< Romalilar 14 >

1 İmanı zayıf olanı aranıza kabul edin, ama tartışmalı konulara girmeyin.
Ku karɓi wanda bangaskiyarsa ba tă yi ƙarfi ba, amma fa kada ku hukunta shi a kan abubuwan da ake da shakka a kai ba.
2 Biri her şeyi yiyebileceğine inanır; imanı zayıf olansa yalnız sebze yer.
Bangaskiyar mutum ta yarda masa yă ci kome, amma wanda bangaskiyarsa ba tă yi ƙarfi ba, yakan ci kayan lambu ne kawai.
3 Her şeyi yiyen, yemeyeni hor görmesin. Her şeyi yemeyen, yiyeni yargılamasın. Çünkü Tanrı onu kabul etmiştir.
Mutumin da yake cin kowane irin abinci, kada yă rena wanda ba ya cin, wanda kuma ba ya cin kowane irin abinci, kada yă ga laifin mutumin da yake ci, domin Allah ya riga ya karɓe shi.
4 Sen kimsin ki, başkasının kulunu yargılıyorsun? Kulu haklı çıkaran da haksız çıkaran da efendisidir. Kul haklı çıkacaktır. Çünkü Rab'bin onu haklı çıkarmaya gücü vardır.
Kai wane ne har da za ka ga laifin bawan wani? Ko bawan yă yi aiki mai kyau, ko yă kāsa, ai, wannan ruwan maigidansa ne. Za a ma tsai da shi, domin Ubangiji yana da ikon tsai da shi.
5 Kimi bir günü başka bir günden üstün sayar, kimi her günü bir sayar. Herkesin kendi görüşüne tam güveni olsun.
Wani yakan ɗauki wata rana da daraja fiye da sauran ranaku; wani kuma yana ganin dukan ranakun ɗaya ne. Ya kamata kowa yă kasance da tabbaci a cikin zuciyarsa.
6 Belli bir günü kutlayan, Rab için kutlar. Her şeyi yiyen, Tanrı'ya şükrederek Rab için yer. Bazı şeyleri yemeyen de Rab için yemez ve Tanrı'ya şükreder.
Wannan mai ɗaukan rana ɗaya da muhimmanci fiye da sauran, yana yin haka ne ga Ubangiji. Wannan mai cin nama, yana yin haka ne ga Ubangiji, gama yakan yi godiya ga Allah; wannan da ba ya ci kuwa, yana yin haka ne ga Ubangiji yana kuwa yin godiya ga Allah.
7 Hiçbirimiz kendimiz için yaşamayız, hiçbirimiz de kendimiz için ölmeyiz.
Gama ba waninmu da yake rayuwa wa kansa kaɗai, kuma ba waninmu da kan mutu don kansa kaɗai.
8 Yaşarsak Rab için yaşarız; ölürsek Rab için ölürüz. Öyleyse, yaşasak da ölsek de Rab'be aitiz.
In muna rayuwa, muna rayuwa ne ga Ubangiji; in kuma muna mutuwa, muna mutuwa ne ga Ubangiji. Saboda haka, ko muna a raye ko muna a mace, mu na Ubangiji ne.
9 Mesih hem ölülerin hem yaşayanların Rabbi olmak üzere ölüp dirildi.
Saboda wannan ne Kiristi ya mutu, ya kuma sāke rayuwa domin yă zama Ubangiji na matattu da na masu rai.
10 Sen neden kardeşini yargılıyorsun? Ya sen, kardeşini neden küçümsüyorsun? Tanrı'nın yargı kürsüsü önüne hepimiz çıkacağız.
Kai kuwa, don me kake ganin laifin ɗan’uwanka? Ko kuma don me kake rena ɗan’uwanka? Gama duk za mu tsaya a gaban kujerar shari’ar Allah.
11 Yazılmış olduğu gibi: “Rab şöyle diyor: ‘Varlığım hakkı için her diz önümde çökecek, Her dil Tanrı olduğumu açıkça söyleyecek.’”
A rubuce yake cewa, “‘Muddin ina raye,’ in ji Ubangiji, ‘kowace gwiwa za tă durƙusa a gabana; kowane harshe kuma zai furta wa Allah.’”
