< Від Луки 19 >

1 І вийшовши проходив через Єрихон.
Yesu ya shiga Yeriko, yana ratsa ta cikinta.
2 І ось чоловік, на ймя званий Закхей, а був він старший між митниками, й був заможний.
Akwai wani mutum a garin, mai suna Zakka. Shi shugaban masu karɓar haraji ne, mai arziki kuma.
3 бачити Ісуса, хто Він, та не зміг за народом, бо малого був вросту.
Ya so yă ga ko wane ne Yesu, amma saboda taron, bai iya ba, domin shi gajere ne.
4 побігши наперед, вилїз на шовковицю, щоб подивитись па Него; бо туди мав проходити.
Saboda haka, ya yi gaba da gudu, kuma ya hau itacen sikamo, don yă gan shi, tun da Yesu zai bi wannan hanyar ne.
5 як прийшов на те місце, споглянувши Ісус, побачив його, й рече до него: Закхею, злїзь боржій додолу; сьогодні бо в дому твоїм треба мені бути.
Da Yesu ya iso wurin, sai ya ɗaga ido sama, ya ce masa, “Zakka, ka yi maza ka sauka. Ni kam, dole in sauka a gidanka yau.”
6 І злїз він боржш, і прийняв Його радїючи.
Sai ya sauka nan da nan, ya karɓe shi da murna.
7 І бачивши всї, нарікала кажучи: Що до грішника чоловіка пійшов у гостину.
Dukan mutane suka ga haka, kuma suka fara gunaguni, suka ce, “Ya je don yă zama baƙon ‘mai zunubi.’”
8 Ставши ж Закхей, каже до Господа: Ось половину достатку мого, Господи, даю вбогим; і коди кого чим обидив, віддаю вчетверо.
Amma Zakka ya tashi a tsaye, ya ce wa Ubangiji, “Duba, Ubangiji! Nan take, rabin dukiyar da nake da shi, na ba wa matalauta. In kuma na taɓa cutan wani, a kan wani abu, zan mayar da shi ninki huɗu.”
9 Рече ж до него Ісус: Що сьогоднї спасеннє домові сьому сталось, бо й він син Авраамів:
Sai Yesu ya ce masa, “Yau, ceto ya zo gidan nan, domin wannan mutum shi ma ɗan Ibrahim ne.
10 прийшов бо Син чоловічий, щоб шукати й спасати погибше.
Saboda Ɗan Mutum ya zo ne, domin yă nemi abin da ya ɓata, yă cece shi kuma.”
11 Як же слухали вони се, додавши сказав приповість: бо був Він близько Єрусалиму, й думали вони, що зараз має царство Боже явитись.
Yayinda suna cikin sauraron wannan, sai ya ci gaba da gaya musu wani misali, domin ya yi kusa da Urushalima, kuma mutanen suna tsammani mulkin Allah zai bayyana, nan da nan.
12 Рече ж оце: Один чоловік значного роду йшов у землю далеку прийняти собі царство, та й вернутись.
Ya ce, “Wani mutum mai martaba ya tafi wata ƙasa mai nisa don a naɗa shi sarki sa’an nan ya dawo.
13 Покликавши ж десять слуг своїх, дав їм десять мин срібла, та й сказав до них: Орудуйте, поки прийду.
Saboda haka ya kira bayinsa goma ya ba su mina goma. Ya ce, ‘Ku yi kasuwanci da kuɗin nan, sai na dawo.’
14 Мішане ж його ненавиділи його, й післали посли слїдом за ним, кажучи: Не хочемо сього, щоб царював над вами.
“Amma talakawansa suka ƙi shi, sai suka aikar da wakilai bayansa, domin su ce, ‘Ba mu son wannan mutum ya zama sarkinmu.’
15 І сталось, як вернув ся він, прийнявши царство, сказав прикликати собі слуг тих, що дав їм срібло, щоб знати, хто що з'орудував.
“Duk da haka, aka naɗa shi sarki, sa’an nan ya dawo gida. Sai ya aika aka kira bayin da ya ba su kuɗin, don yă san ribar da suka samu.
