< Yeremya 32 >

1 Yahuda Kralı Sidkiya'nın onuncu, Nebukadnessar'ın on sekizinci yılında RAB Yeremya'ya seslendi.
Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga Ubangiji a shekara ta goma ta Zedekiya sarkin Yahuda, wanda ya kasance shekara ta goma sha takwas ta Nebukadnezzar.
2 O sırada Babil Kralı'nın ordusu Yeruşalim'i kuşatmaktaydı. Peygamber Yeremya Yahuda Kralı'nın sarayındaki muhafız avlusunda tutukluydu.
Sojojin sarkin Babilon a lokacin suna ƙawanya wa Urushalima annabi Irmiya kuwa yana a tsare a sansanin matsara a fadar Yahuda.
3 Yahuda Kralı Sidkiya onu orada tutuklatmıştı. “Neden böyle peygamberlik ediyorsun?” demişti, “Sen diyorsun ki, ‘RAB şöyle diyor: Bu kenti Babil Kralı'nın eline teslim etmek üzereyim, onu ele geçirecek.
Zedekiya sarkin Yahuda fa ya sa shi a kurkuku yana cewa, “Don me kake yin annabci? Ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga sarkin Babilon, zai kuwa cinye ta.
4 Yahuda Kralı Sidkiya Kildaniler'in elinden kaçıp kurtulamayacak, kesinlikle Babil Kralı'nın eline teslim edilecek; onunla yüzyüze konuşacak, onu gözleriyle görecek.
Zedekiya sarkin Yahuda ba zai kuɓuta daga hannuwan Babiloniyawa ba amma tabbatacce za a ba da shi ga sarkin Babilon, zai kuwa yi masa magana fuska da fuska ya kuma gan shi da idanunsa.
5 Sidkiya Babil'e götürülecek, ben onunla ilgilenene dek orada kalacak, Kildaniler'le savaşsanız bile başarılı olamayacaksınız diyor RAB.’”
Zai kai Zedekiya Babilon, inda zai zauna har sai ya magance shi, in ji Ubangiji. In ka yi yaƙi da Babiloniyawa, ba za ka yi nasara ba.’”
6 Yeremya, “RAB bana şöyle seslendi” diye yanıtladı,
Irmiya ya ce, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
7 “Amcan Şallum oğlu Hanamel sana gelip, ‘Anatot'taki tarlamı satın al. Çünkü en yakın akrabam olarak tarlayı satın alma hakkı senindir’ diyecek.
Hananel ɗan Shallum ɗan’uwan mahaifinka zai zo wurinka ya ce, ‘Saya filina a Anatot, domin a matsayinka na dangi na kurkusa hakkinka ne kuma kai ya wajaba ka saye shi.’
8 “Sonra RAB'bin sözü uyarınca amcamın oğlu Hanamel muhafız avlusunda yanıma gelip, ‘Benyamin bölgesinde, Anatot'taki tarlamı satın al’ dedi, ‘Çünkü miras hakkı da en yakın akrabalık hakkı da senindir. Onu kendin için satın al.’ “O zaman RAB'bin sözünün yerine geldiğini anladım.
“Sa’an nan, kamar dai yadda Ubangiji ya faɗa, sai ga Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina ya zo wurina a sansanin matsara ya ce, ‘Saya filina a Anatot a yankin Benyamin. Da yake hakkinka ne ka fanshe shi ka kuma mallake shi, ka sayo shi wa kanka.’ “Sai na gane cewa wannan maganar Ubangiji ce;
9 Böylece Anatot'taki tarlayı amcamın oğlu Hanamel'den satın aldım. Tarlaya karşılık kendisine on yedi şekel gümüş tartıp ödedim.
saboda haka sai na saye filin a Anatot daga hannun Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina na kuma auna masa shekel goma sha bakwai na azurfa.
10 Satış belgesini çağırdığım tanıkların önünde imzalayıp mühürledim, gümüşü terazide tarttım.
Na sa hannu a takarda, na buga hatimi na liƙe, na sami shaidu na kuwa auna shekel a ma’auni.
