< Eyüp 28 >

1 Gümüş maden ocağından elde edilir, Altını arıtmak için de bir yer vardır.
Akwai ramin azurfa akwai kuma wurin da ake tace zinariya.
2 Demir topraktan çıkarılır, Bakırsa taştan.
Daga cikin ƙasa ake ciro ƙarfe, ana kuma narkar da tagulla daga cikin dutse.
3 İnsan karanlığa son verir, Koyu karanlığın, ölüm gölgesinin taşlarını Son sınırına kadar araştırır.
Mutum ya kawo ƙarshen duhu; yakan bincike zuzzurfar iyaka, yana neman duwatsu a wuri mafi duhu.
4 Maden kuyusunu insanların oturduğu yerden uzakta açar, İnsan ayağının unuttuğu yerlerde, Herkesten uzak iplere sarılıp sallanır.
Nesa da inda mutane suke zama, yakan huda rami yă yi abin lilo, a wurin da mutane ba sa bi.
5 Ekmek topraktan çıkar, Toprağın altı ise yanmış, altüst olmuştur.
Cikin ƙasa inda ake samun abinci, a ƙarƙashinta kuwa zafi ne kamar wuta;
6 Kayalarından laciverttaşı çıkar, Yüzeyi altın tozunu andırır.
akwai duwatsu masu daraja a cikin duwatsunta, akwai kuma zinariya a cikin ƙurarta.
7 Yırtıcı kuş yolu bilmez, Doğanın gözü onu görmemiştir.
Tsuntsu mai farauta bai san hanyarta ba, ba shahon da ya taɓa ganin ta.
8 Güçlü hayvanlar oraya ayak basmamış, Aslan oradan geçmemiştir.
Manyan namun jeji ba su taɓa binta ba, ba zakin da ya taɓa binta.
9 Madenci elini çakmak taşına uzatır, Dağları kökünden altüst eder.
Hannun mutum ya iya sarrafa ƙanƙarar duwatsu, yă kuma tumɓuke tushen duwatsu.
10 Kayaların içinden tüneller açar, Gözleri değerli ne varsa görür.
Yana tona rami a cikin duwatsu idanunsa suna ganin dukan dukiyar da ke cikin duwatsun.
11 Irmakların kaynağını tıkar, Gizli olanı ışığa çıkarır.
Yana nema daga ina ruwan rafi yake ɓulɓulowa yana kuma binciko abubuwan da suke a ɓoye yă kawo su cikin haske.
12 Ama bilgelik nerede bulunur? Aklın yeri neresi?
Amma a ina ne za a iya samun hikima? Ina fahimta take zama?
13 İnsan onun değerini bilmez, Yaşayanlar diyarında ona rastlanmaz.
Mutum bai gane muhimmancinta ba, ba a samunta a ƙasar masu rai.
14 Engin, “Bende değil” der, Deniz, “Yanımda değil.”
Zurfi ya ce, “Ba ta wurina”; teku ya ce, “Ba ta wurina.”
15 Onun bedeli saf altınla ödenmez, Değeri gümüşle ölçülmez.
Ba irin zinariyar da za tă iya sayenta, ko kuma a iya auna nauyinta da azurfa.
16 Ona Ofir altınıyla, değerli oniksle, Laciverttaşıyla değer biçilmez.
Ba za a iya sayenta da zinariyar Ofir, ko sauran duwatsu masu daraja ba.
17 Ne altın ne cam onunla karşılaştırılabilir, Saf altın kaplara değişilmez.
Zinariya da madubi ba za su iya gwada kansu da ita ba, ba kuwa za a iya musayarta da abubuwan da aka yi da zinariya ba.
18 Yanında mercanla billurun sözü edilmez, Bilgeliğin değeri mücevherden üstündür.
Kada ma a ce murjani da duwatsu masu walƙiya; farashin hikima ya fi na lu’ulu’ai.
19 Kûş topazı onunla denk sayılmaz, Saf altınla ona değer biçilmez.
Ba za a iya daidaita darajarta da duwatsun Tofaz na Kush ba, zallar zinariya ma ba tă isa ta saye ta ba.
20 Öyleyse bilgelik nereden geliyor? Aklın yeri neresi?
“To, daga ina ke nan hikima ta fito? Ina fahimta take zama?
21 O bütün canlıların gözünden uzaktır, Gökte uçan kuşlardan bile saklıdır.
An ɓoye ta daga idanun kowane abu mai rai, har tsuntsayen sararin sama ma an ɓoye masu ita.
22 Yıkım'la Ölüm: “Kulaklarımız ancak fısıltısını duydu” der.
Hallaka da mutuwa suna cewa, ‘Jita-jitarta kaɗai muke ji.’
23 Onun yolunu Tanrı anlar, Yerini bilen O'dur.
Allah ya gane hanyar zuwa wurinta. Shi ne kaɗai ya san inda take zama,
24 Çünkü O yeryüzünün uçlarına kadar bakar, Göklerin altındaki her şeyi görür.
Gama yana ganin iyakar duniya kuma yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sama.
25 Rüzgara güç verdiği, Suları ölçtüğü,
Lokacin da ya yi iska ya sa ta hura, ya kuma auna ruwaye.
26 Yağmura kural koyduğu, Yıldırıma yol açtığı zaman,
Lokacin da ya yi wa ruwan sama doka da kuma hanya domin walƙiya,
27 Bilgeliği görüp değerini biçti, Onu onaylayıp araştırdı.
sai ya dubi hikima ya auna ta; ya tabbatar da ita, ya gwada ta.
28 İnsana, “İşte Rab korkusu, bilgelik budur” dedi, “Kötülükten kaçınmak akıllılıktır.”
Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’”

< Eyüp 28 >