< Yuhana 21 >

1 Kimal ni leli imone tutung, Yesu durso liti me kitin nono katwa me kurawan Tibariya; nanere awa durso litime.
Bayan wadannan abubuwa, Yesu ya sake bayyana kansa ga almajiran a bakin tekun Tibariya. Ga yadda ya bayyana kansa:
2 Simon Bitrus wadi ligowe nin Toma ulenge na iwa din yicighe fibari, nin Nataniyel un Kan ana nya Galili, nonon Zabadin nin nan nono katwa Yesu niba ugan.
Saminu Bitrus na tare da Toma wanda ake kira Dan Tagwai, da Natana'ilu daga Kana ta kasar Galili, da 'ya'yan nan na Zabadi, da kuma wadansu almajiran Yesu biyu.
3 Simon Bitrus woro nani, “Meng ma du nkifuzu nibo.” I woroghe nenge, “Arik wang ma du nanfi.” I do idi piru uzirgin nmyen, kiti shanta na ikifo imonba.
Saminu Bitrus yace masu, “Zani su.” sukace masa “Mu ma za mu je tare da kai.” Sai suka fita suka shiga jirgi, amma a daren nan basu kama komai ba.
4 Na kitin shanta, Yesu yissina ngau kurawe, na inung nono katwa we wa yiru Yesuari ba.
To, gari na wayewa, sai ga Yesu tsaye a bakin gaci, amma almajiran basu gane cewa Yesu bane.
5 Yesu tunna a woro nani, “Uzaman, idi nin nimoimon in nlya?' I kawaghe, “Tidimun ba.”
Sai Yesu yace masu, “Samari, kuna da wani abinda za a ci?” Suka amsa masa sukace “A'a”.
6 A woro nani, “Ton imon in kifizu nibo mine ncara ulime nzirge, ima se imon.” Itunna ito imon nkifizu nibowe, na iwa yinin unutune ba bara ngbardang nibowe na iwa kifo.
Yace masu, “Ku jefa taru dama da jirgin zaku samu wasu.” Suka jefa tarunsu har suka kasa jawo shi don yawan kifin.
7 Gono katwa kanga na Yesu wa di nin suwe woro Bitrus ku, “Cikilareari” Na Bitrus nlanza Cikilareari, a kiro kidowo me nin gudun (bara na awa min imon icine kidowo me ba), amini wa tunnun a nyina nanya kurawe.
Sai almajirin nan da Yesu yake kauna yace wa Bitrus, “Ubangiji ne fa!” Da Saminu Bitrus yaji, Ashe, Ubangiji ne, yayi damara da taguwarsa, (don a tube yake), ya fada a tekun.
8 Ngisin nono katwa we da nanya nzirgin nmyene, (bara na iwa di piit nin gau kurawe ba, nafo abunu akut likure udi duru kutyen), inani wa di nwunu nimon kifizu nibo mine gbem nin nibo.
Sauran almajiran kuwa suka zo a cikin karamin jirgi, (domin basu da nisa da kasa, kamar kamu dari biyu zuwa sama), janye da tarun cike da kifi.
9 Na iwa nuzu udu kutyen, iyene acalang nla kitene nin nibo a ufungal ku, kitene.
Da isowarsu gaci, sai suka ga garwashin wuta a wurin da kifi akai, da kuma gurasa.
10 Yesu woro nani, “Daan nin nimon ibo na iworin kifu.”
Yesu ya ce masu “Ku kawo wandansu daga cikin kifin da kuka kama yanzu”.
11 Simon Bitrus do adi wunun imon nkifizu nibowe udu kutyen, gbem nin nibo inin akalt likure nin natat. Vat nin gbardang ni ninig, na imon kifuzue wa marta ba.
Sai Saminu Bitrus ya hau, ya jawo tarun gaci, cike da manyan kifaye dari da hamsin da uku. Amma duk da yawansu, tarun bai tsage ba.
12 Yesu woro nani, “Daan ida li tyara” Na umong nanya nono katwa we wa se kibinayi ntiringhe, “feghari ba? Inung wa yiru Cikilareari
Yesu yace masu, “Ku zo ku karya kumallo”. Daga cikin almajiran kuwa babu wanda yayi karfin halin tambayarsa “Ko shi wanene?” Domin sunsani Ubangiji ne.
13 Yesu da ada yirra ufunga a nakpa nani uni, umunu ibowe ku.
Yesu zo ya dauki gurasar ya ba su, haka kuma kifin.
14 Uleli uzurue utattari wadi na Yesu wa durso litime kitin nono katwa we kimal nfitu me nanyan kul.
Wannan shine karo na uku da Yesu ya bayyana ga almajiransa bayan tashinsa daga matattu.
15 Na ileo tyara, Yesu woro Simon Bitrus ku, “Simon usaun Yuhana, udi nin sunighe kang ukati ulele?” Bitrus woroghe, “Nanere, Cikilari; uyiru ndi nin sufe.” Yesu woroghe, “Sulibya na kam ninghe.”
