< Luuka 8 >

1 jilyahumile unsiki ndebe pambele kuuti, uYesu alyatengwile kukyula ku mapulo ni fikaaja inga, akidalikila na kupulisia imhola inofu isa vutwa vwa Ngulue na vala kijigho na vavili vakaluta palikimo naghwo,
Bayan wannan sai Yesu ya zazzaga gari da ƙauye, yana wa’azin bisharar mulkin Allah. Sha Biyun nan kuwa suna tare da shi,
2 vule vule na vavadala avange vano vakasosilue kuhuma mumapepo amalamafu ni namu nyinga. valyale ghwe maliya juno akemeluagha Magadalena juno vamwumisie amapepo lekela lubale.
da kuma waɗansu mata waɗanda aka warkar da su daga cututtukansu, da kuma mugayen ruhohi. Cikinsu akwai Maryamu (wadda ake kira Magdalin) wadda aljanu bakwai suka fito daga cikinta.
3 uYoana un'dala ghwa Kusa nu m'baha ghwa Helode uSusana na vadala avange vinga, vano valyahmisie ikyuma javo vavuo.
Da Yowanna matar Kuza, manajan iyalin Hiridus; da Suzana; da waɗansu mata da yawa. Waɗannan mata suna taimaka musu cikin hidima, daga cikin abin da suke da shi na zaman gari.
4 ye ilipugha lya vaanhu likong'anile palikimo, mwevalyale avaanhu vano vakisile kuhuma mumapulo minga akajova navo kwa kutumila ifihwani.
Yayinda taron mai girma na taruwa, mutane kuma daga garuruwa dabam-dabam suna zuwa wurin Yesu, sai ya ba da wannan misali ya ce,
5 unyamughunda akalutile kuvyala imbeju kumughunda, pano akale ivwala imbej jimonga mu isio sikaghwila mu lubale lwa sila avaanhu vakakanya na maghulu, ni njuni sa kukyanya sikalia.
“Wani manomi ya fita domin ya shuka irinsa. Da yana watsa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, aka tattaka su, tsuntsayen sararin sama kuma suka cinye su.
6 imbeju isinge sikaghwila mu lihanga ilyumu sati simelile nakuva mamela ghakaola ulwakuva nakulyale nu vunyefunyefu.
Waɗansu suka fāɗi a kan dutse, da suka tsira sai suka yanƙwane don babu ruwa a wurin.
7 imbeju isinge sikaghila mu mapiki gha manfua, ghope amapiki gha manfua ghakakula palikimo ni mbeju sila sikamelelanila.
Waɗansu kuma suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma tare, sai ƙayan suka shaƙe su.
8 neke imbeju isinge sikaghwila mulihanga lino likanoghile kuhola imeto kijigho kukila. pe baho uYesu ye ajovile isio, akajova ilisio, “ghweni juno ali ni mbughulutu isa kupulika na apulike”
Waɗansu kuma har yanzu, suka fāɗi a ƙasa mai kyau, suka yi girma, suka ba da amfani riɓi ɗari-ɗari, fiye da abin da aka shuka.” Da faɗin haka sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
9 kange avavulanisivua vakamposia uvufumbue vwa kihwani ikio.
Almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
10 uYesu akavamula aakti, Mupelilue uughanike kukila kukagula ulufiso lwa vutwa vwa Ngulue, neke avaanhu avange vilivulanisivua kukihwani kwene, neke kuuti, 'vangalole navangalolaghe kange vangapulike navangakagulaghe'.
Sai ya ce, “Ku ne aka ba sanin asirin mulkin Allah, amma ga sauran mutane kam, ina magana da misalai, saboda, “‘ko da yake suna kallo, ba za su gani ba, ko da yake suna ji, ba za su gane ba.’
11 nu vu vwe vufumbue vwa kihwani iki. imbeju lwe lisio lya Nguluve.
“Ga ma’anar misalin, irin, shi ne maganar Allah.
12 imbeju sila sikaghwila mu lubale lwa sila ava ve vaanhu vano vipulika ilisio, neke pambele umuhosi uSetano itola kutli kuhuma mumwoojo, neke kuuti navangitikilaghe nambe kukagula.
