< Yuhanna 1 >

1 Başlangıçta Söz vardı. Söz Tanrı'yla birlikteydi ve Söz Tanrı'ydı.
Tun farar farawa akwai Kalma, Kalman kuwa yana nan tare da Allah, Kalman kuwa Allah ne.
2 Başlangıçta O, Tanrı'yla birlikteydi.
Yana nan tare da Allah tun farar farawa.
3 Her şey O'nun aracılığıyla var oldu, var olan hiçbir şey O'nsuz olmadı.
Ta wurin Kalman ne aka halicci dukan abubuwa. In ba tare da shi ba, babu abin da aka yi wanda aka yi.
4 Yaşam O'ndaydı ve yaşam insanların ışığıydı.
A cikinsa rai ya kasance, wannan rai kuwa shi ne hasken mutane.
5 Işık karanlıkta parlar. Karanlık onu alt edemedi.
Hasken yana haskakawa cikin duhu, amma duhun bai rinjaye shi ba.
6 Tanrı'nın gönderdiği Yahya adlı bir adam ortaya çıktı.
Akwai wani mutumin da aka aiko daga Allah; mai suna Yohanna.
7 Tanıklık amacıyla, ışığa tanıklık etsin ve herkes onun aracılığıyla iman etsin diye geldi.
Ya zo a matsayin mai shaida domin yă ba da shaida game da wannan haske, don ta wurinsa dukan mutane su ba da gaskiya.
8 Kendisi ışık değildi, ama ışığa tanıklık etmeye geldi.
Shi kansa ba shi ne hasken ba; sai dai ya zo a matsayin shaida ne kaɗai ga hasken.
9 Dünyaya gelen, her insanı aydınlatan gerçek ışık vardı.
Haske na gaskiya da yake ba da haske ga kowane mutum mai shigowa duniya.
10 O, dünyadaydı, dünya O'nun aracılığıyla var oldu, ama dünya O'nu tanımadı.
Yana a duniya, kuma ko da yake an yi duniya ta wurinsa ne, duniya ba tă gane shi ba.
11 Kendi yurduna geldi, ama kendi halkı O'nu kabul etmedi.
Ya zo wurin abin da yake nasa, amma nasa ɗin ba su karɓe shi ba.
12 Kendisini kabul edip adına iman edenlerin hepsine Tanrı'nın çocukları olma hakkını verdi.
Duk da haka dukan waɗanda suka karɓe shi, ga waɗanda suka gaskata a sunansa, ya ba su iko su zama’ya’yan Allah
13 Onlar ne kandan, ne beden ne de insan isteğinden doğdular; tersine, Tanrı'dan doğdular.
’ya’yan da aka haifa ba bisa hanyar’yan adam, ko shawarar mutum ko nufin namiji ba, sai dai haifaffu bisa ga nufin Allah.
14 Söz, insan olup aramızda yaşadı. O'nun yüceliğini –Baba'dan gelen, lütuf ve gerçekle dolu biricik Oğul'un yüceliğini– gördük.
Kalman ya zama mutum, ya kuwa zauna a cikinmu. Muka ga ɗaukakarsa, ɗaukaka ta wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaici, wanda ya zo daga wurin Uba, cike da alheri da gaskiya.
15 Yahya O'na tanıklık etti. Yüksek sesle şöyle dedi: “‘Benden sonra gelen benden üstündür. Çünkü O benden önce vardı’ diye sözünü ettiğim kişi budur.”
(Yohanna ya ba da shaida game da shi. Ya ɗaga murya yana cewa, “Wannan shi ne wanda na ce, ‘Mai zuwa bayana ya fi ni girma domin yana nan kafin ni.’”)
16 Nitekim hepimiz O'nun doluluğundan lütuf üzerine lütuf aldık.
Daga yalwar alherinsa dukanmu muka sami albarka bisa albarka.
17 Kutsal Yasa Musa aracılığıyla verildi, ama lütuf ve gerçek İsa Mesih aracılığıyla geldi.
Gama an ba da doka ta wurin Musa; alheri da gaskiya kuwa sun zo ne ta wurin Yesu Kiristi.
18 Tanrı'yı hiçbir zaman hiç kimse görmedi. Baba'nın bağrında bulunan ve Tanrı olan biricik Oğul O'nu tanıttı.
Ba wanda ya taɓa ganin Allah, sai dai Allah da yake Ɗaya da kuma Makaɗaici wanda yake a gefen Uba, shi ne ya bayyana shi.
19 Yahudi yetkililer Yahya'ya, “Sen kimsin?” diye sormak üzere Yeruşalim'den kâhinlerle Levililer'i gönderdikleri zaman Yahya'nın tanıklığı şöyle oldu –açıkça konuştu, inkâr etmedi– “Ben Mesih değilim” diye açıkça konuştu.
To, ga shaidar Yohanna sa’ad da Yahudawan Urushalima suka aiki firistoci da Lawiyawa su tambaye shi ko shi wane ne.
