< Mark 1 >

1 The beginning of the Good News of Jesus Christ, the Son of God.
Wannan itace farkon bisharar Yesu Almasihu, Dan Allah.
2 As it is written in the prophets, “Behold, I send my messenger before your face, who will prepare your way before you:
kamar yadda aka rubuta cikin littafin annabi Ishaya. Duba, ina aika manzona, a gabanka, wanda zai shirya maka hanya.
3 the voice of one crying in the wilderness, ‘Make ready the way of the Lord! Make his paths straight!’”
Akwai murya mai kira a jeji, tana cewa ka shirya hanyar Ubangiji. ka daidaita ta.
4 John came baptizing in the wilderness and preaching the baptism of repentance for forgiveness of sins.
Yahaya ya zo, yana baptisma acikin jeji yana wa'azin tuba, domin gafarar zunubai.
5 All the country of Judea and all those of Jerusalem went out to him. They were baptized by him in the Jordan river, confessing their sins.
Dukan kasar Yahudiya da mutanen Urshalima suka zo wurin sa, a ka kuma yi masu baptisma a kogin urdun. suna furta zunubansu.
6 John was clothed with camel’s hair and a leather belt around his waist. He ate locusts and wild honey.
Yahaya yana saye da tufa ta gashin rakumi, yana kuma da damara ta fata a kugunsa, abincinsa fara ce da zuma.
7 He preached, saying, “After me comes he who is mightier than I, the strap of whose sandals I am not worthy to stoop down and loosen.
Yana wa'azi, ya ce “akwai mai zuwa a bayana wanda ya ke da iko fiye da ni. wanda ko maballin takalminsa ban isa in kwance ba.
8 I baptized you in water, but he will baptize you in the Holy Spirit.”
Ni ina yi maku baptisma da ruwa, amma mai zuwa a bayana zai yi maku baptisma da Ruhu Mai Tsarki''.
9 In those days, Jesus came from Nazareth of Galilee, and was baptized by John in the Jordan.
Sai ya kasance a kwanakin nan Yesu ya zo daga Nazarat ta Galili, sai Yahaya ya yi masa baptisma a kogin urdun.
10 Immediately coming up from the water, he saw the heavens parting and the Spirit descending on him like a dove.
Sa'adda Yesu ya fito daga ruwan, sai sama ta bude, sai Ruhu ya sauko a bisansa da kamanin kurciya.
11 A voice came out of the sky, “You are my beloved Son, in whom I am well pleased.”
Sai wata murya ta zo daga sama, tana cewa, “Kai kaunataccen Dana ne. zuciyata ta na murna da kai kwarai''.
12 Immediately the Spirit drove him out into the wilderness.
Sai Ruhu ya iza shi zuwa jeji.
13 He was there in the wilderness forty days, tempted by Satan. He was with the wild animals; and the angels were serving him.
Yana a jeji kwana arba'in, Shaidan yana jarabtar sa. Yana cikin jeji da dabobi, sai malaiku su ka yi masa hidima.
14 Now after John was taken into custody, Jesus came into Galilee, preaching the Good News of God’s Kingdom,
Bayan da aka kama Yahaya, Yesu ya shiga kasar Galili yana wa'azin bisharar Allah.
15 and saying, “The time is fulfilled, and God’s Kingdom is at hand! Repent, and believe in the Good News.”
Yana cewa, “Lokaci ya yi, gama mulkin Allah ya kusato. Ku tuba ku bada gaskiya ga bishara”.
16 Passing along by the sea of Galilee, he saw Simon and Andrew, the brother of Simon, casting a net into the sea, for they were fishermen.
Sa'adda ya ke wucewa a gefen takun Galili, sai ya ga Saminu da Andarawus, dan'uwansa suna jefa taru a teku, domin su masunta ne.
17 Jesus said to them, “Come after me, and I will make you into fishers for men.”
Yesu ya ce masu ku zo, ku biyo ni, ni kuwa sai in maisheku masuntan mutane”.
18 Immediately they left their nets, and followed him.
Nan da nan suka bar tarun su, suka bi shi.
19 Going on a little further from there, he saw James the son of Zebedee, and John his brother, who were also in the boat mending the nets.
Sa'adda Yesu ya yi tafiya kadan, sai ya ga Yakubu dan Zabadi da Yahaya dan'uwansa; suna gyaran tarunsu a jirgin ruwa.
20 Immediately he called them, and they left their father, Zebedee, in the boat with the hired servants, and went after him.
Sai ya kira su, su kuwa suka bar mahaifinsu Zabadi a jirgin ruwan da ma'aikatansu, sai su ka bi shi.
21 They went into Capernaum, and immediately on the Sabbath day he entered into the synagogue and taught.
Da su ka shigo cikin kafanahum, a ranar asabar, Yesu ya shiga majami'a ya koya masu.
22 They were astonished at his teaching, for he taught them as having authority, and not as the scribes.
Su ka yi mamakin koyarwarsa, domin ya na koya masu da iko ba kamar marubuta ba.
23 Immediately there was in their synagogue a man with an unclean spirit, and he cried out,
A nan cikin majami'a akwai wani mutum mai kazamin ruhu, sai ya yi ihu da karfi.
