< Luuka 16 >

1 uYesu akavavula avavulanisivua vake, “palyale nu muunhu jumonga m'mofu alyale nu m'baha mu mbombo jake,
Yesu ya ce wa almajiransa, “An yi wani mai arziki wanda aka yi wa manajansa zargin yin banza da dukiyarsa.
2 pe vakampela umm imhola sa m'baha jula kuuti, um'bombi ghwako um'baha itaghania ifyuma fyako. pe ummo akan'kemela akam'bula akati, “kwe kiliku ulyuve kino nipulika? humia imhola ija vuvaha vwako, ulwakuva nungave m'baha kange mu mbombo jango.
Sai ya kira manajan, ya tambaye shi, ‘Me nake ji haka a kanka? Ka kawo lissafin aikinka, domin ba za ka iya cin gaba da aikinka ba.’
3 um'baha jula akijovela mu mwoojo ghwake, nivombe kiki, ulwakuva untwa ghwango ikunivusia mu mbombo jango ija vuvaha? nisila ngufu sa kulima, na kusuma nivona soni.
“Sai manajan ya ce cikin tunaninsa, ‘Maigidana zai kore ni daga aiki, me zan yi? Ba ni da ƙarfin noma, kuma ina jin kunyan yin bara.
4 nikagula lino kyale nivomba kyande vanivusisie mu mbombo jango ja kwimilila avaanhu vanyupile mu nyuma save.
Na san abin da zan yi, don mutane su karɓe ni a gidajensu, bayan an kore ni daga aiki a nan.’
5 pe pano umweimilili jula akavakemhela voni vano visighilua nu ntwa ghwake akam'bula ughwa kwanda, 'ghusighilua ilingi nu ntwa ghwango?'
“Sai ya kira kowane ɗaya da maigidansa yake bin bashi. Ya tambayi na farkon ya ce, ‘Nawa ne maigidana yake bin ka?’
6 akati, 'fighelelo kilundo fya mafuta akam'bula,' tola ilikalataasi lyako ng'ani ng'ani lemba ifijigho fihaano,
“Ya amsa ya ce, ‘Garwar mai na zaitun guda ɗari tara.’ “Manajan ya ce, ‘Ga takardarka, ka zauna maza ka mai da shi ɗari huɗu.’
7 pe akam'bula ujunge najuve ghusighilua ilingi? akati, 'ifighelelo kilundo kimo ifya vutine vwa ngano'. tola ilikalataasi lyako, lemba ifijigho lekela kwoni'.
“Ya kuma tambayi na biyun, ‘Kai fa, nawa ne ake bin ka?’ “Sai ya amsa ya ce, ‘Buhunan alkama dubu.’ “Ya ce, ‘Ga takardarka, ka mai da shi ɗari takwas.’
8 untwa jula akamughinia um'baha jula ulakuva alyavombile nu vukagusi. ulwakuva avaanha va pa iisi iji vali nuvukagusi vyinga kukila avaanha va Nguluve. (aiōn g165)
“Maigidan kuwa ya yabi manajan nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama’yan duniyan nan suna da wayon yin hulɗa da junansu fiye da’yan haske. (aiōn g165)
9 lino une nikuvavula kuuti, muvatangaghe avajinu ni kyuma kino mulinakyo, neke kyande kisilile, mwupilue ku vukalo vwa kusila na kusila. (aiōnios g166)
Ina gaya muku, ku yi amfani da dukiya na wannan duniya, domin ku sami wa kanku abokai. Saboda bayan dukiyar ta ƙare, za a karɓe ku a wuraren zama da sun dawwama. (aiōnios g166)
10 juno mugholofu mu lidebe kyongo iva mugholofu na mulikome. ghwope juno namugholofu mu lidebe naiva mugholofu na mulikome kange.
“Duk wanda ana amincewa da shi cikin ƙaramin abu, ana kuma amincewa da shi cikin babba. Kuma duk marar gaskiya cikin ƙaramin abu, zai zama marar gaskiya cikin babba.
