< Yuhana 14 >

1 Na iwa yinin ayi mine nana ba. Yinnan nin Kutelle; yinna nin mi wang.
“Kada zuciyarku ta bachi. Kun gaskata da Allah, sai kuma ku gaskata da ni.
2 Ngan Cifining niti lissosin duku gbardang; ndafo na nani ba, nwa bellin minu, nma du ndi kyele minu kiti.
A gidan Ubana akwai wurin zama dayawa. Da ba haka ba, da na fada maku, domin zan tafi in shirya maku wuri.
3 Asa ndo ndi kyele minu kiti, nma kuru nsa nda yiru minu nin litining bara kiti kanga na meng duku, anung wang nan so ku.
In kuwa na je na shirya maku wuri, zan dawo in karbe ku zuwa wurina domin inda nake kuma ku kasance.
4 Kiti ka na ndin cinu udue, iyiru libauwe.”
Kun san hanya inda zan tafi.”
5 Tuma woro Yesu ku, “Cikilari, nati yiru kikangga na udin cinu udue ba, iyizari tima yyinnu libauwe?”
Toma ya ce wa Yesu, “Ubangiji, bamu san inda za ka tafi ba, yaya za mu san hanyar?”
6 Yesu woroghe, “Menghari libauwe, kidegene nin lai; na umong wasa ada kitin Cifeba, se adofino kiti ning.
Yesu ya ce masa, “Ni ne hanya, ni ne gaskiya, ni ne rai; Ba mai zuwa wurin Uba sai ta wurina.
7 Andi iyinni, ima yinnu Ucif ninghe wang; ucizunu nene udu ubun, iyininghe, iyeneghe tutung.”
Da kun san ni, da kun san Ubana kuma. Amma daga yanzu kun san shi, kuma kun gan shi.”
8 Filibus woro Yesu ku, “Cikilari durso nari Ucife, ulele ma batinu nari.”
Filibus ya ce wa Yesu, “Ubangiji, ka nuna mana Uban, wannan za ya ishe mu.”
9 Yesu woroghe, “Ndandauna kiti mine kan nani, umini du sa uyinniya Filibus? Vat nlenge na ayenei, ayene ucife; iyizari uma woru, durso nari Ucife?
Yesu ya ce masa, “Ina tare da ku da dadewa, amma har yanzu baka san ni ba, Filibus? Duk wanda ya gan ni, ya ga Uban. Yaya za ka ce, 'Nuna mana Uban'?
10 Na uynna nworu ndi nanya Ncife, a Ucif nanya nighe ba? Ulire na ndin su na unliti nighari ba; nani, Ucifere na adi nanya nighere dinsu katwa me.
Baka gaskata cewa Ina cikin Uban, Uban kuma yana ciki na ba? Maganganun da nake fada maku, ba da ikona nake fadi ba, amma Uban ne da yake zaune a ciki na yake yin ayyukansa.
11 Yinna nin mi, nworu ndi nanya Ncife, a Ucife nanya ning; andi na nani ba, yinna ni mi bara nitwa nighe.
Ku gaskata ni cewa ina cikin Uban, Uban kuma na ciki na, ko kuwa ku bada gaskiya domin ayyukan kansu.
12 Kidegenere, ndin belu minu, ulenge na ayinna nin mi, nitwawe na ndin su, ame ma su ni ning wang, ame masu ni didya bara na meng din cinu ucindu kitin Cife.
“Lalle hakika, ina gaya maku, duk wanda ya gaskata ni zai yi ayyukan da nake yi, kuma zai yi ayyuka fiye da wadannan, domin zan tafi wurin Uba.
13 Vat nimon ile na itirino nanya lissaning, Meng masu ining bara Ucife nan se ngongong nanya Nsaune.
Duk abinda kuka roka da sunana, zan yi shi domin a daukaka Uban cikin Dan.
14 Asa utirino imonmong nanya lissaning, mma su.
Idan kuka roke ni komai cikin sunana, zan yi shi.
15 Andi udi nin su ning uma dortu uduka ning.
“Idan kuna kaunata, za ku kiyaye dokokina.
16 Meng masu Ucife kucukusu, ame ma nimu umong unan bunu bara anan so nan ghinu udu sa ligang. (aiōn g165)
Sa, annan zan yi addu'a ga Uba, zai kuwa baku wani mai ta'aziya domin ya kasance tare daku har abada. (aiōn g165)
17 Uruhu kidege. Na uyii wasa usereghe ba bara na udin yenjughe ba ana uyirughe ba. Anung, iyirughe, bara a sosin nanghinu tutun ama yitu nanya mine.
