< 1 Sama’ila 2 >

1 Sai Hannatu ta yi addu’a ta ce, “Zuciyata tana farin ciki a cikin Ubangiji; a cikin Ubangiji an sa ina jin daɗi ƙwarai. Na buɗe bakina na yi wa abokan gābana dariya. Kai! Ina murna domin ka cece ni!
Mon âme a tressailli d’allégresse dans le Seigneur, et ma force a été exaltée en mon Dieu; ma bouche s’est dilatée sur mes ennemis, parce que je me suis réjouie dans votre assistance.
2 “Babu wani mai tsarki kamar Ubangiji babu wani, in ban da kai; babu wani dutse kamar Allahnmu.
Il n’est pas de saint comme est le Seigneur; car il n’en est pas d’autre en dehors de vous, et il n’est pas de fort comme notre Dieu.
3 “Ka daina maganganu na girman kai ka kuma daina faɗin kalmomin ɗaga kai; gama Ubangiji Allah ne masani daga gare shi kuma ana auna ayyuka.
Ne multipliez point des paroles hautaines en vous glorifiant; que les anciens discours s’éloignent de votre bouche, parce que le Seigneur est le Dieu des sciences, et que c’est pour lui que sont préparées les pensées.
4 “An kakkarya bakkuna masu yaƙi, amma su da ka raunana an ba su makaman ƙarfi.
L’arc des forts a été vaincu, et les faibles ont été ceints de force.
5 Waɗanda a dā suna da abinci sosai; yanzu suna ƙodago saboda abinci, masu fama da yunwa kuwa sun daina jin yunwa. Ita da take bakararriya, ta haifi’ya’ya bakwai amma ita da tana da’ya’ya da yawa, ta zama mai baƙin ciki.
Ceux qui auparavant regorgeaient se sont loués pour du pain; et les affamés ont été rassasiés, jusque là qu’une femme stérile a enfanté un grand nombre d’enfants, et que celle qui en avait beaucoup est tombée dans la langueur.
6 “Ubangiji ne ke kawo mutuwa, yă kuma rayar yana kai ga kabari, yă kuma tā da. (Sheol h7585)
C’est le Seigneur qui fait mourir et qui fait vivre, qui conduit aux enfers et qui en ramène. (Sheol h7585)
7 Ubangiji ne yakan aika da talauci da kuma dukiya; yakan ƙasƙantar yă kuma ɗaukaka.
C’est le Seigneur qui fait le pauvre et qui enrichit, qui abaisse et qui relève.
8 Yakan tā da matalauci daga ƙura, yă kuma ɗaga mai bukata daga tarin toka; yă zaunar da su tare da’ya’yan sarki; yă kuma sa su gāji mulki na ɗaukaka. “Harsashin duniya na Ubangiji ne; a bisansu ne ya kafa duniya.
Il fait sortir de la poussière l’indigent, et du fumier il élève le pauvre, afin qu’il s’asseye avec les princes, et qu’il occupe un trône de gloire; car au Seigneur appartiennent les pôles de la terre, et il a posé sur eux l’univers.
9 Zai kiyaye ƙafafun masu tsarki, amma mugaye za su lalace cikin duhu. “Ba bisa ga ƙarfi mutum ba ne mutum ke nasara;
Il gardera les pieds de ses saints, et les impies se tairont dans les ténèbres, parce que ce n’est point par sa propre force que l’homme se fortifiera.
10 waɗanda suke gāba da Ubangiji za su hallaka. Zai yi musu tsawa daga sama, Ubangiji zai hukunta dukan duniya. “Zai ba wa sarkinsa ƙarfi, yă kuma ɗaukaka shafaffensa.”
C’est le Seigneur que redouteront ses ennemis, et c’est sur eux-mêmes qu’il tonnera dans les cieux. Le Seigneur jugera les confins de la terre, il donnera l’empire à son roi, et il élèvera la puissance de son christ.
11 Sa’an nan, Elkana ya koma gida a Rama amma yaron ya yi hidima a gaban Ubangiji a ƙarƙashin Eli firist.
Après cela, Elcana s’en alla à Ramatha dans sa maison; mais l’enfant servait en la présence du Seigneur et devant Héli, le prêtre.
12 ’Ya’yan Eli firist, mutane ne masu mugunta. Ba su ɗauki Ubangiji a bakin kome ba.
Or, les fils d’Héli étaient des fils de Bélial, ne connaissant point le Seigneur,
13 Al’ada ce ga firistoci da mutane cewa in wani ya miƙa hadaya, yayinda nama yake kan wuta, bawan firist zai zo da babban cokali mai yatsu,
Ni le devoir des prêtres envers le peuple; car quiconque avait immolé une victime, le serviteur du prêtre venait, tandis que les chairs cuisaient, et il avait la fourchette à trois dents en sa main,
14 zai soka cokali mai yatsun a tukunyar, ko butar da ake dafan naman. Duk abin da cokali mai yatsun ya cako daga tukunyar, ya zama na firist. Haka aka yi ta yi wa Isra’ilawan da suka zo miƙa hadaya a Shilo.
