< Від Луки 1 >

1 Яко ж бо многі заходились опоряджувати повість про добре знані нам речі,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 як передали нам ті, що з почину були самовидцями й слугами слова;
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 то здалось і менї гаразд, довідавшись од почину про все пильно, поряду тобі написати, високоповажний Теофиле,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 щоб знав певноту того, чого тебе навчено.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 Був за Ірода, царя Юдейського, один сьвященик, на ймя Захарія, з черги Авиїної, а жінка його з дочок Ааронових, а ймя її Єлисавета.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Були ж праведні обоє перед Богом, ходячи у всіх заповідях та наказах Господнїх безпорочні.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 і не було в них дитини: бо Єлисавета була неплідна, й обоє постарілись у днях своїх.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Стало ся ж, як служив він порядком черги своєї перед Богом,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 то, звичаєм сьвященства, довелось йому кадити, увійшовши в церкву Господню.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 А все множество народу молилось ізнадвору під час кадження.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Явив ся ж йому ангел Господень, стоячи правобіч жертівнї кадильної.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 І вжахнув ся Захарія побачивши, і страх обняв його.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 Рече ж до него ангел: Не лякай ся, Захаріє: бо вислухана молитва твоя, і жінка твоя Єлисавета вродить сина тобі, й даси ймя йому Йоан.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 І буде радість тобі й веселість; і многі різдвом його радувати муть ся.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 Буде бо великий перед Господем, і вина нї міцного напитку не пити ме; й Духом сьвятим сповнить ся ще з утроби матери своєї.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 І многих синів Ізраїлевих наверне до Господа Бога їх.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 І йти ме він перед Ним духом і силою Ілиї, щоб навернути серця батьків до дїтей, і неслухняних до мудрости праведних, приготовити Господеві людей готових.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 І рече Захарія до ангела: По чім же знати му се? я бо старий, і жінка моя ізстарілась у днях своїх.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 І озвавшись ангел, рече йому: Я Гавриїл, що стою перед Господем; і послано мене промовити до тебе та сповістити тебе про се.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 І ось замовкнеш і не зможеш говорити, аж по день, коли станеть ся се, за те що не поняв віри словам моїм, котрі справдять ся пори своєї.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 І ждав народ Захарії, і дивував ся, що барить ся він у церкві.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Вийшовши ж він, не зміг промовити до них; і постерегли вони, що видїннє бачив у церкві; бо він кивав до них, і зоставсь нїмий.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 І сталось, як сповнились днї служення його, пійшов до господи своєї.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Після ж тих днїв зачала Єлисавета, жінка його, й втаїлась пять місяцїв, говорячи:
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 Що так менї дав Господь у ті днї, як зглянув ся, зняти з мене докір між людьми.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Місяця ж шестого післав Бог ангела Гавриїла в город Галилейський, званий Назарет,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 до дїви, зарученої чоловікові, на ймя Йосифові, з дому Давидового; а ймя дїви Мария.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 І прийшовши ангел до неї, рече: Радуй ся, благодатная. Господь з тобою; благословенна єси між женами.