Waɗanda suka fāɗi a kan hanya su ne mutanen da suka ji, amma Iblis, yakan zo ya ɗauke maganar daga zuciyarsu, don kada su gaskata, su sami ceto.
13 kange na sila sinosikaghwila mu lihanga ilyumu ve vaanhu vala vano ikulipulika ilisio na kukulyupila ku lukelo neke vasila malela ghoghoni, vikwitika lwene ku nsiki n'debe nu n'siki ghwa ngelo vighua.
Na kan dutse kuwa, su ne da jin maganar, sukan karɓa da murna, amma ba su da saiwa. Sukan gaskata na ɗan lokaci, amma lokacin gwaji, sai su ja da baya.
14 ni mbeju sila sinosikaghwila mu manfua ve vaavhu vano vikulipulika ilisio, neke pano vighenelela kukula vikong'ana ni mbombele nu vumofu nu vunono vwa vwumi uvu neke navihola imheeke.
Irin da suka fāɗi a cikin ƙaya kuwa, su ne mutanen da suka ji, amma a kwana a tashi, tunanin kayan duniya, da neman arziki, da son jin daɗi, sukan hana su ba da’ya’ya.
15 neke imbeju sila sino sikaghwila mu lihanga ilinono ve vaanhu vala vano ilutila kuvukoola na moojo ghave manono, pano vapulike ilisio vigadilila kange liva panono na kuhola imheeke sa lugudo.
Amma irin da suka fāɗi a ƙasa mai kyau kuwa, su ne mutane masu kyakkyawar zuciya, mai kyau, da suka ji, suka riƙe, suka kuma jimre har suka ba da’ya’ya.”
16 lino nakwale nabe jumo juno ikinga itala na kukujikupikila ni bakuli nambe kukujivika paasi pa kitanda. kisila kuvika itala pakyanya neke kuuti unuubhu ghweni juno ikwingila apate kukujagha.
“Ba mai ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta a cikin tulu, ko kuma ya sa ta a ƙarƙashin gado ba. A maimakon haka, yakan sa ta a kan wurin ajiye fitila, saboda mutane masu shigowa su ga haske.
17 ulwakuva nakwekili kino kikujifisa nakingakagulike, nambe kyokyoni kino kilimulufiso kino nakilikagulika kingave mulumuli.
Ba abin da yake ɓoye da ba za a fallasa ba. Kuma ba abin da yake rufe, da ba za a sani ba, ko a fitar da shi a fili ba.
18 pe lino uvisaghe maaso pano ghuva ghupulikisia. ulwakuva juno ali nakyo, kwamwene ikwongelesevua kukila, neke juno nsila nambe kidebe kila kino alinakyo kilipokua”.
Saboda haka, ku yi tunani da kyau yadda kuke saurara. Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda ba shi da shi kuma, abin da yake tsammani yana da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
19 pambele ung'iina ghwa Yesu na vanyalukolo vakisa kwa mwene navakavelelela ulwakuva ja lipugha lya vaanhu.
Sai uwar Yesu da’yan’uwansa suka zo, domin su gan shi, amma ba su iya zuwa kusa da shi ba, saboda taron.
20 vakampela imhola kuuti “umama ghwako na vanyalukolo vako ali panji pala vilonda kukukwagha uve”
Sai wani ya faɗa masa cewa, “Ga uwarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje suna so su gan ka.”
21 neke uYesu kavamula akati,” umama ghwango na vanyalukoo vango ve vala vano vikulipulika ilisio lya Nguluve na kukulyitika”.
Ya amsa ya ce, “Mahaifiyata da’yan’uwana, su ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma aikata ta.”
22 jikahumile mu kighono kimonga mu fighono fila fino uYesu na vavulanisivua vaake akatogha u kyombo, akavavula,”tulovoke ku mwambo ja vuvili ja malenga lisiva/malenga” vakaling'anisia ikyombo kwave.
Wata rana Yesu ya ce wa almajiransa, “Mu haye zuwa wancan gefen tafkin.” Sai suka shiga jirgin ruwa suka fara tafiya.