11 nave umue namulyale vagholofu mu kyuma kino na kyakyangani pe ghwevene juno ikuvitika ku kyuma ikya lweli?
In fa ku ba amintattu ne cikin tafiyar da dukiya ta wannan duniya ba, wa zai amince muku da dukiya ta gaskiya?
12 kange nave namulyale vagholofu kutumila ikyuma kya muunhu junge, ghweveni juno ikuvapela sino sinu jumue?
In fa ku ba amintattu ne cikin tafiyar da dukiyar wani ba, wa zai ba ku dukiya naku, na kanku?
13 nakwale um'bombi juno ikuvavombela avatwa vavili, ulwakuva ghukunkalalilagha jumo na kumughana ujunge, nambe kukolana nuju na kum'benapula uju. nungawesie kukum'bombela uNguluve ni kyuma.
“Babu wani bawa mai iya bauta wa iyayengiji biyu ba. Ko dai ya ƙi ɗaya, ya so ɗayan, ko kuwa ya dāge ga yi wa ɗaya bauta, sa’an nan ya rena ɗayan. Ba za ku iya ku bauta wa Allah tare da bauta wa Mammon (wato, Kuɗi) a lokaci ɗaya ba.”
14 pe avafarisayi, vano valyale vinoghua indalama ye vapulike aghuo ghoni vakam'benafula.
Da Farisiyawa masu son kuɗi suka ji wannan duka, sai suka yi wa Yesu tsaki.
15 kange akavavula, “umue mwemwemu mukuvona hwene vanya kyang'ani pa maaso gha vaanhu, neke UNguluve akagwile amoojo ghinu. ulwakuva lino lyimike kwa muunhu liva ng'alasi pa maaso ghwa Nguluve.
Ya ce musu, “Ku ne masu mai da kanku marasa laifi a gaban mutane, amma Allah ya san zuciyarku. Abu mai daraja a gaban mutane, abin ƙyama ne a gaban Allah.
16 indaghilo na vavili pwefilyale kuhanga uYohani panoa akisile. kuhuma unsiki ughuo, imhola inofu ja vutwa vwa Nguluve jikapulisivue, nu muunhu ghweni ighela kukwingila ku ngufu.
“An yi shelar Doka da Annabawa har zuwa lokacin Yohanna. Tun daga lokacin nan, bisharar mulkin Allah ne ake wa’azinta, kowa kuma yana ƙoƙarin kutsa kai ya shiga.
17 neke kihugu ku kyanya ni iisi fivuke kuliko ililembe limo lya ndaghilo likosekane.
Gama ta fi sauƙi sama da ƙasa su shuɗe, da a ce ɗigo guda ɗaya na rubutun, ya fita ya fāɗi daga cikin Doka.
18 ghweni juno ikumuleka un'dala ghwake na kun'toola un'dala ujunge ivwafuka, ghwope juno ikun'toola juno alekilue numughosi ghwake ivwafuka.
“Duk wanda ya saki matarsa ya auri wata mace, zina ne yake yi. Kuma mutumin da ya auri macen da aka sake, zina ne yake yi.
19 palyale nu mmofu jumonga alyafwalile amhenda aghanya sambalau na gha ndalama akale ihovokela uvumofu vwake uvukome.
“An yi wani mutum mai arziki wanda yakan sa tufafi masu ruwan shunayya, da kuma na lallausan lilin, yana kuma cikin rayuwar jin daɗi kullum.
20 nu nkotofu jumonga ilitavua lyake Lasali vakam'biki pa mulyango ghwa kunji kwa mofu jula, alyale ni fikongo.
A ƙofar gidansa kuma akan ajiye wani mai bara, mai suna Lazarus, wanda jikinsa duk gyambuna ne.
21 ghwope akinoghelua kulia ikyakulia kino kikaghwisagha pasi pa mofu jula nasi mbua sikisa sikamumyanga ifikong'o fyake.
