< Yohanna 17 >

1 Da Yesu ya fadi wandannan abubuwa, sai ya tada idanunsa sama ya ce, ya Uba, sa'a ta zo; ka daukaka Danka, domin Dan shi ya daukaka ka,
Jésus parla ainsi; puis, levant les yeux au ciel, il dit: Père, l'heure est venue; glorifie ton Fils, afin que ton Fils te glorifie,
2 kamar yadda ka ba shi iko akan dukkan 'yan adam, ya ba da rai madawwami ga duk wanda ka ba shi. (aiōnios g166)
et que, par le pouvoir que tu lui as donné sur toute créature, il donne la vie éternelle à tous ceux que tu lui as donnés. (aiōnios g166)
3 Wannan ne rai madawwami: wato su san ka, Allah makadaici na gaskiya, da shi kuma wanda ka aiko, Yesu Almasihu. (aiōnios g166)
Or c'est ici la vie éternelle, qu'ils te connaissent, toi, le seul vrai Dieu, et celui que tu as envoyé, Jésus-Christ. (aiōnios g166)
4 Na daukaka ka a duniya, na gama aikin da ka ba ni in yi.
Je t'ai glorifié sur la terre; j'ai achevé l'oeuvre que tu m'avais donnée à faire.
5 Yanzu, ya Uba, ka daukaka ni tare da kai da daukaka wadda ni ke da ita tare da kai tun kafin duniya ta kasanci.
Et maintenant, toi, Père, glorifie-moi auprès de toi-même de la gloire que j'avais auprès de toi, avant que le monde fût.
6 Na bayyana sunanka ga mutunen da ka ba ni acikin duniya. Na ka suke, ka ba ni su, sun kuwa kiyaye maganarka.
J'ai manifesté ton nom aux hommes que tu m'as donnés du milieu du monde; ils étaient à toi! et tu me les as donnés, et ils ont gardé ta parole.
7 Yanzu kuwa sun san duk iyakar abinda ka ba ni daga gare ka yake,
Maintenant ils ont reconnu que tout ce que tu m'as donné vient de toi.
8 don kuwa maganganun da ka fada mani. Na fada masu, sun kuma karba, sun sani kuwa hakika na fito daga gareka ne, kuma sun gaskata kai ne ka aiko ni.
Car je leur ai donné les paroles que tu m'as données, et ils les ont reçues; ils ont vraiment reconnu que je suis venu de toi, et ils ont cru que c'est toi qui m'as envoyé.
9 Ina yi masu addu'a. Ba domin duniya ni ke yin addu'a ba, amma domin wadanda ka bani gama na ka ne.
Je prie pour eux; je ne prie pas pour le monde, mais pour ceux que tu m'as donnés, parce qu'ils sont à toi.
10 Gama dukan abinda ke nawa na ka ne, naka kuwa nawa ne, an kuma daukaka ni a cikinsu.
Et tout ce qui est à moi est à toi, et ce qui est à toi est à moi, et je suis glorifié en eux.
11 Ba na cikin duniya kuma, amma wadannan mutane suna cikin duniya, ni kuwa ina zuwa wurin ka. Ya Uba mai Tsarki, ka adanasu cikin sunanka da ka ba ni domin su zama daya, kamar dai yadda muke daya.
Je ne suis plus dans le monde, mais eux sont dans le monde, et moi je vais auprès de toi. Père saint, garde-les! Qu'ils soient fidèles à ton nom, que tu m'as chargé de faire connaître, afin qu'ils soient un comme nous.
12 Lokacin da ina tare da su, na adanasu acikin sunanka da ka ba ni. Na kiyaye su, kuma ko daya kuwa daga cikinsu ba ya bace ba, sai dai dan hallakar nan, domin Nassi ya cika.
Pendant que j'étais avec eux, je les gardais, et ils étaient fidèles à ton nom que tu m'as chargé de faire connaître. Je les ai préservés, et aucun d'eux ne s'est perdu, sinon le fils de perdition, afin que l'Écriture fût accomplie.
