas, celui qui le trahissait, connaissait aussi cet endroit, parce que Jésus et ses disciples s'y étaient souvent réunis.
3 Yahuza kuwa, bayan ya dauko kungiyar soja daga manyan firistoci, da Farisawa, da 'yan majalisa, suka zo wurin, rike da fitilu, da cociloli, da makamai.
Judas, ayant donc pris la cohorte et les agents envoyés par les principaux sacrificateurs et les pharisiens, vint dans ce lieu avec des lanternes, des torches et des armes.
4 Sai Yesu, da ya san duk abinda ke faruwa da shi, yayiwo gaba, yace masu, ''Wa kuke nema''
Jésus, qui savait tout ce qui allait lui arriver, s'avança et leur dit: Qui cherchez-vous?
5 Suka amsa masa su ka ce, ''Yesu Banazare'' Yesu yace masu, Ni ne'' Yahuza kuma, wanda ya bashe shi, yana tsaye tare da sojojin.
Ils lui répondirent: Jésus de Nazareth. Jésus leur dit: C'est moi! Judas, qui le trahissait, se trouvait aussi avec eux.
6 Sa'adda ya ce masu, ''Ni ne'', suka koma da baya, suka fadi a kasa.
Dès que Jésus leur eut dit: C'est moi! — ils reculèrent et tombèrent à terre.
7 Ya sake tambayarsu kuma, ''Wa ku ke nema?'' su ka ce, ''Yesu Banazare.''
Il leur demanda encore une fois: Qui cherchez-vous? Ils répondirent: Jésus de Nazareth.
8 Yesu ya amsa, ''Ai, na gaya maku cewa, Ni ne. In kuwa ni ku ke nema, ku bar wadannan su tafi abinsu;''
Jésus reprit: Je vous ai dit que c'est moi; si donc c'est moi que vous cherchez, laissez aller ceux-ci.
9 Wannan kuwa domin maganar daya fada ta cika, ''Daga cikin wadanda ka ba ni, ko daya bai bace mani ba.''
Ainsi fut accomplie la parole qu'il avait dite: Je n'ai perdu aucun de ceux que tu m'as donnés.
10 Saminu Bitrus kuwa, da ya ke yana da takobi, ya zaro ya kai wa bawan babban firist sara, ya dauke masa kunnensa na dama, sunan bawan Malkus ne.
Alors Simon Pierre, qui avait une épée, la tira, frappa le serviteur du souverain sacrificateur, et lui coupa l'oreille droite. Ce serviteur s'appelait Malchus.
11 Yesu ya ce wa Bitrus, ''Mai da takobin ka kubenta. Ba zan sha kokon da Uba ya ba ni ba.'?
Mais Jésus dit à Pierre: Remets ton épée dans le fourreau: ne boirai-je pas la coupe que le Père m'a donnée à boire?
12 Sai sojojin da hafsan, da 'yan majalisar Yahudawa, suka kama Yesu, suka daure shi.
La cohorte, le tribun et les agents des Juifs, se saisirent alors de Jésus et le chargèrent de liens.
13 Da fari suka tafi da shi wurin Hanana, don shi surukin Kayafa ne, wanda ya ke shi ne babban firist a shekaran nan.
Ils l'emmenèrent d'abord chez Anne; car il était le beau-père de Caïphe, qui était souverain sacrificateur cette année-là.
14 Kayafa kuma shi ne ya ba Yahudawa shawara, cewa ya fiye masu mutum daya ya mutu domin mutane.
Or, Caïphe était celui qui avait donné ce conseil aux Juifs: Il vaut mieux qu'un seul homme meure pour le peuple.
15 Saminu bitrus ya bi bayan Yesu, haka kuma wani almajirin yayi. Almajirin nan kuwa sananne ne ga babban firist, sai ya shiga har farfajiyar babban firist din tara da Yesu;
Simon Pierre, avec un autre disciple, suivait Jésus. Cet autre disciple était connu du souverain sacrificateur; il entra donc avec Jésus dans la cour du souverain sacrificateur.
16 Amma bitrus kuwa ya tsaya a bakin kofa daga waje. Sai daya almajirin da ya ke sananne ga babban firist ya fita, yayi magana da macen da ta ke tsaron kofar, sa'an nan ya shigo da Bitrus.