Da suka karya kumallon, Yesu yace wa Saminu Bitrus, “Bitrus dan Yahaya, kana kaunata fiye da wadannan?” Bitrus yace masa “I ya Ubangiji, ka sani ina kaunarka” Yesu yace masa “Ka ciyar da 'ya'yan tumakina”.
16 Akuru a bellinghe unba, “Simon, usaun Yuhana, udi nin sughe?” Bitrus woroghe, “Nanere Cikilari, fewe yiru ndi nin sufe.” Yesu woroghe, Su libya na kam ning.”
Ya sake fada masa karo na biyu, “Saminu Dan Yahaya, kana kaunata?” Bitrus Yace masa “I ya Ubangiji, ka sani ina kaunarka”. Yesu yace masa, “Ka lura da Tumakina”.
17 A bellinghe tutung untat, “Simon usaun Yuhana, udi nin Su nighe?” Ayin Bitrus nana bara na Yesu ntiringhe untat,”Udi nin Su nighe?” A woro ghe nenge, “Cikilari, uyiru imon vat, uyiru kap ndi nin sufe.” Yesu woroghe, “Su libya na kam nighe.”
Ya sake fada masa, karo na uku, “Bitrus Dan Yahaya, kana kaunata? Sai Bitrus bai ji dadi ba domin Yesu ya fada masa karo na uku, “Kana kaunata” Yace masa, “Ubangiji ka san komai duka, ka sani ina kaunarka.” Yesu yace masa “Ka ciyar da tumaki na.
18 Kidegenere, Ndin belu f, kube na uwa di gono, asa ushono imon udo kiti kanga na udi nin sun due; asa ukuno uta kukune, uma nakpu acarafe, umong shonfi imon a yaunfi adomun kiti kanga na udi nin sun due ba.”
Hakika, hakika, Ina gaya maka, lokacin da kake kuruciyarka, kakan yi wa kanka damara, ka tafi inda ka ga dama. amma in ka tsufa, zaka mike hannuwanka wani yayi maka damara, ya kai ka inda baka nufa ba.”
19 Yesu wa bellin nani, anan ta iyinno imus nkul ulenge na Bitrus masu, ati Kutelle gongong. Na amala ubellu nani, a woro Bitrus ku, “Dofini.”
To Yesu ya fadi haka ne domin ya nuna irin mutuwar da Bitrus zai yi ga daukakar Allah. Bayan ya fadi haka, sai yace wa Bitrus, ka biyo ni.
20 Bitrus gitirno, a yene gono katwa kanga na Yesu dinin sume din dortu nani- ulenge na awa sossin figirin Yesu kubin lii nimonli a woro, a woro, “Ghari unite na ama lewufi?”
Bitrus ya juya sai ya ga almajirin da Yesu yake kauna yana biye dasu; wanda ya jingina a kirgin Yesu lokacin cin jibin nan da yace “Ya Ubangiji, wanene zai bashe ka?”
21 Bitrus yene ghe a woro Yesu ku, “Iyaghari unit ulele masu?”
Da Bitrus ya gan shi, yace wa Yesu “Ya Ubangiji, Me mutumin nan zai yi?”
22 Yesu woroghe, “Andi nfere acica uduru usa nighe, iyaghari nmyenfeku? Dofini.”
Yesu yace masa, “Idan ina so ya zauna har in dawo ina ruwanka? Ka biyo ni.”
23 Uliru une mala kiti nanya linuana vat, au na kani gono katwa we ba ku ba. A nani, na Yesu wa woro Bitrus a na kani gono katwa we ba ku ba, ame dei wa woro “Andi nfere a cica uduru usa nighe iyaghari nmyenfeku?”
Wannan zance ya yadu cikin 'yan'uwa cewa, wannan almajirin ba zai mutu ba. Alhali Yesu bai cewa Bitrus, wannan almajirin ba zai mutu ba, Amma “Idan ina so ya zauna har in dawo ina ruwanka?”
24 Amere gono katwa kanga na ana ni ushaida ni lenge imone, ulenge na ana nyertin ilenge imone, tiyiru tutung ushaida me kidegenere.
Wannan shine almajirin da yake shaida wadannan abubuwa, wanda ya rubuta su, kuma mun tabbata shaidarsa gaskiya ne.
25 Imonimong duku tutung gbardang na Yesu na su. Inda nafo ina yertu ining vat, nyinan nworu unin uyie litime na uwa se kitin ciwu nafa niyerte ile na iwa su ba.
Akwai kuma sauran abubuwa da yawa wanda Yesu yayi. Idan da an rubuta kowannensu daya bayan daya, ina gaya maku, ko duniya bazata iya daukar litattafan da za a rubuta ba.

< Yuhana 21 >