13 Amma yanzu ina zuwa wurinka, Ina fadar wadannan abubuwa tun ina duniya, domin farin cikina ya zama cikakke a zukatansu.
Mais maintenant je vais auprès de toi, et je dis ces choses, étant encore dans le monde, afin qu'ils aient en eux la plénitude de ma joie.
14 Na ba su maganarka, kuma duniya ta tsane su domin su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ba na duniya ba ne.
Je leur ai donné ta Parole, et le monde les a haïs, parce qu'ils ne sont pas du monde, comme je ne suis pas du monde.
15 Ba ina roko ka dauke su daga cikin duniya ba, amma domin ka tsare su daga mugun nan.
Je ne te prie pas de les ôter du monde, mais de les préserver du mal.
16 Su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ba na duniya ba ne.
Ils ne sont pas du monde, comme je ne suis pas du monde.
17 Ka kebe su domin kanka cikin gaskiya. maganarka gaskiya ce.
Sanctifie-les par la vérité; ta Parole est la vérité.
18 Kamar dai yadda ka aiko ni cikin duniya, haka kuma na aike su cikin duniya.
Comme tu m'as envoyé dans le monde, je les ai aussi envoyés dans le monde.
19 Na kebe kaina gareka sabili da su, domin su ma kansu a kebe su gareka cikin gaskiya.
Et je me sanctifie moi-même pour eux, afin qu'eux aussi soient sanctifiés par la vérité.
20 Ina addu'a ba domin wadannan kadai ba, amma har da wadanda zasu gaskata da ni ta wurin maganarsu,
Ce n'est pas seulement pour eux que je prie, mais aussi pour ceux qui croiront en moi par leur parole,
21 Domin su zama daya dukansu, kamar yadda kai, ya Uba, ka ke ciki na, ni kuma na ke cikin ka. Ina roko suma su kasance a cikinmu, domin duniya ta gaskata cewa ka aiko ni
afin que tous soient un, comme toi. Père, tu es en moi, et moi en toi; afin qu'eux aussi soient en nous, pour que le monde croie que c'est toi qui m'as envoyé.
22 Daukakar da ka bani, ita nake basu, domin su zama daya, kamar yadda mu ke daya;
Je leur ai donné la gloire que tu m'as donnée, afin qu'ils soient un, comme nous sommes un:
23 ni a cikinsu, kai kuma a ciki na. Domin su kammalu cikin zama daya, domin duniya ta sani cewa ka aiko ni, kuma ka kaunace su, kamar yadda ka kaunace ni.
moi en eux, et toi en moi, afin qu'ils soient parfaits dans l'unité, et que le monde connaisse que c'est toi qui m'as envoyé, et que tu les as aimés comme tu m'as aimé.
24 Ya Uba, ina so wadanda ka ba ni, su ma su kasance tare da ni inda nake, domin su dubi daukakata da ka yi mani. Domin ka kaunace ni tun kafin halittar duniya.
Père, je veux que là où je suis, ceux que tu m'as donnés y soient aussi avec moi, afin qu'ils contemplent ma gloire, la gloire que tu m'as donnée, parce que tu m'as aimé avant la création du monde.
25 Ya Uba mai adalci, duniya kam, ba ta sanka ba, amma ni na sanka; kuma wadannan sun sani kai ne ka aiko ni.
Père juste, le monde ne t'a pas connu; mais moi, je t'ai connu, et ceux-ci ont reconnu que c'est toi qui m'as envoyé.
26 Na sanar masu da sunanka, zan kuma sanar da shi domin kaunar da ka yi mani ta kasance a cikinsu, ni kuma in kasance a cikinsu,
Je leur ai fait connaître ton nom, et je le leur ferai connaître, afin que l'amour dont tu m'as aimé soit en eux, et que je sois moi-même en eux.

< Yohanna 17 >