Bai yi mūsu ba, amma ya shaida a fili cewa, “Ba ni ne Kiristi ba.”
21 Onlar da kendisine, “Öyleyse sen kimsin? İlyas mısın?” diye sordular. O da, “Değilim” dedi. “Sen beklediğimiz peygamber misin?” sorusuna, “Hayır” yanıtını verdi.
Sai suka tambaye shi suka ce, “To, wane ne kai? Kai ne Iliya?” Ya ce, “A’a, ni ba shi ba ne.” “Kai ne Annabin nan?” Ya amsa ya ce, “A’a.”
22 Bu kez, “Kim olduğunu söyle de bizi gönderenlere bir yanıt verelim” dediler. “Kendin için ne diyorsun?”
A ƙarshe suka ce, “Wane ne kai? Ka ba mu amsa don mu mayar wa waɗanda suka aike mu. Me kake ce da kanka?”
23 Yahya, “Peygamber Yeşaya'nın dediği gibi, ‘Rab'bin yolunu düzleyin’ diye çölde haykıranın sesiyim ben” dedi.
Yohanna ya amsa da kalmomin annabi Ishaya, “Ni murya ne mai kira a hamada, ‘Ku miƙe hanya domin Ubangiji.’”
24 Yahya'ya gönderilen bazı Ferisiler ona, “Sen Mesih, İlyas ya da beklediğimiz peygamber değilsen, niye vaftiz ediyorsun?” diye sordular.
To, waɗansu Farisiyawan da aka aika
suka tambaye shi suka ce, “Don me kake yin baftisma in kai ba Kiristi ba ne, ba kuwa Iliya ba, ba kuma annabin nan ba?”
26 Yahya onlara şöyle yanıt verdi: “Ben suyla vaftiz ediyorum, ama aranızda tanımadığınız biri duruyor.
Yohanna ya amsa ya ce, “Ni dai ina baftisma da ruwa ne, amma a cikinku akwai wani tsaye da ba ku sani ba.
27 Benden sonra gelen O'dur. Ben O'nun çarığının bağını çözmeye bile layık değilim.”
Shi ne mai zuwa bayana, wanda ko igiyar takalmansa ma ban isa in kunce ba.”
28 Bütün bunlar Şeria Irmağı'nın ötesinde bulunan Beytanya'da, Yahya'nın vaftiz ettiği yerde oldu.
Wannan duk ya faru ne a Betani a ƙetaren Urdun, inda Yohanna yake yin baftisma.
29 Yahya ertesi gün İsa'nın kendisine doğru geldiğini görünce şöyle dedi: “İşte, dünyanın günahını ortadan kaldıran Tanrı Kuzusu!
Kashegari Yohanna ya ga Yesu yana zuwa wajensa sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah mai ɗauke zunubin duniya!
30 Kendisi için, ‘Benden sonra biri geliyor, O benden üstündür. Çünkü O benden önce vardı’ dediğim kişi işte budur.
Wannan shi ne wanda nake nufi sa’ad da na ce, ‘Mutum mai zuwa bayana ya fi ni girma, domin yana nan kafin ni.’
31 Ben O'nu tanımıyordum, ama İsrail'in O'nu tanıması için ben suyla vaftiz ederek geldim.”
Ko ni ma dā ban san shi ba, sai dai abin da ya sa na zo ina baftisma da ruwa shi ne domin a bayyana shi ga Isra’ila.”
32 Yahya tanıklığını şöyle sürdürdü: “Ruh'un güvercin gibi gökten indiğini, O'nun üzerinde durduğunu gördüm.
Sai Yohanna ya ba da wannan shaida, “Na ga Ruhu ya sauko kamar kurciya daga sama ya zauna a kansa.
33 Ben O'nu tanımıyordum. Ama suyla vaftiz etmek için beni gönderen, ‘Ruh'un kimin üzerine inip durduğunu görürsen, Kutsal Ruh'la vaftiz eden O'dur’ dedi.
Dā ban san shi ba, sai dai wanda ya aiko ni in yi baftisma da ruwa ya gaya mini cewa, ‘Mutumin da ka ga Ruhu ya sauko ya kuma zauna a kansa shi ne wanda zai yi baftisma da Ruhu Mai Tsarki.’
34 Ben de gördüm ve ‘Tanrı'nın Oğlu budur’ diye tanıklık ettim.”
Na gani na kuma shaida cewa wannan Ɗan Allah ne.”
35 Ertesi gün Yahya yine öğrencilerinden ikisiyle birlikteydi.
Kashegari kuma Yohanna yana can tare da biyu daga cikin almajiransa.
36 Oradan geçen İsa'ya bakarak, “İşte Tanrı Kuzusu!” dedi.
Da ya ga Yesu yana wucewa, sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah!”
37 Onun söylediklerini duyan iki öğrenci İsa'nın ardından gitti.
Da almajiran nan biyu suka ji ya faɗi haka, sai suka bi Yesu.
