< Yoshuwa 7 >

1 Amma Isra’ilawa ba su yi aminci game da kayan da aka hallaka ba; Akan ɗan Karmi, ɗan Zabdi, ɗan Zera, na kabilan Yahuda ya kwashi waɗansu abubuwa, saboda haka fushin Ubangiji ya sauka a kan Isra’ilawa.
Or, les enfants d’Israël transgressèrent le commandement, et s’approprièrent de l’anathème; car Achan, fils de Charmi, fils de Zabdi, fils de Zaré, de la tribu de Juda, prit quelque chose de l’anathème, et le Seigneur fut irrité contre les enfants d’Israël.
2 Sai Yoshuwa ya aika mutane daga Yeriko zuwa Ai kusa da Bet-Awen gabas da Betel, ya ce musu, “Ku je ku leƙo ku ga yadda yankin yake.” Sai mutanen suka je suka leƙo asirin ƙasar Ai.
Et lorsque Josué envoya de Jéricho des hommes contre Haï, qui est près de Béthaven, au côté oriental de la ville de Béthel, il leur dit: Montez, et explorez la terre. Ceux-ci, accomplissant ses ordres, explorèrent Haï.
3 Da suka dawo wurin Yoshuwa suka ce, “Ba lalle dukan jama’a su je yaƙi da Ai ba, ka aika mutum dubu biyu ko dubu uku su je su ciwo ƙasar da yaƙi, ba sai ka dami mutane duka ba, gama mutanen wurin kaɗan ne.”
Et, revenus, ils lui dirent: Que tout le peuple ne monte point, mais que deux ou trois mille hommes aillent, et détruisent la ville: pourquoi tout le peuple se fatiguerait-il en vain contre des ennemis très peu nombreux?
4 Saboda haka sai kimanin mutum duba uku suka haura; amma mutanen Ai suka fatattake su,
Il monta donc trois mille combattants, qui aussitôt tournant le dos,
5 suka kashe Isra’ilawa wajen mutum talatin da shida, suka fafari Isra’ilawa tun daga bakin ƙofar birnin har zuwa wurin da ake fasa duwatsu. Suka karkashe su a gangare. Wannan ya sa zuciyar Isra’ilawa ta narke suka zama kamar ruwa.
Furent battus par les habitants de la ville de Haï; et il tomba trente-six hommes d’entre eux; et les ennemis les poursuivirent depuis la porte jusqu’à Sabarim, et ils les taillèrent en pièces, pendant qu’ils fuyaient à travers les versants; et le cœur du peuple fut saisi d’une grande crainte et s’écoula comme l’eau.
6 Sai Yoshuwa ya yaga tufafinsa ya fāɗi rubda ciki a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, yana can har yamma. Dattawan Isra’ila ma suka yi haka, suka zuba toka a kawunansu.
Mais Josué déchira ses vêtements et tomba, incliné vers la terre devant l’arche du Seigneur jusqu’au soir, tant lui que tous les anciens d’Israël; et ils mirent de la poussière sur leurs têtes,
7 Yoshuwa kuma ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, me ya sa ka sa mutanen nan suka ƙetare Urdun don ka bari mu shiga hannun Amoriyawa su hallaka mu? Kila da mun haƙura mun zauna a ɗaya gefen Urdun da ya fi mana!
Et Josué dit: Hélas! Seigneur Dieu, pourquoi avez-vous voulu que ce peuple passât le fleuve du Jourdain, pour nous livrer aux mains de l’Amorrhéen et nous perdre? Oh! que ne sommes-nous demeurés au-delà du Jourdain comme nous avions commencé!
8 Ya Ubangiji me zan ce, yanzu da abokan gāban Isra’ilawa suka ci ƙarfinsu?
Mon Seigneur Dieu, que dirai-je, voyant Israël tournant le dos devant ses ennemis?
9 Yanzu Kan’aniyawa da sauran jama’a za su ji, za su zo su kewaye mu su share sunanmu daga duniya. To, yanzu me za ka yi don girman sunanka?”
Les Chananéens rapprendront et tous les habitants de la terre, et réunis ensemble, ils nous envelopperont, et ils effaceront notre nom de la terre; et que ferez-vous pour votre grand nom?
10 Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka tashi! Me kake yi kwance rubda ciki?
Et le Seigneur dit à Josué: Lève-toi et pourquoi es-tu couché la face contre terre?
11 Isra’ilawa sun yi zunubi, sun karya sharaɗin da na yi musu. Sun ɗauki waɗansu abubuwan da aka keɓe; sun yi sata, sun yi ƙarya, sun ɓoye su cikin kayansu.
Israël a péché et il a transgressé mon alliance; ils ont pris quelque chose de l’anathème; ils l’ont dérobé, ils ont menti, et ils l’ont caché parmi leurs bagages.
12 Shi ne ya sa Isra’ilawa suka kāsa yin tsayayya da abokan gābansu; suka juya suka gudu domin za a hallaka su. Ba zan sāke kasancewa tare da ku ba sai in kun hallaka duk abin da aka keɓe don hallaka.
Israël ne pourra pas tenir devant ses ennemis, et il les fuira, parce qu’il s’est souillé par l’anathème: je ne serai plus avec vous, jusqu’à ce que vous détruisiez celui qui est coupable de ce crime.
13 “Tashi, ka je ka tsarkake mutane. Ka ce musu su tsarkake kansu, su yi shiri domin gobe; gama ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, a cikinku akwai abubuwan da aka keɓe, ya Isra’ilawa. Ba za ku iya yin tsayayya da abokan gābanku ba sai in kun rabu da abubuwan nan da aka haramta.
