< Luuka 1 >

1 kulyuve mwoghopua Tiofilo avaanhu vinga valembile imhola isa Yesu Kilisite ndavule silyavombike kulyusue.
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 valembile imhola isi ndavule tulyapangilue na vano valyalolile na maaso ghave, navano valyasipulisie kuhuma vuvutengulilo vwake.
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 ulwakuva nilondile vunono uvwakyang'haani vwa mhola sa Yesu vuhuma vuvutengulilo lino najune nivwene lunono kukulembela isi sooni muvutavike.
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 neke ulukagule ulwakyang'haani lwa mbombo sino ukavulanisivue.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 mu fighono fya Helode untwa ghwa Yudea, pwealyale untekesi jumonga juno alyale ikemelua Sakalia ughwa lukolo lwa Abia un'dala ghwake alyahumile muvaliive va Haluni, ni litavua lyake alyale ikemelua Elisabeti.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 voni van valyale vagholofu pa maaso gha Nguluve amaghendele ghale ghasita kukuvapika mundaghilo sooni munjovele ja Mutwa.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 neke navalyale nu mwana ulwakuva uElisabeti alyale mughumba na kukavalilo akuo voni vale vaghogholofijo.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 lino lulyahumile kuuti uSakalia alyale nu Mhepo umwimike kuvutavike vwa Nguluve. akalutile nuvutavike vwa vutekesi kuhumila mu vutavike vwa ludimo lwake.
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 kwevulyale uvutavike uvwa kuvomba mu nyumba ja Nguluve veni umuunhu untekesi, veni idalikila akasalulua ikipugha akingila mu nhumba ja Mutwa akanyanya uvufumba.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 ilipugha lyoni lya vaanhu vakava vikufunya kunji ye vinyanya uvusumba.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 unyaMhola ghwa Mutwa akamwumila na kukwiima ulubale lwa luvoko lwa ndia kufitekelelo kuno vinyanyila uvusumba.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 uSakalia akoghopa ye alwaghile ulutetemo lulyamughwila.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 neke unyaMhola akam'bula kuuti, ulekaghe pikwoghopa Sakalia ulwakuva ulufunyo lwako lupulikike. undala ghwako uElisabeti ikukuholela umwana ilitavua lyake ghukun'kemela Yohani.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 ghuliva nu lukelo na kuhovoka, na vinga vikuhovokela kuholua kwa mwene.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 ulwakuva iliva nu vuvaha kuhuma kwa Mutwa ujuo nanganyisaghe nambe kimonga kino kighasia. looli ingufu sa Mhepo umwimike siiva nu mwene kuhuma pano ali mulileme lwa ng'iina.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 na vaanhu vinga ava Silaeli ilikuvagomosiagha kwa Nguluve uMutwa ghwave.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 ujuo ilikumulongolela uMutwa mu ngufu nu mwojo ndavule alyale uEliya kusambania mu ngufu sa Mhepo uMwimike neve vano navikumwoghopa vighendagha muluhala lwa vano valweli. ikuvavombela ndiki kukuvavika kwa Mutwa avaanhu vano vaghelanisivue vwimila jake.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 uSakalia akam'bula unyaMhola, “niwesia ndani kukagula ili? ulwakuva une nili nsehe nu n'dala ghwango na maka ghake ghali minga kyongo”.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 unyaMhola akamwamula na kumb'ula, une nene Gabilieli, nejuno nikwima pavulongolo pa Nguluve. nisung'ilue kukuvuula, kukuletela iMhola inofu iji.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 kange lolagha, nungajove kinu ghuva kimie nungawesie kujova kuhanga ikighono kila pano isi siva sihumile. ulu lwe ulwakuva ukakunilue kukwitika amasio ghango ghano mu nsiki ghiva ghavombike.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 lino avaanhu valyale vikumughula uSakalia. valyadeghile kuuti alyale itumila unsiki mwinga ku nyumba inyimike ja kufunyila.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 neke ye ahumile kunji, akakunilue kujova navo. pe aveene vakakagula kuuti, luvonike lumonga mu nyuma inyimike neke umwene akava ihufia lumonga na mavoko. akajigha kinunu.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 ye fisilile ifighono fyakuvomba imbombo jakilekesi ayavukile kugomoka kunyumba jake.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 pambele uSakalia akavuja kukaja kuhuma ku mbombo sake sakitekesi un'dala ghwake akava n'kunue, akifisa amesi ghahaano akajova.