Ruhun gaskiya. Wanda duniya ba zata iya karba ba, domin bata gan shi ba, ko ta san shi. Amma ku kun san shi, domin yana tare da ku, zai kuma kasance a cikin ku.
18 Na nma sun minu usanminu ba; nma kpillu kiti mine.
Ba zan barku ku kadai ba; zan dawo wurin ku.
19 Nin kubiri bat, uyee ba kuru uyene ba, ama anung ma yenjui. Meng ma yittu nin lai, anung ma ti ulai.
Sauran dan gajeren lokaci, duniya kuma ba zata ka ra gani na ba, amma ku kuna gani na. Saboda ina raye, kuma zaku rayu.
20 Lilone ima yinnu nworu ndi nanya Ncifning, anung yitta nanya nighe, ameng yitta nanya mine.
A wannan rana zaku sani ina cikin Ubana, ku kuma kuna ciki na, ni ma ina cikin ku.
21 Ulenge na adi nin duka nighe amini din dortu unin, amere ule na adi nin sunighe; ame ulenge na adi nin sunig, Ucif ning mati usume, Meng mati usu me ndurso liti ning kiti me.”
Shi wanda yake da dokokina yake kuma bin su, shine ke kauna ta, kuma shi wanda ke kauna ta Ubana zai kaunace shi, Ni ma kuma zan kaunace shi in kuma bayyana kaina gare shi.”
22 Yahuda (na Iskaroti ba) woro Yesu ku, “Cikilari, iyaghari mati udurso litife kiti bit ana kitin yii ba?”
Yahuza (ba Iskariyoti ba) ya ce ma Yesu, “Ubangiji, meyasa za ka bayyana kanka a gare mu, ba ga duniya ba?”
23 Yesu kawa aworoghe, “Andi umong di nin suu nighe ama dortu uliru nighe. Ucif nighe ma yitu nin suu me, arik tina dak kitime ti da so ligowe nanghe.
Yesu ya amsa ya ce masa,”Kowa yake kauna ta, zai kiyaye maganata. Ubana kuwa zai kaunace shi, za mu zo wurinsa mu zauna tare da shi.
24 Ulenge na adi nin suu nighe ba, na adin dortu uliru nighe ba. Ulire na ilanza na unaghari ba un Cifere na anan tuyi.
Shi wanda baya kauna ta, ba ya kiyaye maganganuna. Maganar da kuke ji ba daga gareni take ba, amma daga Uba wanda ya aiko ni take.
25 Ndin bellu minu ule ulire, a ndutu nanginu.
Na fada maku wadannan abubuwa, sa'adda nake tare da ku.
26 Vat nani, unan bune, Uruhu ulauwe, ulenge na ucife matuu nin lissa nighe, ma dursuzu minu imon vat, imon ile na nna belu minu.
Saidai, mai ta'aziyar- Ruhu Mai Tsarki wanda Uba zai aiko cikin sunana, zai koya maku kome, kuma zai tunashe ku dukan abinda na fada maku.
27 Lissosin lishau nsun minu mun, Nna minu lissosin lisheu ning. Na ndin nizu nafo na uyii din nizu ba. Na iwa yinin ayi mine nana ba, a na iwa yinni ilanza fiu ba.
Na bar ku da salama; ina ba ku salamata. Ba kamar yadda duniya ke bayarwa Nake bayarwa ba. Kada zuciyarku ta baci, kuma kada ku tsorata.
28 Ina lanza, nna bellin minu, 'Nma su ucin, nma kpilu kiti mine tutung.' Andi idi nin sunighe, iba su liburi libo bara ndin cinu ucin du kitin Ncif. Bara Ucife karin akatini.
Kun ji dai na fada maku, 'zan tafi, kuma Zan dawo gare ku'. Idan kuna kaunata, za ku yi farinciki domin za ni wurin Uban, gama Uban ya fi ni girma.
29 Nene nna bellin minu a idutu sa uti, asa imone nin ta ima yinnu.
Yanzu na fada maku kafin ya faru, domin idan ya faru, ku gaskata.
30 Na nma su uliru nanghinu gbardang ba, bara ugo nyii ulele din cinu. Na adi nin likara kitene ning ba,
Ba zan kara magana mai yawa da ku ba, domin mai mulkin duniyan nan yana zuwa. Bashi da iko a kai na,
31 Uyii nan yinno Meng di nin suu Ncife. Ndin su imon ile na Ucife asa atayi nsu, nafo na ana nei uduke. Fitan, dan ti sun kiti kane.”
amma domin duniya ta san cewa ina kaunar Uban, Ina yin daidai abinda Uban ya Umarce ni. Mu tashi mu tafi daga nan.

< Yuhana 14 >