Lève-toi, sanctifie le peuple, et dis-leur: Sanctifiez-vous pour demain; car voici ce que dit le Seigneur Dieu d’Israël: L’anathème est au milieu de toi, Israël; tu ne pourras tenir devant tes ennemis, jusqu’à ce que disparaisse d’au milieu de toi celui qui s’est souillé de ce crime.
14 “‘Da safe ku zo kabila-kabila. Kabilar da Ubangiji ya ware, za tă zo gaba gida-gida; gidan da Ubangiji ya ware, za su zo gaba iyali-iyali. Iyalin kuma da Ubangiji ya ware, za su zo gaba mutum bayan mutum.
Vous viendrez dès le matin, chacun dans votre tribu; et quelle que soit la tribu que le sort désigne, elle viendra divisée en ses familles, la famille en maisons, et la maison en hommes.
15 Mutumin da aka same shi da haramtattun abubuwan kuwa za a ƙone shi, duk da mallakarsa domin ya karya sharaɗin da Ubangiji ya yi muku, ya yi abin kunya a Isra’ila!’”
Et quiconque aura été surpris dans ce crime, sera consumé par le feu avec tout ce qui lui appartient, parce qu’il a transgressé l’alliance du Seigneur, et qu’il a commis un forfait dans Israël.
16 Kashegari da sassafe Yoshuwa ya sa Isra’ilawa suka fito kabila-kabila, aka ware kabilar Yahuda.
C’est pourquoi Josué, se levant dès le matin, fit venir Israël selon ses tribus, et la tribu de Juda fut trouvée coupable.
17 Gidan Yahuda suka zo gaba, sai aka ware gidan Zera, aka sa suka fito iyali-iyali, sai aka ware Zabdi.
Et lorsqu’elle se fut présentée selon ses familles, la famille de Zaré fut trouvée coupable. Et Josué la présentant aussi par maisons, il trouva celle de Zabdi coupable.
18 Yoshuwa kuwa ya sa iyalin Zabdi suka fito mutum-mutum, sai kuwa aka ware Akan ɗan Karmi, ɗan Zimri, ɗan Zera na kabilar Yahuda.
Et divisant la maison de Zabdi par chaque homme, il trouva coupable Achan, fils de Charmé, fils de Zabdi, fils de Zaré, de la tribu de Juda.
19 Sai Yoshuwa ya ce wa Akan, “Ɗana, sai ka ba Ubangiji, Allah na Isra’ila ɗaukaka, ka yi masa yabo. Ka gaya mini abin da ka yi; kada ka ɓoye mini.”
Alors Josué dit à Achan: Mon fils, rends gloire au Seigneur Dieu d’Israël; confesse et déclare-moi ce que tu as fait; ne le cache pas,
20 Akan kuwa ya amsa ya ce, “Gaskiya ne! Na yi wa Ubangiji, Allah na Isra’ila zunubi. Ga abin da na yi.
Et Achan répondit à Josué, et lui dit: C’est vraiment moi qui ai péché contre le Seigneur Dieu d’Israël; et c’est absolument ainsi que j’ai agi:
21 A cikin ganimar, na ga doguwar riga mai kyau irin ta Babilon, da shekel ɗari biyu na azurfa, da kuma sandan zinariya mai nauyin shekel hamsin, sai raina ya so su, na kuwa kwashe su. Na tona rami a cikin ƙasa a tentina; na ɓoye.”
J’ai vu parmi les dépouilles un manteau d’écarlate, fort beau, et deux cents sicles d’argent, et une règle d’or de cinquante sicles; et, les convoitant, je les pris et les cachai dans la terre au milieu de ma tente; mais l’argent, je le couvris de terre dans une fosse,
22 Sai Yoshuwa ya aiki’yan aika suka tafi da gudu zuwa tenti ɗin, haka kuwa suka same su a ɓoye a tentinsa, da azurfa a ƙarƙashi.
Josué envoya donc des serviteurs, qui, courant à la tente d’Achan, trouvèrent toutes les choses cachées dans le même lieu, et l’argent aussi.
23 Suka kwashe kayan daga tenti ɗin suka kawo wa Yoshuwa da sauran Isra’ilawa, suka baza su a gaban Ubangiji.
Et les enlevant de la tente, ils les apportèrent à Josué et à tous les enfants d’Israël, et les jetèrent devant le Seigneur.
24 Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka ɗauki Akan ɗan Zera, da azurfar, doguwar rigar, sandan zinariya,’ya’yansa maza da mata, shanunsa, jakuna da tumaki, tentinsa da duk abin da yake da shi, suka kai su Kwarin Akor.
Or, Josué et tout Israël avec lui prenant Achan, fils de Zaré, l’argent, le manteau et la règle, d’or; ses fils aussi et ses filles, ses bœufs, ses ânes et ses brebis, sa tente elle-même et tous ses meubles, les conduisirent dans la vallée d’Achor,
25 Yoshuwa ya ce, “Me ya sa ka jawo mana wahala haka? Ubangiji zai kawo maka wahala kai ma a yau.” Sai dukan Isra’ilawa suka jajjefe shi, bayan da suka gama jifarsa sai suka ƙone sauran.
Où Josué dit: Parce que tu nous a troublés, que le Seigneur te trouble en ce jour-ci. Et tout Israël le lapida, et tout ce qui était à lui, fut consumé par feu.
26 Suka tara manyan duwatsu a kan Akan, tarin duwatsun na nan a can har wa yau. Sa’an nan Ubangiji ya huce daga fushinsa mai zafi. Saboda haka ake kiran wurin Kwarin Akor.
Et ils amassèrent sur lui un grand monceau de pierres, qui est demeuré jusqu’au présent jour. Ainsi fut détournée deux la fureur du Seigneur. Et ce lieu a été appelé du nom de vallée d’Achor jusqu’aujourd’hui.

< Yoshuwa 7 >