23 neke vakatengula kuvuka, uYesu akaghona tuulu, imhepo imbaha jikatengula na kuviika amavingo amavaagha mu lisumbe. amalenga ghakatengula kumema mu kyombo, vakava mu lutalamu ulwa kudwidivala kyongo.
Da suna cikin tafiya, sai barci ya kwashe shi. Sai wata babban iska ta taso kan tafkin, har ruwa ya fara shiga cikin jirgin. Suka shiga babban hatsari.
24 pepano avavulanisivua vake vakisa kwamwene na kukunsisimula, vakatisagha, “Mutwa m'bha! Mutwa m'baha! tuli pipi pifua! akasisimuka na akajidalikila imhepo na mavingo gha malenga fikajigha kukava kimie.
Almajiran suka je suka tashe shi daga barci, suka ce, “Ubangiji, Ubangiji, za mu nutse!” Ya tashi ya kwaɓe iskar da kuma haukar ruwan. Sai ruwan da iskar suka natsu. Kome ya yi tsit.
25 kange akavavula, “ulwitiko lyinu lulikughi?” vakoghopa na kudegha, vakajofesania umuunhu ghweni nu junge, “uju ghwe veeni, juno idalikila na jimhepo na nagha malenga fyope fikun'kunda?”
Sai ya tambayi almajiransa, “Ina bangaskiyarku?” A cikin tsoro da mamaki, suka ce wa junansu, “Wane ne wannan? Yana ba da umarni ga iska da ruwa ma, kuma suna biyayya da shi?”
26 vakafika kumpulo ghwa ghuno vaGelasi ulubale ulwa kunsana ghwa Galilaya.
Suka shiga jirgin ruwa zuwa yankin Gerasenawa da yake a hayin tafkin, daga wajen Galili.
27 uYesu ati ikile na kukanya pa lihanga, umuunhu jumonga kuhuma mu mpulo akatang'ana naghwo, nu muunhu uju alayale ni ngufu sa mapepo amalamafu. ifighono finga naakale kifyala amenda, kange akale naikukala mu nyumba, neke ikala ku mbiipa.
Da Yesu ya sauka daga jirgin, sai ga wani mutum mai aljanu daga garin. Mutumin ya daɗe bai sa tufafi ba, kuma ba ya zama a gida. Yana zama a cikin kaburbura.
28 ati amwaghile uYesu akalila ku lisio na kughua paasi pavulongolo jake. kulisio ilikome akati, nivombile kiki kulyuve, uYesu mwana ghwa Nguluve juno alikukyanya? nikusuuma nungamhumhusiaghe une”
Da ya ga Yesu, sai mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi, ya fāɗi a gabansa, yana ihu cewa, “Ina ruwanka da ni, Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ina roƙonka, kada ka ba ni wahala!”
29 uYesu akaaghavula amapepo amalamafu ghahume kwa muunhu jula, ulwakuva ke kinga ghakampumusiagha nambe kwe kuuti alyale ikungua ni nyololo na kubanua na kuvikua pavulolelesi, akadumulagha ifipinyua na kutwalua na mapepo amalamafu kuhanga kulihaka.
Gama Yesu ya riga ya umarci mugun ruhun ya fita daga mutumin. Sau da yawa mugun ruhun ya sha kamunsa. Ko da yake akan daure shi hannu da ƙafa, da sarƙa, a kuma yi gadinsa, amma yakan tsinke sarƙoƙinsa, aljanun kuma su kore shi zuwa wuraren kaɗaici, inda ba kowa.
30 uYesu akamposia, “ilitavua lyako veve veeni? akamula akati, “Legioni” ulwakuva amapepo minga ghingile kwa mwene.
Yesu ya tambaye shi, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa, “Tuli,” gama aljanu masu ɗumbun yawa ne suna cikinsa.
31 vakaghendelela kukunsuuma nangatuvulaghe kuuti tulute kulina. (Abyssos g12)
Suka yi ta roƙonsa kada yă umarce su su shiga ramin Abis. (Abyssos g12)
32 ilipugha lya ngube lilyale lidimua kukyanya kukidunda, amapepo ghala ghakansuuma aghavule ghingine mu nguve sila, akaghavula kuvomba ndikio. pe
A wurin kuwa, akwai babban garken aladu da suke kiwo a gefen tudu. Aljanun suka roƙi Yesu ya bar su, su shiga cikin aladun, ya kuwa yardar musu.