11 Satış belgesini –kural ve koşulları içeren mühürlenmiş kâğıdı ve açık sözleşme belgesini– aldım.
Na ɗauki takardar ciniki, takardar da aka rubuta sharuɗan a ciki, da kuma takardar da ba a liƙe ba,
12 Amcamın oğlu Hanamel'in, satış belgesini imzalayan tanıkların ve muhafız avlusunda oturan bütün Yahudiler'in gözü önünde satış belgesini Mahseya oğlu Neriya oğlu Baruk'a verdim.
na kuma ba wa Baruk ɗan Neriya, ɗan Masehiya, wannan takarda a gaban Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina da kuma a gaban shaidun da suka sa hannu a takardan ciniki da kuma a gaban dukan Yahudawan da suke zaune a sansanin matsaran.
13 “Hepsinin gözü önünde Baruk'a şu buyrukları verdim:
“A gabansu na yi wa Baruk waɗannan umarnai cewa,
14 ‘İsrail'in Tanrısı, Her Şeye Egemen RAB diyor ki, Bu satış belgesini –mühürlenmiş, açık olanını– al, uzun süre durmak üzere bir çömleğe koy.
‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka ɗauki waɗannan takardun ciniki, wanda aka liƙe da wanda ba a liƙe ba, ka sa su a cikin tulun yumɓu don kada su lalace.
15 Çünkü İsrail'in Tanrısı, Her Şeye Egemen RAB söz veriyor, bu ülkede yine evler, tarlalar, bağlar satın alınacak’ diyor.
Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa za a sāke saye gidaje, filaye da gonakin inabi a wannan ƙasa.’
16 “Tarlanın satış belgesini Neriya oğlu Baruk'a verdikten sonra RAB'be şöyle yakardım:
“Bayan na ba da takardun ciniki ga Baruk ɗan Neriya, sai na yi addu’a ga Ubangiji na ce,
17 “Ey Egemen RAB! Büyük gücünle, kudretinle yeri göğü yarattın. Yapamayacağın hiçbir şey yok.
“A, Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi sammai da duniya ta wurin ikonka mai girma da kuma hannunka mai iko. Ba abin da ya gagare ka.
18 Binlerce insana sevgi gösterir, ama babaların işlediği günahların karşılığını çocuklarına ödetirsin. Ey büyük ve güçlü Tanrı! Her Şeye Egemen RAB'dir senin adın.
Kakan nuna ƙauna ga dubbai amma kakan hukunta’ya’ya saboda laifin ubanninsu a bayansu. Ya mai girma da kuma Allah mai iko, wanda sunansa ne Ubangiji Maɗaukaki,
19 Tasarıların ne büyük, işlerin ne güçlü! Gözlerin insanların bütün yaptıklarına açıktır. Herkese davranışlarına, yaptıklarının sonucuna göre karşılığını verirsin.
manufofinka da girma suke, ayyukanka kuma masu girma ne. Idanunka suna a buɗe ga dukan hanyoyin mutane; kakan sāka wa kowa gwargwadon halinsa yadda ya dace.
20 Sen ki, Mısır'da, İsrail'de, bütün insanlar arasında bugüne dek mucizeler, harikalar yarattın. Bugün olduğu gibi ün kazandın.
Ka aikata ayyukan banmamaki da kuma al’ajabai a Masar ka kuma ci gaba da su har yă zuwa yau, a Isra’ila da kuma a cikin dukan’yan adam, ka kuma sami sunan da har yanzu yake naka.
21 Halkın İsrail'i belirtilerle, şaşılası işlerle, güçlü, kudretli elinle, büyük korku saçarak Mısır'dan çıkardın.
Ka fitar da mutanenka Isra’ila daga Masar da alamu da abubuwa banmamaki, ta wurin hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi tare da banrazana mai girma.
22 Atalarına vereceğine ant içtiğin bu toprakları, süt ve bal akan ülkeyi onlara verdin.
Ka ba su wannan ƙasa da ka rantse za ka ba wa kakanni kakanninsu, ƙasa mai zub da madara da zuma.
