< Від Івана 13 >

1 Перед святом же Пасхи Ісус, знавши, що настала годи́на Йому́ перейти до Отця з цього світу, полюбивши Своїх, що на світі були́, до кінця полюбив їх.
Ana gab da Bikin Ƙetarewa. Yesu kuwa ya san cewa lokaci ya yi da zai bar wannan duniya, yă koma wurin Uba. Da yake ya ƙaunaci waɗanda suke nasa a duniya, yanzu kuwa ya nuna musu cikakkiyar ƙaunarsa.
2 Під час же вече́рі, як диявол уже був укинув у серце синові Си́мона — Юді Іскаріотському, щоб він видав Його́,
Ana cikin cin abincin yamma, Iblis kuwa ya riga ya zuga Yahuda Iskariyot, ɗan Siman yă bashe Yesu.
3 то Ісус, знавши те, що Отець віддав все Йому в руки, і що від Бога прийшов Він, і до Бога відходить,
Yesu kuwa ya san cewa, Uba ya sa dukan abubuwa a ƙarƙashin ikonsa, ya kuma san cewa daga Allah ya zo, zai kuma koma wurin Allah;
4 устає від вечері, і здіймає одежу, бере рушника́ й підпері́зується.
saboda haka ya tashi daga cin abincin, ya tuɓe rigarsa ta waje, ya ɗaura tawul a ƙugunsa.
5 Пото́му налив Він води до вмива́льниці, та й зачав обмивати ноги учням, і витирати рушнико́м, що ним був підпере́заний.
Bayan haka, sai ya zuba ruwa a cikin kwano, sa’an nan ya fara wanke ƙafafun almajiransa, yana sharewa da tawul wanda ya ɗaura.
6 І підходить до Си́мона Петра, а той каже Йому: „Ти, Господи, ми́тимеш но́ги мені?“
Ya zo kan Siman Bitrus, wanda ya ce masa, “Ubangiji, kai za ka wanke ƙafafuna?”
7 Ісус відказав і промовив йому: „Що́ Я роблю́, ти не знаєш тепер, але опісля́ зрозумієш“.
Yesu ya amsa ya ce, “Yanzu ba ka fahimci abin da nake yi ba, amma nan gaba za ka gane.”
8 Говорить до Нього Петро: „Ти повік мені ніг не обмиєш!“Ісус відповів йому: „Коли́ Я не вмию тебе, — ти не матимеш частки зо Мною“. (aiōn g165)
Sai Bitrus ya ce, “Faufau, ba za ka taɓa wanke ƙafafuna ba.” Yesu ya amsa ya ce, “Sai na wanke ka, in ba haka ba, ba ka da rabo a gare ni.” (aiōn g165)
9 До Нього проказує Си́мон Петро: „Господи, — не самі мої но́ги, а й руки та го́лову!“
Sai Siman Bitrus ya ce, “To, Ubangiji, ba ƙafafuna kaɗai ba har ma da hannuwana da kaina kuma!”
10 Ісус каже йому: „Хто обмитий, тільки но́ги обмити потребу́є, бо він чистий увесь. І ви чисті, — та не всі“.
Yesu ya amsa ya ce, “Wanda ya riga ya yi wanka yana bukata yă wanke ƙafafunsa ne kawai; dukan jikinsa yana da tsabta. Ku kuwa kuna da tsabta, ko da yake ba kowannenku ba.”
11 Бо Він знав Свого зра́дника, тому то сказав: „Ви чисті не всі“.
Gama ya san wanda zai bashe shi, shi ya sa ya ce, “Ba kowa ba ne yake da tsabta.”
12 Коли ж пообмива́в їхні но́ги, і одежу Свою Він надів, засів зно́ву за стіл і промовив до них: „Чи знаєте ви, що́ Я зробив вам?
Da ya gama wanke ƙafafunsu, sai ya sa tufafinsa ya koma wurin zamansa. Ya tambaye su ya ce, “Kun fahimci abin da na yi muku?
13 Ви Мене називаєте: Учитель і Госпо́дь, — і добре ви кажете, бо Я є.
Kuna ce da ni ‘Malam’ da kuma ‘Ubangiji,’ daidai ne kuwa, gama haka nake.
14 А коли обмив ноги вам Я, Госпо́дь і Вчитель, то повинні й ви один о́дному ноги вмивати.
Da yake ni da nake Ubangijinku da kuma Malaminku, na wanke ƙafafunku, haka ku ma ya kamata ku wanke ƙafafun juna.
15 Бо то Я вам при́клада дав, щоб і ви те чинили, як Я вам учинив.
Na ba ku misali domin ku yi yadda na yi muku.
16 Поправді, поправді кажу́ вам: Раб не більший за пана свого́, послане́ць же не більший від того, хто вислав його.
Gaskiya nake gaya muku, ba bawan da ya fi maigidansa, ko ɗan saƙon da ya fi wanda ya aike shi.
17 Коли знаєте це, то блаженні ви, якщо таке чините!
Yanzu da kuka san waɗannan abubuwa, ku masu albarka ne, in kuka yi su.
18 Не про всіх вас кажу́. Знаю Я, кого вибрав, але щоб збуло́ся Писа́ння: „Хто хліб споживає зо Мною, підняв той на Мене п'яту́ свою!“
“Ba dukanku nake nufi ba; na san waɗanda na zaɓa. Wannan kuwa don a cika Nassi ne da ya ce, ‘Wanda ya ci burodina tare da ni ya tasar mini.’
19 Уже тепер вам кажу́, перше ніж те настане, щоб як станеться, ви ввірували, що то Я.
“Ina faɗa muku yanzu tun kafin yă faru, domin in ya faru, ku gaskata cewa ni ne Shi.