12 Böylece her birimiz kendi adına Tanrı'ya hesap verecektir.
Don haka kowannenmu zai ba da lissafin kansa ga Allah.
13 Onun için, artık birbirimizi yargılamayalım. Bunun yerine, hiçbir kardeşin yoluna sürçme ya da tökezleme taşı koymamaya kararlı olun.
Saboda haka bari mu daina ba wa juna laifi. A maimakon, sai kowa yă yi niyya ba zai sa dutsen tuntuɓe ko abin sa fāɗuwa a hanyar ɗan’uwansa ba.
14 Rab İsa'ya ait biri olarak kesinlikle biliyorum ki, hiçbir şey kendiliğinden murdar değildir. Ama bir şeyi murdar sayan için o şey murdardır.
A matsayina na mai bin Ubangiji Yesu na tabbata ƙwarai cewa babu abincin da yake marar tsabta don kansa. Amma in wani ya ɗauka wani abu marar tsabta ne, to, a gare shi marar tsabta ne.
15 Yediğin bir şey yüzünden kardeşin incinmişse, artık sevgi yolunda yürümüyorsun demektir. Mesih'in, uğruna öldüğü kardeşini yediklerinle mahvetme!
In kana ɓata wa ɗan’uwanka zuciya saboda abincin da kake ci, ba halin ƙauna kake nunawa ba ke nan. Kada abincin da kake ci yă zama hanyar lalatar da ɗan’uwanka wanda Kiristi ya mutu dominsa.
16 Size göre iyi olanın kötülenmesine fırsat vermeyin.
Kada ka bar abin da ka ɗauka a matsayi kyakkyawa yă zama abin zargi ga waɗansu.
17 Çünkü Tanrı'nın Egemenliği, yiyecek içecek sorunu değil, doğruluk, esenlik ve Kutsal Ruh'ta sevinçtir.
Gama mulkin Allah ba batun ci da sha ba ne, sai dai na adalci, salama, da kuma farin ciki cikin Ruhu Mai Tsarki,
18 Mesih'e bu yolda hizmet eden, Tanrı'yı hoşnut eder, insanların da beğenisini kazanır.
duk kuwa wanda yake bauta wa Kiristi a haka yana faranta wa Allah rai ne, yardajje kuma ga mutane.
19 Öyleyse kendimizi esenlik getiren ve karşılıklı gelişmemizi sağlayan işlere verelim.
Saboda haka sai mu yi iya ƙoƙari mu aikata abin da zai kawo salama da kuma ingantawa ga juna.
20 Yiyecek uğruna Tanrı'nın işini bozma! Her yiyecek temizdir, ama yedikleriyle başkasının sürçmesine yol açan kişi kötülük etmiş olur.
Kada ku lalatar da aikin Allah saboda abinci. Dukan abinci mai tsabta ne, sai dai ba daidai ba ne mutum yă ci abin da zai sa wani yă yi tuntuɓe.
21 Et yememen, şarap içmemen, kardeşinin sürçmesine yol açacak bir şey yapmaman iyidir.
Ya fi kyau kada ka ci nama ko ka sha ruwan inabi ko kuma ka yi wani abin da zai sa ɗan’uwanka yă fāɗi.
22 Bu konulardaki inancını Tanrı'nın önünde kendine sakla. Onayladığı şeyden ötürü kendini yargılamayan kişi ne mutludur!
Bari duk ra’ayin da kake da shi game da wannan sha’ani yă kasance tsakaninka da Allah. Mai albarka ne wanda zuciyarsa ba tă ba shi laifi game da abin da shi da kansa ya ɗauka cewa daidai ne ba.
23 Ama bir yiyecekten kuşkulanan kişi onu yerse yargılanır; çünkü imanla yemiyor. İmana dayanmayan her şey günahtır.
Amma wanda yake da shakka yakan jawo wa kansa hukunci ne in ya ci, domin yana ci ne ba bisa ga bangaskiya ba; kuma duk abin da bai zo daga bangaskiya ba zunubi ne.

< Romalilar 14 >