Et il la plongeait dans la chaudière, ou dans le chaudron, ou dans la marmite, ou dans le pot; et tout ce qu’enlevait la fourchette, le prêtre l’emportait pour lui. C’est ainsi qu’ils faisaient à tous ceux d’Israël qui venaient à Silo.
15 Tun ma kafin a ƙona kitse, bawan firist yakan zo yă ce wa mutumin da yake miƙa hadaya, “Ka ba wa firist nama domin yă gasa, ba zai karɓi dafaffen nama daga wurinka ba, sai ɗanye.”
Même avant qu’on brûlât la graisse, le serviteur du prêtre venait, et disait à celui qui immolait: Donne-moi de la chair, afin que je la fasse cuire pour le prêtre; car je ne recevrai pas de toi de la chair cuite, mais de la crue.
16 In kuwa mutumin ya ce masa, “Bari kitse yă ƙone tukuna, sa’an nan ka ɗiba duk abin da kake so.” Sai bawan yă ce masa, “A’a, ka ba ni yanzu, in ka ƙi kuwa zan ɗiba ƙarfi da yaji.”
Et celui qui immolait lui disait: Que la graisse d’abord soit brûlée aujourd’hui, selon l’usage, et prenez pour vous tout autant qu’en désire votre âme. Et celui-ci, répondant, lui disait: Point du tout; car tu m’en donneras maintenant, ou bien j’en prendrai de force.
17 Wannan zunubin samarin ya yi muni ƙwarai a gaban Ubangiji, domin sun wulaƙanta hadayar Ubangiji, ƙwarai da gaske.
Ainsi le péché des enfants d’Héli était très grand devant le Seigneur, puisqu’ils détournaient les hommes des sacrifices du Seigneur.
18 Amma yaron nan Sama’ila, yana hidima a gaban Ubangiji yana sanye da efod na lilin.
Cependant devant la face du Seigneur servait Samuel, enfant revêtu d’un éphod de lin.
19 Kowace shekara mahaifiyarsa takan ɗinka’yar taguwa ta kai masa sa’ad da ita da mijinta suka je miƙa hadaya ta shekara.
Et sa mère lui faisait une petite tunique qu’elle lui apportait aux jours prescrits, montant avec son mari, pour immoler l’hostie solennelle.
20 Eli yakan sa wa Elkana da matarsa albarka, yă ce, Ubangiji yă ba ka waɗansu’ya’ya ta wurin matan nan, maimakon wanda ta roƙa daga Ubangiji, ta kuma ba da shi ga Ubangiji. Bayan haka sai su koma gida.
Et Héli bénit Elcana et sa femme et dit à Elcana: Que le Seigneur te rende une postérité par cette femme pour l’intérêt de ce que tu as prêté au Seigneur. Et ils s’en allèrent dans leur demeure.
21 Hannatu kuwa ta sami alfarma daga Ubangiji. Ta yi ciki. Ana cikin haka Sama’ila kuwa sai girma yake ta yi a gaban Ubangiji.
Le Seigneur visita donc Anne, et elle conçut et enfanta trois fils et deux filles, et l’enfant Samuel devint grand devant le Seigneur.
22 To, Eli kuwa ya tsufa ƙwarai, yana kuma jin labari duk abin da’ya’yansa suke yi wa dukan Isra’ila, da yadda suke lalata da matan da suke hidima a bakin ƙofar Tentin Sujada.
Or, Héli était fort vieux; et il apprit tout ce que faisaient ses fils à tout Israël, et comment ils dormaient avec les femmes qui veillaient à la porte du tabernacle,
23 Saboda haka ya ce musu, “Don me kuke yin waɗannan abubuwa? Na sami labari daga wurin mutane a kan duk ayyukan muguntanku.
Et il leur demanda: Pourquoi faites-vous des choses de cette nature, choses très mauvaises, que j’apprends moi-même de tout le peuple?
24 A’a,’ya’yana ba labari mai kyau nake ji cikin mutanen Ubangiji ba.
Cessez, mes enfants; car il n’est pas honorable le bruit qui est parvenu jusqu’à moi, que vous faites transgresser le peuple du Seigneur.
25 In mutum ya yi wa wani laifi Allah yakan kāre shi; amma in mutum ya yi wa Ubangiji zunubi wa zai kāre shi?” Duk da haka,’ya’yansa ba su kula da gargaɗin mahaifinsu ba, domin nufin Ubangiji ne yă hallaka su.
Si un homme pèche contre un homme, Dieu pourra être apaisé pour lui; mais si c’est contre le Seigneur qu’un homme pèche, qui priera pour lui? Et ils n’écoutèrent pas la voix de leur père, parce que le Seigneur voulut les perdre.
