< Luke 20 >

1 On one of those days, as he was teaching the people in the temple and preaching the Good News, the priests and scribes came to him with the elders.
Ana nan wata rana, Yesu yana kan koyarwa a haikali da wa'azin bishara, sai shugaban firistoci da marubuta suka zo wurinsa da dattawa.
2 They asked him, “Tell us: by what authority do you do these things? Or who is giving you this authority?”
Suka yi magana, su na ce masa, “Gaya mana da wanne iko ne ka ke yin wadannan abubuwan? Ko wanene ya baka wannan ikon?”
3 He answered them, “I also will ask you one question. Tell me:
Ya amsa sai ya ce masu, “Ni ma zan yi maku tambaya. Gaya mani game
4 the baptism of John, was it from heaven, or from men?”
da baptisman Yahaya. Daga sama take ko kuwa daga mutane ne?”
5 They reasoned with themselves, saying, “If we say, ‘From heaven,’ he will say, ‘Why didn’t you believe him?’
Sai suka yi mahawara da junansu, suna cewa, “In mun ce, 'Daga sama,' zai ce, 'To don me ba ku ba da gaskiya gareshi ba?'
6 But if we say, ‘From men,’ all the people will stone us, for they are persuaded that John was a prophet.”
Amma in mun ce, 'Daga mutane ne,' dukan mutane za su jejjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata a ransu Yahaya annabi ne.”
7 They answered that they didn’t know where it was from.
Sai suka amsa cewa ba su san ko daga ina ne take ba.
8 Jesus said to them, “Neither will I tell you by what authority I do these things.”
Yesu yace masu, “To haka ni ma ba zan gaya maku ko da wanne iko nake yin wadannan abubuwan ba.”
9 He began to tell the people this parable: “A man planted a vineyard and rented it out to some farmers, and went into another country for a long time.
Ya gaya wa mutane wannan misali, “Wani mutum ya dasa gonar inabi, ya ba wadansu manoma jinginarta, sai ya tafi wata kasa har ya dade.
10 At the proper season, he sent a servant to the farmers to collect his share of the fruit of the vineyard. But the farmers beat him and sent him away empty.
Da lokacin girbi ya yi sai ya aiki wani bawansa zuwa wurin manoman, saboda su bashi daga cikin anfanin gonar. Amma manoman suka doke shi, sai suka kore shi hannu wofi.
11 He sent yet another servant, and they also beat him and treated him shamefully, and sent him away empty.
Ya aike wani bawa kuma sai suka daddoke shi, suka kunyatar da shi, suka kore shi hannu wofi.
12 He sent yet a third, and they also wounded him and threw him out.
Ya kuma sake aike na uku suka yi masa rauni, suka jefar da shi a waje.
13 The lord of the vineyard said, ‘What shall I do? I will send my beloved son. It may be that seeing him, they will respect him.’
Sai mai gonar inabin ya ce, 'Me zan yi? Zan aiki kaunattacen dana. Watakila zasu ba shi daraja.'
14 “But when the farmers saw him, they reasoned among themselves, saying, ‘This is the heir. Come, let’s kill him, that the inheritance may be ours.’
Amma sa'adda manoman suka gan shi, suka yi shawara a tsakaninsu, cewa, 'Wannan ne magajin. Bari mu kashe shi, saboda gadon ya zama namu.'
15 Then they threw him out of the vineyard and killed him. What therefore will the lord of the vineyard do to them?
Suka jefar da shi waje daga gonar, suka kashe shi. Menene ubangijin gonar inabin zai yi da su?
16 He will come and destroy these farmers, and will give the vineyard to others.” When they heard that, they said, “May that never be!”
Zai zo ya halakar da wadannan manoma, sai ya ba wadansu gonar.” Da suka ji wannan, suka ce, “Allah ya sawake!”
17 But he looked at them and said, “Then what is this that is written, ‘The stone which the builders rejected was made the chief cornerstone’?
Amma Yesu ya kalle su, sai yace, “Menene ma'anar wannan nassi? 'Dutsen da magina suka ki, an mayar da shi kan kusurwa'?
18 Everyone who falls on that stone will be broken to pieces, but it will crush whomever it falls on to dust.”
Duk wanda ya fadi kan dutsen zai farfashe. Amma duk wanda dutsen ya fadi a kansa, zai rugurguza shi.”
19 The chief priests and the scribes sought to lay hands on him that very hour, but they feared the people—for they knew he had spoken this parable against them.
Sai marubutan da manyan firistocin suka so su kama shi a wannan sa'a, domin sun sani ya yi wannan misali a kansu ne. Amma sun ji tsoron mutane.
20 They watched him and sent out spies, who pretended to be righteous, that they might trap him in something he said, so as to deliver him up to the power and authority of the governor.
Suna fakonsa, suka aiki magewaya, wadanda suke kamar masu adalci, saboda su sami kuskure cikin maganarsa, don su mika shi ga hukumci da kuma ikon gwamna.
21 They asked him, “Teacher, we know that you say and teach what is right, and aren’t partial to anyone, but truly teach the way of God.
Suka tambaye shi, cewa, “Malam, mun sani da cewa kana fada da koyar da abin ke daidai, kuma ba wanda yake cusa maka ra'ayi, amma kana koyar da gaskiya game da hanyar Allah.