20 Поправді, поправді кажу́ вам: Хто приймає Мого посланця́, той приймає Мене; хто ж приймає Мене, той приймає Того, Хто послав Мене!“
Gaskiya nake gaya muku, ‘Duk wanda ya karɓi wani da na aiko, ni ne ya karɓa ke nan. Kuma duk wanda ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne.’”
21 Промовивши це, затривожився духом Ісус, і осві́дчив, говорячи: „Поправді, поправді кажу́ вам, що один із вас видасть Мене!“
Bayan Yesu ya faɗi haka, sai ya yi juyayi a ruhu, ya kuma furta cewa, “Gaskiya nake gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.”
22 І озиралися учні один на одно́го, непевними бувши, про кого Він каже.
Almajiransa suka dubi juna, suka rasa ko da wa yake.
23 При столі, при Ісусовім лоні, був один з Його учнів, якого любив Ісус.
Ɗaya daga cikin almajiran Yesu wanda yake ƙauna kuwa, yana zaune kusa da shi.
24 От цьому кивну́в Си́мон Петро та й шепну́в: „Запитай, — хто б то був, що про нього Він каже?“
Sai Siman Bitrus ya taɓa wannan almajirin ya ce, “Tambaye shi, wa yake nufi?”
25 І, пригорну́вшись до ло́ня Ісусового, той говорить до Нього: „Хто́ це, Господи?“
Shi kuwa da yake jingine kusa da Yesu, ya ce, “Ubangiji, wane ne?”
26 Ісус же відказує: „Це той, кому, умочивши, подам Я куска́“. І, вмочивши куска́, подав синові Си́мона, — Юді Іскаріо́тському!
Yesu ya amsa ya ce, “Shi ne wanda zan ba shi gutsurin burodin nan sa’ad da na tsoma cikin kwanon.” Da ya tsoma gutsurin burodin, sai ya ba wa Yahuda Iskariyot, ɗan Siman.
27 За тим же куско́м тоді в нього ввійшов сатана́. А Ісус йому каже: „Що́ ти робиш — роби швидше“.
Nan take bayan Yahuda ya karɓi burodin, sai Shaiɗan ya shige shi. Sai Yesu ya ce masa, “Abin nan da kake niyyar yi, ka yi shi maza.”
28 Але жоден із тих, хто був при столі, того не зрозумів, до чо́го сказав Він йому.
Amma ba wani a wurin cin abincin da ya fahimci dalilin da ya sa Yesu ya faɗa masa haka.
29 А тому́, що тримав Юда скриньку на гроші, то деякі ду́мали, ніби каже до нього Ісус: „Купи, що потрібно на свято для нас“, або щоб убогим подав що.
Da yake Yahuda ne ma’aji, waɗansunsu suka ɗauka Yesu yana ce masa yă sayi abin da ake bukata don Bikin ne, ko kuwa yă ba wa matalauta wani abu.
30 А той, узявши кусок хліба, зараз вийшов. Була ж ніч.
Nan da nan da Yahuda ya karɓi burodin, sai ya fita. A lokacin kuwa dare ya yi.
31 Тоді, як він вийшов, промовляє Ісус: „Тепер ось просла́вивсь Син Лю́дський, і в Ньому просла́вився Бог.
Da ya tafi, sai Yesu ya ce, “Yanzu ne aka ɗaukaka Ɗan Mutum aka kuma ɗaukaka Allah a cikinsa.
32 Коли в Ньому прославився Бог, то і Його Бог просла́вить у Собі, і зараз прославить Його!
In kuwa Allah ya sami ɗaukaka a cikin Ɗan, Allah kuwa zai ɗaukaka Ɗan zuwa ga zatinsa, zai kuma ɗaukaka shi nan take.
33 Мої дітоньки, не довго вже бути Мені з вами! Ви шукати Мене будете, але́ — як сказав Я юдеям: „Куди Я йду, туди ви прибути не можете“, — те й вам говорю́ Я тепер.
“’Ya’yana, zan kasance da ku na ɗan ƙanƙani lokaci ne. Za ku neme ni. Kuma kamar yadda na gaya wa Yahudawa, haka nake gaya muku yanzu. Inda zan tafi, ba za ku iya zuwa ba.
34 Нову́ заповідь Я вам даю: Любіть один о́дного! Як Я вас полюбив, так любіть один о́дного й ви!
“Sabon umarni nake ba ku. Ku ƙaunaci juna. Kamar yadda na ƙaunace ku, ku ma ku ƙaunaci juna.
35 По то́му пізнають усі, що ви учні Мої, як бу́дете мати любов між собою“.
Ta haka kowa zai san cewa ku almajiraina ne, in kuna ƙaunar juna.”
36 А Симон Петро Йому каже: „Куди, Господи, ідеш Ти?“Ісус відповів: „Куди Я йду, туди ти́ тепер іти за Мною не можеш, але по́тім ти підеш за Мною“.
Siman Bitrus ya tambaye shi ya ce, “Ubangiji ina za ka?” Yesu ya amsa ya ce, “Wurin da za ni, ba za ka iya zuwa yanzu ba, amma za ka bi ni daga baya.”
37 Говорить до Нього Петро: „Чому, Господи, іти за Тобою тепер я не мо́жу? За Те́бе я душу свою́ покладу́!“
Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, don me ba zan binka yanzu ba? Zan ba da raina saboda kai.”
38 Ісус відповідає: За Ме́не покладе́ш ти душу свою́? Поправді, поправді кажу́ Я тобі: Півень не заспіває, як ти тричі зречешся Мене́.
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Anya, za ka iya ba da ranka saboda ni? Gaskiya nake faɗa maka, kafin zakara yă yi cara, za ka yi mūsun sanina sau uku!

< Від Івана 13 >