24 saying, “Ha! What do we have to do with you, Jesus, you Nazarene? Have you come to destroy us? I know who you are: the Holy One of God!”
Yana cewa Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo ne domin ka halakar da mu? Na san wanene kai. Kai ne Mai Tsarki na Allah”.
25 Jesus rebuked him, saying, “Be quiet, and come out of him!”
Sai Yesu ya tsauta wa kazamin ruhun ya ce, “Ka yi shiru ka fita daga cikinsa”.
26 The unclean spirit, convulsing him and crying with a loud voice, came out of him.
Bayan da kazamin ruhun ya buga shi kasa, sai kazamin ruhun ya yi ihu sa'annan ya fita daga jikinsa.
27 They were all amazed, so that they questioned among themselves, saying, “What is this? A new teaching? For with authority he commands even the unclean spirits, and they obey him!”
Sai dukan mutanen su ka yi mamaki kwarai, suna tambayar junansu menene wannan? wace sabuwar koyarwa ce da iko haka? har yana umartar kazaman ruhohi suna kuwa yi masa biyayya!”
28 The report of him went out immediately everywhere into all the region of Galilee and its surrounding area.
Nan da nan labarinsa ya bazu ko'ina a dukkan kewayen kasar Galili.
29 Immediately, when they had come out of the synagogue, they came into the house of Simon and Andrew, with James and John.
Bayan da suka bar majami'a, sai su ka shiga gidan Saminu da Andarawus, suna kuma tare da Yakubu da Yahaya.
30 Now Simon’s wife’s mother lay sick with a fever, and immediately they told him about her.
Surikar Saminu tana kwance ba lafiya tana fama da zazzabi. Sai suka gaya wa Yesu game da ita.
31 He came and took her by the hand and raised her up. The fever left her immediately, and she served them.
Sai ya zo, ya kama hannunta, ya daga ta, sai zazzabin ya sake ta, ta fara yi masu hidima.
32 At evening, when the sun had set, they brought to him all who were sick and those who were possessed by demons.
Da yamman nan, bayan da rana ta fadi, sai su ka kawo masa dukan marasa lafiya da masu fama da aljanu.
33 All the city was gathered together at the door.
Dukan mutanen garin su ka taru a bakin kofa.
34 He healed many who were sick with various diseases and cast out many demons. He didn’t allow the demons to speak, because they knew him.
ya warkar da masu ciwo da yawa da masu chututtuka iri-iri, ya kuma fitar da bakaken aljanu, amma bai yarda aljanun su yi magana ba domin sun san shi.
35 Early in the morning, while it was still dark, he rose up and went out, and departed into a deserted place, and prayed there.
Ya tashi da sassafe, tun da sauran dare, ya tafi wurin da ba kowa, a can ya yi add'ua.
36 Simon and those who were with him searched for him.
Saminu da wandanda suke tare da shi suka neme shi.
37 They found him and told him, “Everyone is looking for you.”
Suka sa me shi, sai su ka ce masa, “kowa yana nemanka”.
38 He said to them, “Let’s go elsewhere into the next towns, that I may preach there also, because I came out for this reason.”
Ya ce, bari mu tafi wani wuri, zuwa wadansu garuruwan da ke kewaye, Saboda in yi wa'azi a can kuma. Wannan shi yasa na zo nan''.
39 He went into their synagogues throughout all Galilee, preaching and casting out demons.
Ya tafi dukan kasar Galili, yana wa'azi a majimi'un su yana kuma fitar da aljanu.
40 A leper came to him, begging him, kneeling down to him, and saying to him, “If you want to, you can make me clean.”
Wani kuturu ya zo wurinsa. Yana rokonsa, ya durkusa. Ya ce masa, “in ka yarda kana iya warkar da ni.
41 Being moved with compassion, he stretched out his hand, and touched him, and said to him, “I want to. Be made clean.”
Sai ya yi juyayi, Yesu ya mi ka hannun sa ya ta ba shi ya na ce masa “Na yarda. Ka sarkaka”.
42 When he had said this, immediately the leprosy departed from him and he was made clean.
Nan da nan kuturtar ta barshi, ya kuma sa mu tsarkakewa.
43 He strictly warned him and immediately sent him out,
Yesu ya yi masa gargadi sosai, ya salame shi.
44 and said to him, “See that you say nothing to anybody, but go show yourself to the priest and offer for your cleansing the things which Moses commanded, for a testimony to them.”
Ya ce masa “ka tabbata fa kada ka gayawa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, sai ka je ka yi hadaya domin tsarkakewa kamar yadda Musa ya umurta, domin shaida.
45 But he went out, and began to proclaim it much, and to spread about the matter, so that Jesus could no more openly enter into a city, but was outside in desert places. People came to him from everywhere.
Amma da ya fita sai ya fara gaya wa kowa, ya baza maganar a ko'ina, har Yesu bai iya tafiya a sake a garin ba. Ya tafi ya tsaya a wuraren da ba kowa, mutane kuwa su ka zo wurinsa daga ko'ina.

< Mark 1 >