22 Is it lawful for us to pay taxes to Caesar, or not?”
Wai shin doka ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
23 But he perceived their craftiness, and said to them, “Why do you test me?
Amma Yesu ya gane makircinsu, sai ya ce masu,
24 Show me a denarius. Whose image and inscription are on it?” They answered, “Caesar’s.”
“Nuna mani dinari. Sifar wanene da kuma rubutun wanene akan sa?” Suka ce, “Na Kaisar ne.”
25 He said to them, “Then give to Caesar the things that are Caesar’s, and to God the things that are God’s.”
Sai ya ce masu, “To sai ku ba Kaisar abin da ke na Kaisar, ku kuma ba Allah, abin da ke na Allah.”
26 They weren’t able to trap him in his words before the people. They marveled at his answer and were silent.
Marubutan da manyan firistocin ba su sami abin zargi cikin maganarsa, a gaban mutane ba. Suka yi mamakin amsar sa, ba su kuma ce komai ba.
27 Some of the Sadducees came to him, those who deny that there is a resurrection.
Sa'adda wadansu Sadukiyawa suka zo wurinsa, wadan da suka ce babu tashin mattatu,
28 They asked him, “Teacher, Moses wrote to us that if a man’s brother dies having a wife, and he is childless, his brother should take the wife and raise up children for his brother.
suka tambaye shi, cewa, “Malam, Musa ya rubuta mana cewa idan dan'uwan mutum ya mutu, mai mace kuma ba shi da yaro, sai dan'uwansa ya auri matar, ya samar wa dan'uwansa yaro.
29 There were therefore seven brothers. The first took a wife, and died childless.
Akwai 'yan'uwa guda bakwai kuma na farin ya yi aure, sai ya mutu babu da,
30 The second took her as wife, and he died childless.
haka ma na biyun.
31 The third took her, and likewise the seven all left no children, and died.
Na ukun ya aure ta, haka nan na bakwai ma bai bar yaya ba, har suka mutu.
32 Afterward the woman also died.
Daga baya sai matar ma ta mutu.
33 Therefore in the resurrection whose wife of them will she be? For the seven had her as a wife.”
To a ranar tashin mattatu, matar wa za ta zama? Domin duka bakwai din sun aure ta.”
34 Jesus said to them, “The children of this age marry and are given in marriage. (aiōn g165)
Yesu ya ce masu, “'Ya'yan duniyan nan suna aure, ana kuma ba da su ga aure. (aiōn g165)
35 But those who are considered worthy to attain to that age and the resurrection from the dead neither marry nor are given in marriage. (aiōn g165)
Amma wadanda aka ga cancantarsu a waccan tsara, sun isa su sami tashin mattatu, ba za suyi aure ko a aurar da su ba. (aiōn g165)
36 For they can’t die any more, for they are like the angels and are children of God, being children of the resurrection.
Gama ba za su mutu kuma ba, domin suna daidai da mala'iku kuma su 'ya'yan Allah ne, da shike su 'ya'yan tashin matattu ne.
37 But that the dead are raised, even Moses showed at the bush, when he called the Lord ‘The God of Abraham, the God of Isaac, and the God of Jacob.’
Amma batun tashi matattu, ko Musa ma ya nuna wannan, a cikin jeji, inda ya kira Ubangiji, Allah na Ibrahim da kuma Allah na Ishaku da Allah na Yakubu.
38 Now he is not the God of the dead, but of the living, for all are alive to him.”
Yanzu shi ba Allahn matattu ba ne, amma na masu rai, saboda duka suna raye a wurinsa.”
39 Some of the scribes answered, “Teacher, you speak well.”
Wadansu marubuta suka amsa, “Malam, ka amsa da kyau.”
40 They didn’t dare to ask him any more questions.
Gama ba su sake yi masa wadansu tambayoyi ba.
41 He said to them, “Why do they say that the Christ is David’s son?
Yesu ya ce masu, “Yaya suke cewa Almasihu dan Dauda ne?
42 David himself says in the book of Psalms, ‘The Lord said to my Lord, “Sit at my right hand,
Gama Dauda da kansa ya ce a cikin littafin Zabura, Ubangiji ya ce wa Ubangiji na, 'Zauna a hannun dama na,
43 until I make your enemies the footstool of your feet.”’
sai na maida makiyanka a karkashin tafin sawunka.'
44 “David therefore calls him Lord, so how is he his son?”
Dauda ya kira Kristi 'Ubangiji', to ta yaya ya zama dan Dauda?”
45 In the hearing of all the people, he said to his disciples,
Dukan mutane suna ji ya ce wa almajiransa,
46 “Beware of those scribes who like to walk in long robes, and love greetings in the marketplaces, the best seats in the synagogues, and the best places at feasts;
“Ku yi hankali da marubuta, wadanda suna son tafiya da manyan riguna, suna kuma son a gaishe su a cikin kasuwanni, da mayan wuraren zama a cikin majami'u, da kuma manyan wurare a wurin bukukkuwa.
47 who devour widows’ houses, and for a pretense make long prayers. These will receive greater condemnation.”
Suna kuma kwace wa gwamraye gidaje, suna kuma badda kama ta wurin yin doguwar addu'a. Wadannan za su sha hukumci mai girma.”

< Luke 20 >