Shi kuwa yakan yi marmarin cin abin da yakan fāɗi daga tebur na mai arzikin nan. Har karnuka ma sukan zo su lashe gyambunansa.
22 jikava unkotofu jula akafua, avanyaMhola vakantola kuhanga pakifuva pa Abulahamu. ummofu jula ghwope akafua akasyulua.
“Ana nan, sai mai baran ya mutu, kuma mala’iku suka ɗauke shi zuwa gefen Ibrahim. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi.
23 ye alyale mumuko kuvulungu kula akadindula amaaso ghake akamwagha uAbulahamu kuvutali ali nu Lasali pakifuva kyake. (Hadēs g86)
A cikin jahannama ta wuta, inda yana shan azaba, ya ɗaga kai ya hangi Ibrahim can nesa, da kuma Lazarus a gefensa. (Hadēs g86)
24 akalila akati, 'baba Abulahamu, nisaghile un'sung'e u Lasali asase ulwove lwake mumalenga, alunoghelesie ululimi lwango; ulwakuva nipumusivua mu mwoto ughu.
Sai ya yi masa kira ya ce, ‘Baba, Ibrahim, ka ji tausayina, ka aiki Lazarus ya sa ɗan yatsarsa a ruwa, ya ɗiga mini a harshe saboda in ji sanyi, domin ina shan azaba cikin wannan wuta.’
25 neke uAbulahamu akati, 'mwanago kumbuka kuuti mu vwumi vwako ukupile isako sino nono, nu Lasali vule vule alyapatile inyivi. neke lino alyapa uhuvilisivua, najuve ghupumusivua.
“Amma Ibrahim ya ce, ‘Ka tuna fa ɗana, a lokacin da kake duniya, ka sami abubuwa masu kyau naka, Lazarus kuwa ya sami munanan abubuwa. Amma yanzu ya sami ta’aziyya a nan, kai kuwa kana shan azaba.
26 na kukila aghuo, kuvikilie ilina ilikome pakate jitu kuuti vano vilonda kuluta kulyumue vakunuaghe na vaanhu va kulyumue navangalovokaghe kukwisa kulyusue'
Ban da wannan duka ma, tsakaninmu da kai, akwai wani babban rami da aka yi, yadda waɗanda suke son ƙetarewa daga nan zuwa wurinku, ba za su iya ba, kuma ba mai iya ƙetarewa daga wurinku zuwa wurinmu.’
27 umofu jula akati, 'nisuuma baba Abulahamu kuuti unsung'e ku nyumba kwa baba ghwango.
“Ya amsa ya ce, ‘To, ina roƙonka, ya uba, ka aiki Lazarus zuwa gidan mahaifina,
28 ulwakuva nili navanyalukolo vahano neke avavunge na veene ku vwoghofi piti vope vilikwisa pa mhumhuko apa.
gama ina da’yan’uwana biyar maza. Bari yă ba su gargaɗi, don kada su ma su zo wurin nan mai azaba.’
29 neke uAbulahamu akati, 'kwale uMoose na vavili, valeke vavapulikisie vavuo.
“Ibrahim ya amsa ya ce, ‘Suna da Musa da Annabawa, ai, sai su saurare su.’
30 umofu jula akati, 'Ndali, baba Abulamahu, neke nave angalute umuunhu juno ahumile kuvafue vilaata,
“Sai ya ce, ‘A’a, ya uba, Ibrahim, in dai wani ya tashi daga matattu ya je wurinsu, za su tuba.’
31 neke uAbulahamu akam'bula akati, 'ndeve navikuvapulikisia uMoose na vavili navangampulikisie nambe umuunhu angasyuke kuhuma kuvafue.
“Amma ya ce masa, ‘In ba su saurari Musa da Annabawa ba, kai, ko da wani ya tashi daga matattu ma, ba za su saurare shi ba.’”

< Luuka 16 >