< Katwa Nono Katwa 1 >

1 Kutankardan nburne kurka nan wan jertin fimu, Theophilus, inbellen katuawa karka na Yesu wa su akuru a dursuzo,
Littafin da na rubuta da farko, Tiyofilos, ya fadi abubuwan da Yesu ya fara yi ya kuma koyar,
2 har kubi ko na iwa yirgye udumu kitene kane. Ulele wa di bayan urka na nono kaduro me nsere timap tirka na iba durtu na cara Ufunu Ulau nono kadura karka na fere.
har zuwa ranar da aka karbe shi zuwa sama. Wannan kuwa bayan da ya ba da umarni ga zababbun manzanninsa ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
3 Arka na awa durso litime nin lai bayaqn nipama iniu me. Ata ayiri akut anas ndursuzuani me, tutung incin nbeliani nbelen kilari tigo Kutelle.
Bayan ya sha wahala, ya bayyana kan sa da rai a garesu, da alamu da dama masu gamsarwa. Kwana arba'in ya baiyana kansa a garesu yana yi masu magana game da mulkin Allah.
4 Kubi kona awa ligowe nanghinu, anin woro nanin “na wa cin nanya Urshalime ba. Bar nanin son ca, na alkawali Imba ulena ana su minu mu na mani Ufunu Ulau kutelle nama su, na ina malin lanzu kitiningya.
Yayin da yana zaune tare da su ya basu umarni cewa kada su bar Urushalima, amma su jira alkawarin Uban, wanda ya ce, ''Kun ji daga gare ni,
5 Yohanna wa su ubaptizima nin mmen, nin kidun ninnayiru baat Kutelle ma suminu ubastizima nin Funu ulau.”
cewa Yahaya babu shakka ya yi baftisma da ruwa, amma ku za a yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki nan da kwanaki kadan.''
6 Kubi ko na iwa zuro kiti kirum, i tiringye, ''Cikilari, kome kubiari uba kurtunu Kilari Ugo Kutenlle?''
Sa'adda suna tare suka tambaye shi, ''Ubangiji, a wannan lokaci ne za ka maido da mulki ga Isra'ila?”
7 A woroani, ''na ummunere iyini kubi nin kubiri kurka na Ucif kele bari likarame.
Ya ce masu, ''Ba naku bane ku san lokaci ko sa'a wanda Uba ya shirya ta wurin ikonsa.
8
Amma za ku karbi iko, idan Ruhu Mai Tsarki ya zo bisanku, sa'annan za ku zama shaidu na cikin Urushalima da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, har ya zuwa karshen duniya.”
9 Daana abenle uliru une, amini wa fita cindu kitene kane, awut kitene kane wantina nanin iyenju Yesu ku, udu wulu nizi mine.
Lokacin da Ubangiji Yesu ya fadi wadannan abubuwa, yayin da suna kallon sama, sai aka dauke shi zuwa sama, kuma girgije ya boye shi daga idanunsu.
10 Dana anan nono katua wa din yenju udume kitene kane. Nya kube Among anit awa ba tin yisina kupopo mine nin na littuk aboo. Iwadi anan kadura Kutelleari.
Da suka dinga kallon sama yayin da ya tafi, nan da nan, mazaje biyu suka tsaya a gabansu cikin fararen tufafi.
11 Umong worum nin woro, “Anuyge anan Galili bar yangyari indin yenju kitene kane na iwa isin idin yenju kitene kane ba! Nlon liri Yesu ulele ulena Kutelle yira gye ama dak ule uye tutun. Abakpilu nannya ulele na iyenegye adin cinu udu kitene kane.”
Suka ce, ''Ku mazajen Galili me yasa ku ke tsaye a nan kuna kallon sama? Wannan Yesu wanda ya hau zuwa sama zai dawo kamar yadda kuka gan shi yana tafiya zuwa sama.''
12 Da na nono kadura Kutenlle kpila, nonon bazu inliru kutenlle kpinlla u-Urshalima unzu Kupara Olives urka na uwa susut un-Urshalimae.
Da suka dawo Urushalima daga dutsen Zaitun, wanda ke kusa da Urushalima, tafiyar Asabaci daya ne.
13 Da na isa, ighana ipira kuti kitene, kika iwa sosinku. Isan nnono kadure tone: Bitrus, Yohanna, Yakub, Andarawus, Filibos, Toma, Batamawus, Matta, Yakub usaun Haffa, Simon ku-zelot, and Yahuda usaun Yakub.
Da suka iso, sai suka haye zuwa cikin bene inda suke da zama. Sune su Bitrus, Yahaya, Yakubu, Andarawus, Filibus, Toma, Bartalamawus, Matiyu, Yakubu dan Alfa, Siman mai tsattsauran ra'ayi, kuma da Yahuza dan Yakubu.