38 İsa arkasına dönüp ardından geldiklerini görünce, “Ne arıyorsunuz?” diye sordu. Onlar da, “Rabbî, nerede oturuyorsun?” dediler. Rabbî, öğretmenim anlamına gelir.
Da juyewa, sai Yesu ya ga suna bin sa, sai ya tambaye, su ya ce, “Me kuke nema?” Suka ce, “Rabbi” (wato, “Malam”), “ina kake da zama?”
39 İsa, “Gelin, görün” dedi. Gidip O'nun nerede oturduğunu gördüler ve o gün O'nunla kaldılar. Saat dört sularıydı.
Ya amsa musu ya ce, “Ku zo, za ku kuma gani.” Saboda haka suka je suka ga inda yake da zama, suka kuma zauna a can tare da shi. Wajen sa’a ta goma ce kuwa.
40 Yahya'yı işitip İsa'nın ardından giden iki kişiden biri Simun Petrus'un kardeşi Andreas'tı.
Andarawus ɗan’uwan Siman Bitrus, yana ɗaya daga cikin biyun nan da suka bi Yesu bayan da suka ji maganar Yohanna a kan Yesu.
41 Andreas önce kendi kardeşi Simun'u bularak ona, “Biz Mesih'i bulduk” dedi. Mesih, meshedilmiş anlamına gelir.
Abu na fari da Andarawus ya yi shi ne ya sami ɗan’uwansa Siman ya gaya masa cewa, “Mun sami Almasihu” (wato, Kiristi).
42 Andreas kardeşini İsa'ya götürdü. İsa ona baktı, “Sen Yuhanna'nın oğlu Simun'sun. Kefas diye çağrılacaksın” dedi. Kefas, kaya anlamına gelir.
Ya kuma kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi ya ce, “Kai ne Siman ɗan Yohanna. Za a ce da kai Kefas” (in an fassara, Bitrus ke nan).
43 Ertesi gün İsa, Celile'ye gitmeye karar verdi. Filipus'u bulup ona, “Ardımdan gel” dedi.
Kashegari Yesu ya yanke shawara yă tafi Galili. Da ya sami Filibus sai ya ce masa, “Bi ni.”
44 Filipus da Andreas ile Petrus'un kenti olan Beytsayda'dandı.
Filibus, kamar Andarawus da Bitrus shi ma daga garin Betsaida ne.
45 Filipus, Natanel'i bularak ona, “Musa'nın Kutsal Yasa'da hakkında yazdığı, peygamberlerin de sözünü ettiği kişiyi, Yusuf oğlu Nasıralı İsa'yı bulduk” dedi.
Filibus ya sami Natanayel ya kuma gaya masa, “Mun sami wanda Musa ya rubuta game da shi a cikin Doka, kuma wanda annabawa suka rubuta a kansa, Yesu Banazare, ɗan Yusuf.”
46 Natanel Filipus'a, “Nasıra'dan iyi bir şey çıkabilir mi?” diye sordu. Filipus, “Gel de gör” dedi.
Natanayel ya ce, “A Nazaret! Wani abin kirki zai iya fito daga can?” Filibus ya ce, “Zo ka gani.”
47 İsa, Natanel'in kendisine doğru geldiğini görünce onun için, “İşte, içinde hile olmayan gerçek bir İsrailli!” dedi.
Da Yesu ya ga Natanayel yana zuwa, sai ya yi magana game da shi cewa, “Ga mutumin Isra’ila na gaske wanda ba shi da ha’inci.”
48 Natanel, “Beni nereden tanıyorsun?” diye sordu. İsa, “Filipus çağırmadan önce seni incir ağacının altında gördüm” yanıtını verdi.
Natanayel ya yi tambaya ya ce, “A ina ka san ni?” Yesu ya amsa ya ce, “Na gan ka yayinda kake a gindin itacen ɓaure, kafin Filibus yă kira ka.”
49 Natanel, “Rabbî, sen Tanrı'nın Oğlu'sun, sen İsrail'in Kralı'sın!” dedi.
Sai Natanayel ya ce, “Rabbi, kai Ɗan Allah ne. Kai ne Sarkin Isra’ila.”
50 İsa ona dedi ki, “Seni incir ağacının altında gördüğümü söylediğim için mi inanıyorsun? Bunlardan daha büyük şeyler göreceksin.”
Yesu ya ce, “Ka gaskata domin na ce maka na gan ka a gindin itacen ɓaure. Za ka ga abubuwan da suka fi haka.”
51 Sonra da, “Size doğrusunu söyleyeyim, göğün açıldığını, Tanrı meleklerinin İnsanoğlu üzerinde yükselip indiklerini göreceksiniz” dedi.
Sai ya ƙara da cewa, “Gaskiya nake gaya muku, za ku ga sama a buɗe, mala’ikun Allah kuma suna hawa suna kuma sauka a kan Ɗan Mutum.”

< Yuhanna 1 >