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Вона ж, побачивши його, вжахнулась словами його, та й подумала, що б се було за витаннє таке.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 І рече ангел їй: Не лякай ся, Мариє: знайшла бо єси ласку в Бога.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 І ось зачнеш ти в утробі твоїй, і вродиш Сина, й наречеш імя Йому Ісус.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Сей буде великий, і Сином Вишнього звати меть ся, і дасть Йому Господь Бог престол Давида, отця Його:
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 і царювати ме Він над домом Якововим по віки, й царству Його не буде кінця. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Рече ж Мария до ангела: Як буде се, коли чоловіка не знаю?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 І озвавшись ангел, рече їй: Дух сьвятий найде на тебе, й сила Вишнього отїнить тебе; тим і, що вродить ся сьвяте, звати меть ся Сином Божим.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 І ось Єлисавета, родичка твоя і вона також зачала, сина в старості своїй, і се шестий місяць званій неплідною.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 Бо не буде неможливе у Бога всяке слово.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Рече ж Мария: Се рабиня Господня: нехай станеть ся менї по слову твоєму. І пійшов від неї ангел.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Уставши ж Мария тими днями, пійшла швидко в підгіррє, у город Юдин;
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 і ввійшла в господу Захаріїну, і виталась із Єлисаветою.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 І сталось, як почула Єлисавета витаннє Мариїне, кинулась дитина в утробі її; і сповнилась Єлисавета Духом сьвятим,
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 і промовила голосом великим, і рече: Благословенна єси між женами, й благословенний плід утроби твоєї.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 І звідкіля менї се, що прийшла мати Господа мого до мене?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Ось бо, як дійшов голос витання твого до ушей моїх, кинулась з радости дитина в утробі моїй.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 І благословенна, що увірувала, бо сповнить ся, що сказано їй від Господа.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 І рече Мария: Величає душа моя Господа,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 і зрадував ся дух мій у Бозї Спасї моїм,
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 що споглянув на смиреннє слуги своєї: ось бо від нинї блаженною звати муть мене всї роди:
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 бо зробив менї велике Сильний; і сьвяте імя Його.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 І милості Його від роду до роду на боячих ся Його.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Зробив силу рукою своєю, розсипав гордих у думках сердець їх;
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 поскидав потужних з престолів, і підняв угору смиренних;
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 голодних сповнив добром, а багатих одіслав упорожнї;
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 прийняв Ізраїля, слугу свого, на спомин милости,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 (як промовив до батьків наших) Авраамові й насінню його по віки. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Пробувала ж Мария з нею місяцїв зо три, та й вернулась до домівки своєї.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Єлисаветї ж сповнив ся час родити, й вродила вона сина.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 І чули сусіде її і родина її, що Господь показав велику милость свою до неї, і радувались із нею.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 І сталось, восьмого дня прийшли обрізати хлопятко, і хотіли назвати його ймям батька його, Захарією.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 І озвавшись мати його, каже: Нї, а нехай назветь ся Йоаном.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 І казали до неї: Що нікого нема в родині твоїй, щоб звав ся імям сим.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Кивали ж батькові його, як схотів би назвати його.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 І, попросивши таблицї, написав слова: Йоан буде ймя йому. І дивувались усї.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 Відкрили ся яе уста його зараз, і язик його, й заговорив, прославляючи Бога.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 І був на всїх страх, що жили кругом них; і по всьому підгіррю Юдейському пронеслись усї слова ті.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 І положили всі, хто чув, у серці своїм, кажучи: Що ж то за дитина се буде! І рука Господня була з ним.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 І Захарія, батько його, сповнив ся Духом сьвятим, і прорік, глаголючи:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 Благословен Господь Бог Ізраїлїв, що одвідав і зробив ізбавленнє народові своєму,
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 і підняв ріг спасення нам у дому Давида, слуги свого,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 (як промовляв устами сьвятих од віку пророків своїх, ) (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 спасеннє од ворогів наших і з руки всіх ненавидників наших,
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 щоб зробити милость отцям нашим, і спогадати завіт свій сьвятий,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 клятьбу, що кляв ся перед Авраамом, отцем нашим,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 та що дасть нам без страху, з рук ворогів наших визволившись,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 служити Йому в сьвятостї та праведності перед Ним, по всі днї життя нашого.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 А ти, дитино, пророком Вишнього звати меш ся: ходити меш бо перед лицем Господнім, готовити дороги Його;
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 щоб давати знаннє спасення народові Його в оставленню гріхів їх,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 по благій милості Бога нашого, в котрій одвідав нас Схід з висоти,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 щоб засияв сидячим у темряві і тїнї смертній, щоб направити ноги наші на дорогу впокою.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 Хлопятко ж росло та міцніло духом, і пробувало в пустині аж до дня явлення свого перед Ізраїлем.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Від Луки 1 >