16 Прийшов же первий, кажучи: Пане, мина твоя приробила десять мин.
“Na fari ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar goma.’
17 І рече йому: Гаразд, добрий слуго. що у найменшому вірен був єси, то май власть над десятьма городами.
“Maigidan ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawana mai kirki! Tun da ka yi aminci a kan abu ƙanƙani, ka yi riƙon birane goma.’
18 І приступив другий, кажучи; Пане, мина твоя зробила пять мин.
“Na biyun ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar biyar.’
19 Рече ж і сьому: І ти будь над пятьма городами.
“Maigidansa ya ce, ‘Kai ka yi riƙon birane biyar.’
20 Приступив і инший, кажучи: Пане, ось мина твоя, котру я мав сховану в хустцї:
“Sai wani bawan ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, ga minarka. Na ɓoye shi a wani ɗan tsumma.
21 боявсь бо тебе, що ти чоловік жорстокий: береш, чого не клав єси, і жнеш, чого не сіяв.
Na ji tsoronka, don kai mai wuyan sha’ani ne. Kakan ɗauki abin da ba ka ajiye ba, kakan kuma yi girbin abin da ba ka shuka ba.’
22 Рече ж йому: З уст твоїх судити му тебе, лукавий слуго. Знав єси, що я чоловік жорстокий: беру, чого не клав, і жну, чого не сїяв;
“Sai maigidansa, ya amsa ya ce, ‘Zan hukunta ka a kan kalmominka, kai mugun bawa! Ashe, ka san cewa ni mai wuyan sha’ani ne, nakan ɗauka abin da ban ajiye ba, ina kuma girbin abin da ban shuka ba?
23 а чом же не дав єси срібла мого у міняльню? і я, прийшовши, в лихвою виміг би його.
Don me ba ka sa kuɗina a wajen ajiya, don in na dawo, in sami riba a kai ba?’
24 І рече стоячим коло него: Візьміть від него мину, а дайте маючому десять мин.
“Sai ya ce wa waɗanda suke tsaye a wajen, ‘Ku karɓi minarsa ku ba wa wanda yake da mina goma.’
25 І казали йому: Пане, має десять мин.
“Suka ce, ‘Ranka yă daɗe, ai, yana da guda goma ko!’
26 Глаголю бо вам: Що всякому маючому дасть ся, від немаючого ж і що мав, візьметь ся від него.
“Ya amsa ya ce, ‘Ina gaya muku, duk wanda yake da abu, za a ƙara masa. Amma wanda ba shi da shi kuwa, ko abin da yake da shi ma, za a karɓe.
27 А ворогів моїх тих, що не хочуть, щоб царював над ними, приведіть сюда, та й повбивайте передо мною.
Amma waɗannan abokan gābana, waɗanda ba su so in zama sarkinsu ba, ku kawo su nan, ku karkashe su, a gabana.’”
28 І, промовивши се, пійшов далїй, ідучи в Єрусалим.
Bayan Yesu ya yi wannan magana, sai ya yi gaba zuwa Urushalima.
29 І сталось, як наближавсь до Витфагиї та Витаниї, до гори, званої Оливної, післав двох з учеників своїх,
Da ya kai kusa da Betfaji da Betani, a tudun da ake kira Dutsen Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, ya ce musu,
30 глаголючи: Ідїть у село, що перед вами, у котре ввійшовши, знайдете осля привязане, що на него ніхто з людей ніколи не сідав. Одвязавши його, приведіть.
“Ku je ƙauyen da yake gaba da ku. Da kuna shiga, za ku tarar da wani ɗan jaki, wadda ba wanda ya taɓa hawa, a daure a wurin. Ku kunce shi ku kawo nan.
31 І коли хто вас поспитає: На що одвязуєте? так скажіть йому: Що Господеві треба його.
In wani ya tambaye ku, ‘Don me kuke kunce shi?’ Ku ce masa, ‘Ubangiji yana bukatarsa.’”
32 Пійшовши ж послані, знайшли, як Він сказав їм.
Waɗanda aka aika su yi gaba suka tafi, suka kuwa tarar kamar yadda ya gaya musu.
