< Yoshuwa 5 >

1 To, da dukan sarakunan Amoriyawa na yammancin Urdun, da dukan sarakunan Kan’aniyawan da suke bakin teku suka ji yadda Ubangiji ya busar da kogin Urdun a gaban Isra’ilawa, har sai da dukansu suka ƙetare, zuciyarsu ta narke, suka karaya sosai har ma suka rasa samun ƙarfin hali su fuskanci Isra’ilawa.
Quand donc tous les rois des Amorrhéens qui habitaient au-delà du Jourdain, vers le côté occidental, et tous les rois de Chanaan qui possédaient les lieux voisins de la grande mer, apprirent que le Seigneur avait séché le cours du Jourdain devant les enfants d’Israël, jusqu’à ce qu’ils eussent passé, leur cœur défaillit, et le courage les abandonna, parce qu’ils craignaient l’entrée des enfants d’Israël.
2 A lokacin nan Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka yi wuƙaƙe na duwatsu ka yi wa Isra’ilawa kaciya.”
Alors le Seigneur dit à Josué: Fais-toi des couteaux de pierre, et circoncis pour la seconde fois les enfants d’Israël.
3 Sai Yoshuwa ya yi wuƙaƙe na duwatsu, ya yi wa Isra’ilawa kaciya a Gibeyat-Ha’aralot.
Il fit ce qu’avait commandé le Seigneur, et il circoncit les enfants d’Israël sur la colline de la circoncision.
4 Dalilin da ya sa ya yi haka shi ne, dukan waɗanda suka fito daga Masar, dukan mazan da suka kai shekarun shiga soja, sun mutu a cikin jeji a hanya bayan sun bar Masar.
Or voici la cause de la seconde circoncision: Tous les mâles d’entre le peuple, qui sortirent de l’Egypte, tous hommes de guerre, moururent dans le désert pendant les très longs détours du chemin;
5 Dukan mutanen da suka fito daga Masar an yi musu kaciya, amma duk waɗanda aka haifa a jeji a tafiya daga Masar, ba a yi musu ba.
Et ils avaient été tous circoncis; mais le peuple qui naquit dans le désert
6 Isra’ilawa sun yi tafiya a jeji shekaru arba’in, har sai da dukan mazan da suka kai shekarun shiga soja da suka bar Masar suka mutu, domin ba su yi wa Ubangiji biyayya ba. Gama Ubangiji ya rantse cewa ba zai bar su su ga ƙasar da ya yi wa iyayensu alkawari da rantsuwa cewa zai ba su ba, ƙasar da zuma da madara suke kwarara, ƙasar da take cike da albarka.
Pendant quarante années de marche dans cette très vaste solitude, fut incirconcis, jusqu’à ce que fussent consumés ceux qui n’avaient pas écouté la voix du Seigneur, et à qui auparavant il avait juré qu’il ne leur montrerait pas la terre où coulent du lait et du miel.
7 Sai ya sa yaransu ne suka taso a maimakonsu, su ne waɗanda Yoshuwa ya yi wa kaciya. Sun kasance ba kaciya gama ba a yi musu ba a hanya.
Les fils de ceux-ci succédèrent à leurs pères, et furent circoncis par Josué, parce qu’ils étaient incirconcis, comme ils étaient nés, et que pendant le chemin personne ne les avait circoncis.
8 Kuma bayan da aka yi wa al’ummar kaciya dukansu, sai suka dakata a nan, sai da suka warke.
Mais après qu’ils furent tous circoncis, ils demeurèrent campés dans le même lieu, jusqu’à ce qu’ils fussent guéris.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Yau na kawar muku da zargin Masar.” Saboda haka ake kiran sunan wurin Gilgal har wa yau.
Alors le Seigneur dit à Josué: Aujourd’hui, j’ai ôté l’opprobre de l’Egypte de dessus vous. Et ce lieu a été appelé du nom de Galgala jusqu’au présent jour.
10 Da yamman rana ta goma sha huɗu ga wata, lokacin da suke a Gilgal a filin Yeriko, Isra’ilawa suka yi Bikin Ƙetarewa.
Et les enfants d’Israël demeurèrent à Galgala, et firent la Pâque, au quatorzième jour du mois, vers le soir, dans les plaines de Jéricho.
11 A kashegarin Bikin, a wannan rana, sai suka ci daga cikin amfanin ƙasar, burodi marar yisti da hatsin da aka gasa.
Et ils mangèrent des fruits de la terre le jour suivant, des pains azymes et de la farine séchée au feu de la même année.
12 Kashegari bayan da suka ci amfanin ƙasar kuwa, Manna ta yanke, mutanen Isra’ila kuma ba su ƙara samunta ba. A wannan shekara suka fara cin amfanin ƙasar Kan’ana.
Et la manne cessa après qu’ils eurent mangé des fruits de la terre, et les enfants d’Israël n’usèrent plus de cette nourriture, mais ils mangèrent des fruits de la terre de Chanaan de la présente année.
13 To, da Yoshuwa ya yi kusa da Yeriko, ya tā da idanunsa ya duba, sai ya ga wani mutum tsaye a gabansa riƙe da takobi, sai Yoshuwa ya je wurinsa ya ce masa, “Kai namu ne ko na abokan gābanmu?”
Or, comme Josué était dans la campagne de la ville de Jéricho, il leva les yeux et vit un homme debout en face de lui, tenant un glaive nu; et il alla vers lui, et dit: Es-tu des nôtres ou de nos ennemis?
14 Mutumin ya ce, “Babu ko ɗaya, na dai zo ne a matsayin shugaban rundunar sojojin Ubangiji.” Sai Yoshuwa ya kwanta da fuskarsa har ƙasa, ya girmama shi, ya ce masa, “Ranka yă daɗe, wane saƙo kake da shi domin bawanka?”
Il répondit: Nullement, mais je suis le prince de l’armée du Seigneur, et maintenant je viens. Josué tomba incliné vers la terre. Et, adorant, il dit: Que dit mon Seigneur à son serviteur?
15 Shugaban rundunar sojojin Ubangiji ya amsa ya ce, “Ka cire takalmanka, gama wurin da kake tsaye, mai tsarki ne.” Sai Yoshuwa ya cire takalmansa.
Ôte, dit-il, ta chaussure de tes pieds; car le lieu dans lequel tu es est saint. Et Josué fit comme il lui avait été commandé.

< Yoshuwa 5 >