33 lino amapepo ghala ghakaghuma kwa muunhu jula na kukwingila mu ngube sila, ni lipugha lila likakimbila ku kidunda kino kitoghile kuhanga mulisumbe na kusovelela umuo.
Da aljanun suka fita daga cikin mutumin, sai suka shiga cikin aladun. Garken kuma ya gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, kuma suka nutse.
34 avaanhu vala vano vadimagha ingube sila vati valolile kino kihumile, vakakimbila na kuhmia imhola sila pa mpulo na kufikaaja fya kunji fino fikuvasyuta.
Da masu kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka ruga da gudu zuwa garin da kewaye suka kai labari.
35 avaanhu ye vapulike isio vakaluta kulola kino kihumile, pe vakisa kwa Yesu vakamwagha umuunhu juno amapepo amalamafu ghamuhumile. afwalile vunofu kange alinuluhala lwoni, ikalile pa maghulu gha Yesu pe vakoghopa.
Mutanen kuma suka fito don su ga abin da ya faru. Da suka iso wurin Yesu, sai suka tarar da mutumin da aljanun suka fita daga cikinsa, yana zaune kusa da Yesu sanye da tufafi, kuma cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
36 pepano jumonga mu veene juno akalolile kino kihumile akatengula kukuvapangila avange ndave umuunhu uju juno alyale ilongosivua na mapepo amalamafu vule asosilue.
Waɗanda suka ga abin da faru, suka gaya wa mutanen yadda aka warkar da mai aljanun.
37 avaanhu voni ava mu kighavo kya vagelasi ni mbale sino sikuvasyuta vakansuuma uYesu avuke kuveene ulwakuva valyale nu vwoghofi kyongo. pe akingila mu kyombo ivuka iluta.
Sai dukan mutanen yankin Gerasenawa suka roƙi Yesu ya bar su, don sun tsorata sosai. Sai Yesu ya shiga jirgin ruwa ya tafi.
38 umuunhu jula juno alyahumilue na mapepo amalamafu ghala akansuuma uYesu kuluta naghwope, neke uYesu akam'bula kuuti, 'alute na kujova, “
Mutumin da aka fitar da aljanun daga cikinsa, ya roƙi Yesu don yă tafi tare da shi, amma Yesu ya sallame shi ya ce,
39 gomoka ku nyumba jaako na kuvala ghoni ghala ghano uNguluve akuvombile” umuunhu uju akavuka, na kupulisia mu mpulo ghwoni ghoni ghala ghano uYesu alyavombile vwimila jake.
“Koma gida, ka shaida babban alherin da Allah ya yi maka.” Sai mutumin ya tafi yana faɗin abin da Yesu ya yi masa a duk garin.
40 pe uYesu akalutagha, ilipugha likamwupila, ulwakuva voni valyale vikumughulila.
Da Yesu ya koma, taron suka marabce shi, don dā ma duk suna jiransa.
41 lola akisa umuunhu jumonga ikemelua ghwe Yailo ghwe jumo mu valongosi mu nyumba inyimike ja kufunyila. uYailo akaghua paasi pa maghulu gha Yesu na kukunsuma alute ku nyumba jake,
Sai wani mutum mai suna Yayirus, wani mai mulkin majami’a, ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, yana roƙonsa ya zo gidansa,
42 ulwakuva alyale nu mwana u minja jumo mwene, unya maaka kijigho na ghavili, alyale mu lwa kufua. ye iluta ilipugha likakong'anagha kwa mwene.
domin diyarsa ɗaya tak, wadda ta kai shekara goma sha biyu, tana bakin mutuwa. Da Yesu yake kan hanyarsa, taron mutane masu yawa suka yi ta matsa shi a kowane gefe.
43 umukijuuva juno idanda jilyahumagha ku maka kijigho na ghavili pwe alyale pala alyatumile indalama soni ku vaghanga, neke nakwale juno alyasosie nambe jumo,
A wurin kuwa, akwai wata mace wadda tana da ciwon zubar da jini, har na shekara goma sha biyu, amma babu wanda ya iya warkar da ita.
