< Від Луки 5 >

1 І сталось, як народ товпивсь до Него слухати слово Боже, Він стояв коло озера Генисарецького.
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
2 І побачив два човни, що стояли край озера, рибалки ж, одійшовши від них, полоскали неводи.
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
3 Ввійшовши ж ув один з човнів, що був Симонів, просив його від землі відчалити трохи. І сівши, навчав народ із човна.
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
4 Як же перестав глаголати, рече до Симона: Поступи на глибінь, та закиньте неводи ваші на ловитву.
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
5 І озвавшись Симон, каже Йому: Наставниче, всю ніч трудившись, нїчого не піймали ми; тільки ж, по слову Твоєму, закину невода.
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
6 І, се зробивши, вловили пребагато риби; роздер ся ж невід їх,
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
7 і махнули вони на товаришів своїх, що були в другому човні, щоб прийшли помогти їм. І прийшли вони, й сповнили обидва човни, так що потопали вони.
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
8 Бачивши ж Симон Петр, припав до колїн Ісусових, кажучи: Йди від мене: бо я чоловік грішний. Господи.
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9 Страх бо обняв його і всіх із ним од улову риби, що вловили.
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 Так само й Якова і Йоана, синів Зеведеєвих, що були спільниками Симоновими. І рече до Симона Ісус: Не лякай ся, від нині людей ловити меш.
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11 І пригнавши вони човни свої до берега, та покинувши все, пійшли слідом за Ним.
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
12 І сталось, як був Він ув однім городі, аж ось чоловік увесь у проказі. І, побачивши Ісуса, упавши на лице, благав Його, кажучи; Господи, коли хочеш, можеш мене очистити.
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
13 І простягши Він руку, приторкнувсь до него, глаголючи: Хочу, очистись. І зараз проказа покинула його.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
14 І наказав Він йому нікому не говорити, а, пійшовши, покажи себе священикові та принеси за очищеннє твоє, як звелїв Мойсей, на сьвідкуваннє їм.
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
15 Та слово про Него розійшлось тим більш, і насходилось народу пребагато слухати й сцїлятись у Него від недуг своїх.
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
16 Він же виходив у пустиню та молив ся.
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
17 І сталось одного дня, що Він учив, і сиділи Фарисеї та учителї закону, що; поприходили з усіх сїл Галилейських та Юдейських і з Єрусалиму, й сила Господня була на сцїленнє їх.
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
18 І ось мужі принесли на постелї чоловіка, що був розслаблений, і шукали, як би внести його та положити перед Ним.
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 І, не знайшовши, як би внести його кріз натовп, вилїзли на хату, й кріз черепяну стелю спустили його з постїллю в середину перед Ісуса.
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
20 І, бачивши віру їх, рече йому: Чоловіче, оставляють ся тобі гріхи твої.
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
21 І почали міркувати письменники та Фарисеї, кажучи: Хто сей, що говорить хулу? Хто може оставляти гріхи, як тільки один Бог?
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
22 Постерігши ж Ісус думки їх і озвавшись, рече до них: Що ви говорите в серцях ваших?
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
23 Що легше? сказати: Оставляють ся тобі гріхи твої; або сказати: Встань та й ходи?
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
24 От же, щоб знали ви, що власть має Син чоловічий на землі оставляти гріхи, розслабленому: Тобі глаголю: Устань, і, взявши постїль твою, йди до дому твого.
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
25 І зараз уставши перед ними й узявши на чому лежав, пійшов до дому свого, прославляючи Бога.
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
26 І острах обняв усїх, і прославляли Бога, й сповнили ся страхом, кажучи: Що бачили предивне сьогодні.
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
27 А після сього вийшов, і побачив митника на ймя Левію, сидячого на митниці, і рече йому: Йди слідом за мною.
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
28 І, зоставивши все, уставши пійшов слїдом за Ним.
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
29 і справив гостину велику Левій Йому у господі своїй, і було там багато митників і инших, що свдїли з ними.
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
30 І нарікали письменники їх та Фарисеї на учеників Його, кажучи: На що з митниками та грішниками їсте й пете?
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
31 І озвавшись Ісус, рече до них: Не треба здоровому лікаря, а недужому.
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
32 Не прийшов я кликати праведників, а грішників до покаяння.
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 Вони, ж казали до Него: Чого ж ученики Йоанові постять часто й молять ся, так само й Фарисейські, Твої ж їдять і пють?
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
34 Він же рече до них: Чи зможете синів весільних, поки жених з ними, заставити постити?
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
35 Прийдуть же днї, що візьмуть жениха від них, тоді постити муть у ті дні.
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
36 Сказав же й приповість до них; Що ніхто латки з одежини нової не пришиває до одежини старої; коли ж нї, то й нову розідре, й старій не личить латка з нового.
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
37 І ніхто не наливав вина нового в бурдюки старі; коли ж ні, порве нове вино бурдюки, й вино витече, й бурдюки пропадуть.
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
38 А вино нове в бурдюки нові наливають, то й буде все ціле.
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
39 Ніхто, пивши старе, не бажав зараз нового; каже бо: Старе лучче.
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< Від Луки 5 >