26 Yaron nan Sama’ila ya dinga girma cikin kwarjini da cikin tagomashi a gaba Ubangiji da mutane.
Cependant l’enfant Samuel avançait et croissait, et plaisait autant au Seigneur qu’aux hommes.
27 Wani mutum ya zo wurin Eli ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ashe ban bayana kaina sosai ga mahaifinka lokacin da yake a Masar a ƙarƙashin Fir’auna ba?
Or, il vint un homme de Dieu vers Héli, et il lui dit: Voici ce que dit le Seigneur: Ne me suis-je pas ouvertement révélé à la maison de ton père, lorsqu’ils étaient en Égypte, dans la maison de Pharaon?
28 Na zaɓi mahaifinka daga cikin dukan kabilar Isra’ila yă zama firist nawa don yă yi hidima a bagade, don yă ƙona turare mai ƙanshi, don kuma yă sanya doguwar riga a gabana. Na kuma ba wa iyalin mahaifinka dukan hadaya ta ƙonawa da Isra’ila suka miƙa.
Je l’ai choisi entre toutes les tribus d’Israël pour mon prêtre, afin qu’il montât à mon autel, qu’il brûlât pour moi de l’encens, et qu’il portât un éphod devant moi; et j’ai donné à la maison de ton père de tous les sacrifices des enfants d’Israël.
29 Don me kuke rena hadayata da sadakokina da na ƙayyade domin mazaunina? Don me kake girmama’ya’yanka fiye da ni ta wurin cinye sashe mafi kyau na kowane hadayar da mutanena Isra’ila suka miƙa?’
Pourquoi avez-vous jeté sous vos pieds ma victime et mes présents que j’ai ordonné d’offrir dans le temple, et as-tu plus honoré tes fils que moi, pour que vous mangeassiez les prémices de tous les sacrifices d’Israël mon peuple?
30 “Saboda haka Ubangiji Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na yi alkawari cewa gidanka da gidan mahaifinka za su yi mini hidima a gabana har abada.’ Amma, yanzu Allah ya ce, ba zai yiwu ba; waɗanda suke girmama ni; Ni ma zan girmama su. Amma waɗanda suke ƙasƙantar da ni, haka za a ƙasƙantar da su.
C’est pour cela que le Seigneur Dieu d’Israël dit: Parlant, j’ai parlé, afin que ta maison et la maison de ton père servit en ma présence pour toujours. Or, le Seigneur dit maintenant: Loin de moi cela! mais quiconque m’aura glorifié, je le glorifierai; ceux au contraire qui me méprisent, seront avilis.
31 Lokaci yana zuwa sa’ad da zan rage ƙarfinka da ƙarfin iyalin gidan mahaifinka. Domin kada a sāke samun tsohon mutum a zuriyarka.
Voici que des jours viendront, et je couperai ton bras, et le bras de la maison de ton père, en sorte qu’il n’y ait point de vieillard dans ta maison.
32 Za ka zama da ɓacin rai a mazaunina ko da yake za a yi wa Isra’ila alheri. A zuriyarka ba za a taɓa samun tsohon mutum ba.
Et tu verras ton rival dans le temple, au milieu de toutes les prospérités d’Israël; et il n’y aura de vieillard dans ta maison en aucun jour.
33 Kowannenku da ban kashe daga hidima a bagadena ba, za a bar shi don yă cika idanunka da hawaye da kuma baƙin ciki, dukan sauran zuriyarka kuwa za su mutu a ƙuruciyarsu.
Cependant je n’enlèverai pas entièrement de mon autel tout homme issu de toi; mais je ferai que tes yeux s’éteindront, et que ton âme se desséchera: et une grande partie de ta maison mourra, lorsqu’elle sera parvenue à l’âge viril.
34 “‘Abin da kuma ya faru da’ya’yanka biyu Hofni da Finehas zai zama alama a gare ka; saboda mutuwarsu za tă zama a rana ɗaya.
Or, ce qui en sera pour toi le signe, est ce qui doit arriver à tes deux fils, Ophni et Phinéès: en un seul jour ils mourront tous les deux.
35 Zan tayar wa kaina amintaccen firist wanda zai aikata abin da nake so yă yi, zan kuwa ba shi zuriya da koyaushe za su yi aiki a gaban zaɓaɓɓen sarkina.
Et je me susciterai un prêtre fidèle qui agira selon mon cœur et mon âme; et je lui édifierai une maison fidèle, et il marchera devant mon christ, tous les jours.
36 Sa’an nan duk wanda ya rage a zuriyarka zai zo yă durƙusa a gabansa yă roƙi kuɗi da abinci, zai kuma roƙa a yardar masa yă taimaki firistoci da aiki domin yă sami abin da zai ci.’”
Or, il arriva, que quiconque sera resté dans ta maison, viendra, afin qu’on prie pour lui et qu’il offre une pièce d’argent, et une miche de pain, et qu’il dise: Admettez-moi, je vous conjure, à une fonction sacerdotale, afin que je mange une bouchée de pain.

< 1 Sama’ila 2 >