14 Vat mine wa muna ati nafo warum inlira mu cancom. Nannya mine awani wa duku, Marayamu unan Isa nan nuane.
Dukansu kuwa suka hada kai gaba daya, yayin da suka ci gaba da naciya cikin addu'a. Tare da su kuma akwai mata, Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma 'yan'uwansa.
15 Nan nayirane Bulus nin fita nan nuana me anan yinnu sauye. Kubi kind anan dortu Yesu wadi anit likalt nin Na kuta bah kitene. Amino wa woro,
A cikin wadannan kwanaki Bitrus ya tashi tsaye a tsakiyar 'yan'uwa, kimanin mutane dari da ashirin, ya ce,
16 “Linuana nin ton tipinpin wadi kitenen Yahuda tona ugo Dauda wa yerti, uworsu. To ti pipingye Na dak kidegenghe, barna Ufunu Ulauwe Na belin Dauda ku a yertin.
'' 'Yan'uwa, akwai bukatar Nassi ya cika, wanda Ruhu Mai Tsarki ya fada a baya ta bakin Dauda game da Yahuza, wanda ya jagoranci wadanda suka kama Yesu
17 Aworo nanin awadi gono kata Kutelle nafo arik, amino durso anan ni vira Yesu inanin wakifo imologhe.”
Domin yana daya daga cikinmu kuma ya karbi rabonsa na ladan wannan hidima,”
18 Nene unit une nase ukubu kitenen su ni vira ine Nin Nile ikube awa seru kunen. Amino wa diu kutin kika ne liburi me tutoo tijiye gonna ti nuzu udas timalakiti.
(Wannan mutum fa ya sai wa kansa fili da cinikin da ya yi na muguntarsa, kuma a nan ya fado da ka, cikinsa ya fashe, hanjinsa suka zubo waje.
19 Vat anit na idin nanya Urshalima lanza yeri segye, inanin na yicila lisa kitene imin mmi nin tilem na aramik bar kitenere umon na kukuo.
Duka mazaunan Urushalima suka ji wannan, saboda haka suka kira wannan fili da harshensu “Akeldama'' wato, “Filin Jini.”)
20 Ame Bitrus nin kuro woro, “In na yene ilemon na ina se Yahudaku idi nafo na Maizaburana belin ari, “na kilarime ku vat, na iwa cin umon kilari meba.”' iminin yene tuo tipipinnye na Dauda na nyertin tidi kitene Yahudere: 'Na umon yiru kutet me.'”
“Domin an rubuta a littafin Zabura, 'Bari filinsa ya zama kufai, kada a bar kowa ya zauna wurin,'kuma, 'Bari wani ya dauki matsayinsa na shugabanci.'
21 Bara nanin ukamata ti fere ulena ama yiru kitu me (kutet Yahuda) ukamata unite di nan arik kubi kon Cikilari bite Yesu wa fere nari.
Saboda haka ya zama dole, daya daga cikin wadanda suke tare da mu tun lokacin da Ubangiji Yesu yana shiga da fita, a tsakaninmu,
22 Indian with tun kubi kana ame Yohana wa ti Yesu ku ubaptisema had udak kubi kana iwa hirigye Yesu ku kitene Kane. Unit ulena tima feru the AMA yitu ulena Ana yene Yesu ku kin nzime ayita nin lai nin kidun kulme.
farawa daga baftismar yahaya har zuwa ranar da aka dauke shi daga wurinmu zuwa sama, ya zama daya daga cikin mu wurin shaidar tashinsa.”
23 Barà nanin nono katua me nin gonna nin tisa anit a tiba. Umon lisame wadi Yusuf Barsabas, ulena Lisa me wadi tutun Justus. Unan ba wadi Matthias.
Suka gabatar da mutum biyu, Yusufu wanda ake kira Barsabbas, wanda kuma aka yiwa suna Justus, da kuma Matayas.
24 Itaa nlira iworo, “Fe Cikilari, yiru nibinei nanit vat, durso nari nanya nawaba alele na ufere
Su ka yi addu'a suka ce, ''Ubangiji, kai ka san zuciyar dukan mutane, ka bayyana mana wanda ka zaba cikin su biyun nan
25 ayiru kiti nanyan nkaa katawe na Yahuda nacin ana ti kulapi amini naduo kika na kiduogye.”
Domin ya dauki gurbin da kuma manzancin daga inda Yahuza ya kauce zuwa nashi waje''
26 Inanin wa su mafeferu, Mathias leu ma feruferu amini wasuo urum nanya nanan kata Yesua.
suka jefa kuri'a a kansu; zabe ya fada kan Matayas kuma suka lissafta shi tare da manzanni sha dayan.

< Katwa Nono Katwa 1 >