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 “ulwakuva lwe luno uMutwa ambombile une ye andolile kulughano lwoni kukumbusikisia isoni pa maaso gha vaanhu”
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 ye ghufikile umwesi ghwa n'tanda pavukunue vwa Elisabeti uNguluve akatuma unyaMhola uGabilieli kuluta mu iisi ja Galilaya ilitavua ilinge Nasaleti,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 kwa mhinja juno akatambulwagha Maliya. kwa mhinja juno alyatunilue nu mughosi ilitavua lyake ghwe Yosefu. umuholua mukikolo kya Davidi nilitavua lya mhinja akakemeluagha ghwe Maliya.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 unyaMhola ye afikile akati, “nikukuhungila uve ghwe juno usungukilue nu Mutwa, uMutwa alinuve;
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 amasio ghanyaMhola ghaka mangajisia kyongo mu mwojo ghwake na alyaghamanyile kiki unyaMhola ihungila hungila iji kidegho.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 unyaMhola akam'bula “nungoghopaghe Maliya ulwakuva uNguluve akusungukile.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 lolagha ghuva nu vukunue, ghupapagha umwana neke ghukun'kemelagha ilitavua ghwe Yesu.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 iliva m'baha ikemeluagha mwana ghwa juno alikukyanya kyongo, uMutwa uNguluve neke ikumpelagha ikitengo kya vutwa kya Davidi uvuse.
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 itemagha uvutwa mu lukolo lwa Yakovo uvusila nakusila lusiku. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 uMaliya akam'bula unyaMhola ili, iva ndani ulwakuva une nanighelile kuvwafuka nu mughosi ghwoghwoni?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 unyamhola akamwamula akam'bula “uMhepo uMwimike ikwisa kulyuve. ni ngufu sa juno alikukyanya kyongo sikwisa kulyuve. pe lino umwimike juno iholua ikemeluagha mwana ghwa Nguluve.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 lolagha ulukololuo uElisabeti alinuukunue vwa mwana mufighono fyake fya vughogholo, ughu ghwe mwesi ghwa n'tanda juno valyatile mughumba.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 ulwakuva kwa Nguluve nakwekili kino kimuulemile”
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 uMaliya akajova akati, une nilim'baanda ghwa Mutwa neke luuleke luve luve kulyune ndavule ujovile” pe pano unyaMhola akavuka iluta.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 ye fikikile ifighono nde filingi uMaliya avuka ng'haning'habi na kuluta ku iisi jimonga jino jale nyafidunda, ija Yudea.
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 ukuo akingila mu nyumba ija Sakalia na kumwungila uElisabeti,
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 lino pe lulyahumile kuuti,” uElisabeti ye apulike uluhungilo lwa Maliya. umwana mu lileme akaomoka tomoka, neke uElisabeti ingufu isa Mhepo uMwimike sikamwisila.
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 pe akatengula pijova kungufu akati, “ufunyilue uve mukighavo kya vakijuuva najumwana juno alimulileme lyako afunyilue.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 neke lulindani kulyune ungiina ghwa Mutwa lunoghile pikwisa kulyune?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 ulwakuva lolagha ye lupulikike mu mbughulutu sango ilisio lya kuhungila kulyuve umwana mulileme lyango atomwike nu lukelo.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 neke afunyilue umukijuva jula juno alyitike kuuti vulyahumila uvya kyang'haani vwa sino alyavulilue kuhuma kwa Mutwa”.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 uMaliya akati, inimbula jango jikunfunya uMutwa,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 naghumwojo ghwango ghuvovwike mwa Nguluve umpoki ghwango.
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 ulwakuva avulolile uvukotofu vwa m'banda ghwake umhinja. lolagha kuhuma mu fisina fyoni vikughonelagha nilifunyua.