44 akisile kunsana kwa Yesu akabasia uluvilo lwa mwenda ghwake, kukenyemukila idanda jikaleka kuhuma.
Sai ta zo ta bayansa, ta taɓa bakin rigarsa. Nan da nan, zubar da jininta ya tsaya.
45 uYesu akaposia, “veni juno anayabasisie?” vati vakanile vooni, uPeteli akati, ghwe Ntwa ilipugha lwa vaanhu vinga kyongo vakusyngutile, vikukupita”.
Yesu ya yi tambaya, “Wa ya taɓa ni?” Bayan kowa ya yi musu, sai Bitrus ya ce, “Ubangiji, ai, mutane da yawa suna matsinka ta kowane gefe.”
46 neke uYesu akati, “umuunhu juma anyabasisie, lwakuva nivele nikagwile ingufu sihumile kulyune”.
Amma Yesu ya ce, “Wani ya taɓa ni, na san cewa iko ya fita daga wurina.”
47 umukijuuva ati avwene kuuti nangawesie kufisa kino avombile, akatengula kukwoghopa, akafughama paasi pa maghulu gha Yesu akapulisia pa maaso gha vaanhu voni kino kintwalile umwene kumwabasia na fino asosilue mu lwa kukenyemukila.
Sai macen, da ta ga ba halin ɓoyewa, sai ta fita, jikinta na rawa, ta fāɗi a gabansa. A gaban dukan mutanen, ta faɗi dalilin da ya sa ta taɓa shi, da yadda ta warke nan take.
48 pe pano akati kwamwene, “mwalivango usokile vwimila ulwitiko lwako. ulutaghe nulutengano!
Sai Yesu ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya.”
49 uYesu ye ighendelela kujova isio, umuunhu jumonga iisa kuhuma kunyumba ja mulolelesi ghwa nyumba inyimike ja kufunyila, akati, “umwalivako afwile. nunga ng'asiaghe um'bulanisi”.
Yayinda Yesu na cikin magana har yanzu, sai ga wani daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’ar ya ce, “Kada ka ƙara damun malam, diyarka ta rasu.”
50 neke uYesu ye apulike ndikio, akamwamula akati, “nungoghopaghe' lwene ghitikaghe umwalivo isooka.
Da Yesu ya ji wannan, sai ya ce wa Yayirus, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata, za a kuma warkar da ita.”
51 neke ye ingile mu nyumba ijio, nakam'bulile umuunhu ghweni kukwingila palikimo nu mwene looli ju Peteli, uYohani nu Yakovo, uviise ghwa minja nu ng'iina ghwa mina.
Da ya iso gidan Yayirus, sai ya hana kowa yă bi shi cikin ɗakin, sai dai Bitrus, da Yohanna, da Yaƙub, da kuma mahaifin da mahaifiyar.
52 lino avaanhu vooni vano pwevalyale pala vakava vilila na kuhumia amasio vwimila jaake, neke uYesu akavavula akati? namungajovaghe ilisio, naafwile neke aghonelile lwene”
Ana cikin haka, dukan mutanen kuma sai kuka da makoki suke ta yi, domin yarinyar. Sai Yesu ya ce, “Ka daina yin kuka, ba tă mutu ba, tana barci ne.”
53 neke vakanseka kwa kukumbenapula vakakagwile kuuti afwile.
Sai suka yi masa dariya, da yake sun san cewa, ta mutu.
54 uYesu akan'ola uluvoko umija jula akankemeela fiijo akati, “ghwe mwana ima!”
Amma Yesu ya kama ta a hannu ya ce, “Diyata, tashi.”
55 uvwumi vwake vukan'gomokela pe akima ghu nsiki ghughughuo. akavalaghila akati vampele ikinu ikyakulia.
Ruhunta ya dawo, kuma ta tashi, nan take. Yesu ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
56 avapafi vake vakadegha, neke akavalaghila kuuti navangam'bulaghe nambe muunhu kino kilyahumile.
Iyayenta suka yi mamaki, amma ya ba su umarni kada su faɗa wa kowa abin da ya faru.

< Luuka 8 >