Mais Pierre se tenait dehors, près de la porte. L'autre disciple, qui était connu du souverain sacrificateur, sortit, parla à la portière, et fit entrer Pierre.
17 Sai yarinyar mai tsaron kofar ta ce wa Bitrus, ''kai ma ba kana cikin almajiran mutumin nan ba?'' Yace ''bani ba.''
Alors cette servante, qui gardait la porte, dit à Pierre: N'es-tu pas, toi aussi, des disciples de cet homme? Il répondit: Je n'en suis pas.
18 To, barorin da dogaran Haikali suna tsaye a wurin, sun kuwa hura wutar gawayi, suna jin dumi, gama ana sanyi. Bitrus ma yana tsaye tare da su yana jin dumin.
Les serviteurs et les agents se tenaient là auprès d'un feu qu'ils avaient allumé, parce qu'il faisait froid, et ils se chauffaient. Pierre se tenait avec eux, et il se chauffait aussi.
19 babban firist ya tambayi Yesu game da almajiransa da koyarwarsa kuma.
Le souverain sacrificateur interrogea donc Jésus sur ses disciples et sur sa doctrine.
20 Yesu ya amsa masa, Ai, na yi wa duniya magana a bayyane. Na kuma sha koyarwa a majami'u da Haikali in da Yahudawa duka sukan taru. Ban fadi komai a boye ba.
Jésus lui répondit: J'ai parlé ouvertement au monde; j'ai toujours enseigné dans la synagogue et dans le temple, où se rassemblent tous les Juifs, et je n'ai rien dit en secret.
21 Don me kake tambaya ta? Ka tambayi wadanda suka saurare ni a kan abinda na fada, ai, sun san abinda na fada.
Pourquoi m'interroges-tu? Demande à ceux qui m'ont entendu ce que je leur ai dit; ceux-là savent ce que j'ai dit.
22 Sa'adda Yesu ya fadi wannan, wani daga cikin 'yan majalisar da ke tsaye a wurin ya nushi Yesu, yace, ''Kana amsa wa babban firist haka.''
Comme il parlait ainsi, un des agents qui étaient présents donna un soufflet à Jésus, en disant: Est-ce ainsi que tu réponds au souverain sacrificateur?
23 Yesu ya amsa masa yace, ''Idan na fadi mugun abu to, ka bada shaida kan hakan. In kuwa dai dai na fada, to, dan me za ka nushe ni?''
Jésus lui répondit: Si j'ai mal parlé, fais voir ce que j'ai dit de mal; mais si j'ai bien parlé, pourquoi me frappes-tu?
24 Sai Hanana ya aika daYesu a daure wurin Kayafa, babban firist.
Alors Anne l'envoya, chargé de liens, à Caïphe, le souverain sacrificateur.
25 To Saminu Bitrus yana tsaye yana jin dumin. Mutanen kuwa suka ce masa, ''Anya kai ma ba cikin almajiransa ka ke ba?'' Sai yayi musu yace, ''A'a, ba na ciki.''
Cependant, Simon Pierre se tenait là et se chauffait; et on lui dit: N'es-tu pas, toi aussi, de ses disciples? Il le nia et répondit: Je n'en suis pas.
26 Sai wani daga cikin bayin babban firist, wato dan'uwan wanda Bitrus ya fillewa kunne, yace, ''Ashe, ban gan ka tare da shi a lambun ba?
L'un des serviteurs du souverain sacrificateur, parent de celui à qui Pierre avait coupé l'oreille, lui dit: Ne t'ai-je pas vu dans le jardin avec lui?
27 Bitrus ya sake yin musu, nan da nan kuwa zakara yayi cara.
Pierre nia une fois encore; et aussitôt le coq chanta.
28 Daga wurin Kayafa kuma suka kai Yesu fadar Gwamna. Da asuba ne kuwa, su kansu ba su shiga fadar Gwamnan ba, wai don kada su kazantu su kasa cin jibin Ketarewa.
Ils emmenèrent ensuite Jésus de chez Caïphe au prétoire; c'était le matin. Mais ils n'entrèrent pas eux-mêmes dans le prétoire, afin de ne point se souiller et de pouvoir manger la Pâque.