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 ulwakuva umwene unya sooni avombile sino mbaha kylyune. ni litavua lyake ilyimike.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 uvukola vwake kuhuma ikisina ni kisina ku vano vikumwopa umwene.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 avonisie ingufu mu luvoko lyake avapalanisie vala vano vakighiniagha mu masaghe gha mooja ghave.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 avisisie paasi avana va vatwa kuhuma mufitengo fyave ifya vutwa na kukuvatosia kukyanya vano vakotofu.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 alyavapelile avanya njala ifinu ifi nono looli avamofu avadagile na mavoko gheene.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 ahumisie uvutangilisi kwa Isilaeli um'bombi ghake, neke akumuke kuvonesia uvuhugu.
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 (ndavule alyajovile kuvanhaata vitu) kwa Abulahamu ni fisina fyake kuvusila na kusila” (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 uMalia alikalile nu Elisabeti hwene mesi ghatatu pepano akagomoka ku nyumba ja mwene.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 lino unsiki ghulyafikile ughwa Elisabeti kupaapa umwana un'dimi.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 avabading'ani vake na vanyalukolo vake valyapulike ndavule uMutwa atupelanisie mu vuhugu vwake, kange vakahovoka palikimo nu mwene.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 lino kilyahumile ikighono kya lekela kwoni valisile kukivungo najumwana lulyanoghile vampele ilitavua lyake ghwe Sakalia kulwiho lwa vise.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 looli ung'ina akamula akati, “ndali” ikemelua ghwe Yohani”
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 vakam'bula napwale nambe jumo mulukolo juno itambulua ku litavua ili”
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 pe vakam'bombela ikimanyilo uvise kuuti, umwene iti ilitavua akemelue veni.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 uvise akalonda ikisegho akalemba “ilitavua ghwe Yohani” voni vakadegha ku ili
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 ku kenyemukila umulomo ghake ghukadinduka nu lumili lwake lukava vuleka akajova na kukumughinia uNguluve
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 uludwesi lukavisila voni vano valikalile pipi navoimbombo isio sikakwilana mu iisi jooni ja fidunda fya Yudea,
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 na voni vano valyaghapulike vakaghagadilila mu mwoojo ghave, vakati umwana uju ghwa ndani ndani?” ulwakuva uluvoko lwa Mutwa lulyale palikimo naghwo.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 ivise ghwa Sakalia akapeluula ingufu nu Mhepo uMwimike akatengula kuhumia uvuvili akatisagha,
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 aghinwaghe uMutwa, uNguluve ghwa Isilaeli, ulwakuva atangile kange na kukuvavanga avaanhu vake.
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 atupelile uvupoki kuhuma mu nyumba ja nyambombo ghwake u Davidi, kuhuma mukikolo kya m'bombi ghwake uDavidi.
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 ndavule alyajovile mumulomo ghwa vavili vake vano kwevalyale kuhuma kuvukuulu. (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 alatupoka kuhuma kuvalugu viitu na kuhuma mumavoko ghavaanhu vooni vano vikutukalalila.
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 alavomba ndiki kuvonesia ulusungu kuvanhaata vitu na kukumbuka ululaghilo lwake ulwimike.
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 ulujigho luno alayjovile kwa Abulahamu unhaata ghwitu.
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 alyajighile na kunkangasia kuuti lunoghile pikum'bombela umwene kisila vwoghofi pano tupokilue pihuma mumavoko ghavalugu viitu.
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 muvwimike na muvagholofu uvwakyang'haani pa maaso ghake ni fighono fyake fyoni.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 Ena, najuve mwana ghukemeluagha uli mb'ili ghw ajuno ali kukyanya fiijo ulwakuva alyaghendelelagha ku maaso ghwa Mutwa kuuti ikuvavonesia isila. neke kukunosekesia isila avaanhu pano ikwisagha umwene.
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 kukuvavula avaanhu vake kuuti valapyanilwagha valavuvunagha uvupoki kusila kusila ja vupoki vwa nyfi saave.
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 ili lilyahumile ulwakuva ja lusungu lwa Nguluve ghwitu ulwakuva ilijuva kuhuma kukyanya likutwisila.
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 kukutumulikila ku vano vikalile mu ng'isi nu lumwighighi ghwa vafue alavomba ndiki kulongosia amaghulu ghitu kusila ja lutengano.”
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 lino umwana jula akakula na kuva nyangufu mwa Mhepo uMwimike. alikalile kulihaka kuhanga unsiki ghuno akavonekagha ku vaSilaeli.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luuka 1 >