33 Як же одвязували вони осля, казали господарі його до них: На що одвязуєте осля?
Suna cikin kunce ɗan jakin, sai masu ɗan jakin suka ce musu, “Don me kuke kunce shi?”
34 Вони ж сказали: Господеві його треба.
Suka amsa suka ce, “Ubangiji ne na bukatarsa.”
35 І привели його до Ісуса; й, накинувши свою одежу на осля, посадили Ісуса.
Suka kawo shi wurin Yesu. Suka sa rigunarsu a kan ɗan jakin, sa’an nan suka sa Yesu a kai.
36 Як же Він їхав, простилали одежу свою по дорозі.
Yana cikin tafiya, sai mutane suka shimfiɗa rigunarsu a kan hanya.
37 Коли ж вже наближив ся Він до збочу гори Оливної, почало все мно-жество учеників радуючись хвалити Бога голосом великим за всї чудеса, що бачили,
Da ya yi kusa da wurin da hanyar ta gangara zuwa Dutsen Zaitun, sai dukan taron almajirai suka fara yabon Allah, da muryoyi masu ƙarfi, da murna, saboda dukan ayyukan banmamaki da suka gani. Suna cewa,
38 говорячи: Благословен грядущий пар в імя Господнє; впокій на небі, і слава на вишинах!
“Mai albarka ne sarki wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Salama ta kasance a sama, da ɗaukaka kuma a can cikin sama!”
39 А деякі з Фарисеїв між народом казали до Него: Учителю, закажи ученикам Твоїм.
Sai waɗansu Farisiyawa a cikin taron suka ce wa Yesu, “Malam, ka kwaɓi almajiranka!”
40 І озвавшись рече їм: Глаголю вам, що коли сї замовкнуть, каміннє кричати ме.
Ya amsa ya ce, “Ina gaya muku, ko da sun yi shiru, duwatsu za su fara kirari.”
41 І, як наближивсь, то, побачивши город, заплакав над ним,
Da ya yi kusa da Urushalima, ya kuma ga birnin, sai ya yi kuka a kanta,
42 глаголючи: О, коли б зрозумів і ти хоч у день сей твій, що для впокою твого! тепер же воно закрито перед очима твоїми.
kuma ya ce, “In ke, ko ke ɗin ma, dā ma kin san abin da zai kawo miki salama a wannan rana, amma yanzu an ɓoye shi daga idanunki.
43 Бо прийдуть дні на тебе, й обкинуть вороги твої валами тебе, та й обляжуть тебе, й стиснуть тебе звідусюди.
Ranakun za su auko miki, a lokacin da abokan gābanki za su gina bango gāba da ke, su kuma kewaye inda kike, za su kuma tsare kowane gefenki, su sa ke a tsakiya.
44 І з землею зрівняють тебе з дїти твої у тобі; і не зоставлять у тобі каменя на камені; бо не розумів єси часу одвідин твоїх.
Za su fyaɗa ke a ƙasa, ke da’ya’yan da suke cikin katanganki. Ba za su bar wani dutse a kan wani ba, saboda ba ki gane da lokacin da Allah zai ziyarce ki ba.”
45 І ввійшовши у церкву, почав виганяти продаючих і купуючих,
Sai ya shiga filin haikali, ya fara korar masu sayar da kaya.
46 глаголючи їм: Писано: Дом мій - дом молитви; ви ж його зробили вертепом розбійників.
Ya ce musu, “A rubuce, yake cewa, ‘Gidana, zai zama gidan addu’a,’amma ga shi kun mai da shi ‘kogon’yan fashi.’”
47 І навчав щодня в церкві. Архиєреї ж та письменники й значні людські шукали Його вбити.
Kowace rana, ya yi ta koyarwa a haikalin. Amma manyan firistoci, da malaman dokoki, da shugabannin mutane, suna ƙoƙarin kashe shi.
48 І не знайшли, що б зробити Йому; народ бо ввесь горнувсь до Него слухаючи.
Amma ba su sami hanyar yin haka ba, domin kalmominsa sun kama hankalin dukan mutanen.

< Від Луки 19 >