29 Sai bilatus fa ya fita zuwa wurinsu, yace, 'Wane zargi ku ke kawowa akan mutumin nan?'
Pilate sortit donc, alla vers eux et leur dit: Quelle accusation portez-vous contre cet homme?
30 ''Sai suka amsa suka ce, ''idan da mutumin nan bai yi mugun abu ba, me zai sa mu yi kararsa a wurin ka''
Ils lui répondirent: Si ce n'était pas un malfaiteur, nous ne te l'aurions pas livré.
31 bilatus yace masu, ''Ku tafi da shi da kan ku mana, ku hukunta shi bisa ga shari'arku!'' Sai Yahudawa su kace masa, ''Ai, ba mu da ikon zartar da hukuncin kisa akan kowa.''
Alors Pilate leur dit: Prenez-le vous-mêmes et jugez-le selon votre loi. Les juifs lui dirent: Il ne nous est pas permis de faire mourir personne.
32 Sun fadi Wannan ne don a cika maganar da Yesu yayi, wadda ta kwatanta irin mutuwar da zai yi.
C'était afin que fût accompli ce que Jésus avait dit, pour indiquer de quelle mort il devait mourir.
33 Sai bilatus ya sake shiga cikin fadar Gwamnan, ya kira Yesu ya ce masa, ''kai sarkin Yahudawa ne?''
Alors Pilate rentra dans le prétoire, et, ayant fait venir Jésus, il lui dit: C'est toi qui es le roi des Juifs?
34 Yesu ya amsa, '' wannan fadarka ce, ko kuwa wadansu ne suka ce da ni haka a wurinka?''
Jésus répondit: Dis-tu cela de ton propre mouvement, ou d'autres te l'ont-ils dit de moi?
35 Bilatus ya amsa “Ni ba Bayahude bane, ko kuwa?'' Ai, jama'arka ne da manyan firistoci suka bashe ka gareni. ''Me ka yi?''
Pilate répondit; Suis-je Juif? Ta nation et les principaux sacrificateurs t'ont livré à moi; qu'as-tu fait?
36 Yesu ya amsa, ''Mulkina ba na duniya nan ba ne. Da mulkina na duniyan nan ne da barorina za su yi yaki kada a bashe ni ga Yahudawa. To, mulkina ba daga nan ya ke ba.''
Jésus répondit: Mon règne n'est pas de ce monde. Si mon règne était de ce monde, mes gens combattraient, pour que je ne fusse pas livré aux Juifs; mais maintenant mon règne n'est pas d'ici-bas.
37 Sai Bilatus yace masa, ''Wato ashe, sarki ne kai?'' Yesu ya amsa, ''Yadda ka fada, ni sarki ne. Domin wannan dalili aka haife ni, domin kuma wannan dalili na zo cikin duniya, don in bada shaida game da gaskiya. Kowane mai kaunar gaskiya kuma yakan saurari muryata.''
Alors Pilate lui dit: Tu es donc roi? Jésus répondit: Tu le dis, je suis roi. Voici pourquoi je suis né et pourquoi je suis venu dans le monde: c'est pour rendre témoignage à la vérité. Quiconque est pour la vérité écoute ma voix.
38 Bilatus yace masa, ''Menene gaskiya?'' Bayan da ya fadi haka, ya sake fitowa wurin Yahudawa, yace masu, ''Ni kam, ban sami mutumin nan da wani laifi ba.
Pilate lui dit: Qu'est-ce que la vérité? Quand Pilate eut dit cela, il sortit de nouveau pour aller vers les Juifs, et il leur dit: Je ne trouve aucun crime en lui.
39 Amma dai kuna da wata al'ada, in Idin Ketarewa ya yi, na kan sakar maku mutum daya. To, kuna so in sakar maku sarkin Yahudawa?''
Mais vous avez une coutume, c'est que je vous relâche quelqu'un à la fête de Pâque; voulez-vous donc que je vous relâche le roi des Juifs?
40 Sai suka sake daukar kururuwa suna cewa, ''A; a, ba wannan mutum ba, sai dai Barabbas.'' Barabbas din nan kuwa dan fashi ne.
Alors ils s'écrièrent de nouveau: Non! Pas lui, mais Barabbas! Or, Barabbas était un brigand.

< Yohanna 18 >