23 Gelip ülkeyi mülk edindiler, ama senin sözünü dinlemediler, Kutsal Yasan uyarınca yürümediler. Yapmalarını buyurduğun şeylerin hiçbirini yapmadılar. Bu yüzden bütün bu felaketleri getirdin başlarına.
Suka shiga suka mallake ta, amma ba su yi maka biyayya ba, ba su kuma bi dokarka ba; ba su yi abin da ka umarce su ba. Saboda haka ka kawo masifa a kansu.
24 “İşte, kenti ele geçirmek için kuşatma rampaları yapıldı. Kılıç, kıtlık, salgın hastalık yüzünden kent saldıran Kildaniler'e teslim edilecek. Söylediklerin yerine geldi, sen de görüyorsun!
“Duba yadda aka gina mahaurai don a kame birni. Saboda takobi, yunwa da annoba, za a ba da birnin ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye shi da yaƙi. Abin da ka faɗa ya faru, yadda kake gani yanzu.
25 Yine de, Egemen RAB, kent Kildaniler'e teslim edileceği halde sen bana, ‘Tarlayı çağırdığın tanıklar önünde gümüşle satın al’ dedin.”
Ko da yake za a ba da birnin ga Babiloniyawa, kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka ce mini, ‘Saye fili da azurfa ka kuma sa a shaida cinikin.’”
26 Bunun üzerine RAB Yeremya'ya şöyle seslendi:
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
27 “Bütün insanlığın Tanrısı RAB benim. Var mı yapamayacağım bir şey?
“Ni ne Ubangiji Allah na dukan’yan adam. Akwai wani abin da ya gagare ni?
28 Bu yüzden RAB diyor ki: Bak, bu kenti Kildaniler'le Babil Kralı Nebukadnessar'ın eline vermek üzereyim; onu ele geçirsin.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga Babiloniyawa da kuma ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, wanda zai yaƙe ta.
29 Kente saldıran Kildaniler gelip onu ateşe verecekler. Kenti de damlarında Baal'ın onuruna buhur yakıp başka ilahlara dökmelik sunular sunarak beni öfkelendirdikleri evleri de yakacaklar.
Babiloniyawan da suke yaƙi da wannan birni za su zo ciki su cinna masa wuta; tare da gidaje inda mutane suka tsokane ni na yi fushi ta wurin ƙona turare a rufin ɗakuna wa Ba’al suka zub da hadayun sha wa waɗansu alloli.
30 “Çünkü İsrail ve Yahuda halkları gençliklerinden beri hep gözümde kötü olanı yapıyor; İsrail halkı ellerinin yaptıklarıyla beni sürekli öfkelendiriyor, diyor RAB.
“Mutanen Isra’ila da na Yahuda ba abin da suka yi sai mugunta a gabana daga ƙuruciyarsu; tabbatacce, mutanen Isra’ila ba su yi kome ba sai dai tsokane ni da abin da hannuwansu suka yi, in ji Ubangiji.
31 Evet, bu kent kurulduğundan bu yana beni öyle öfkelendirdi, kızdırdı ki onu önümden söküp atacağım.
Daga ranar da aka gina ta har zuwa yanzu, wannan birni ta tā da fushina da hasalata da dole a kawar da ita daga gabana.
32 Çünkü İsrail ve Yahuda halklarının –kendilerinin, krallarının, önderlerinin, kâhinlerinin, peygamberlerinin, Yahuda ve Yeruşalim'de yaşayanların– beni öfkelendirmek için yaptıkları kötülüklerin haddi hesabı yok.
Mutanen Isra’ila da na Yahuda sun tsokane ni ta wurin dukan muguntar da suka aikata su, sarakunansu da fadawansu, firistocinsu da annabawa, mutanen Yahuda da mutanen Urushalima.
33 Bana yüzlerini değil, sırtlarını çevirdiler. Onları defalarca uyarmama karşın dinlemediler, yola gelmediler.
Sun juya mini bayansu ba fuskokinsu ba; ko da yake na koyar da su sau da sau, ba su saurara ko bi horo na ba.
34 Bana ait olan bu tapınağa iğrenç putlarını yerleştirerek onu kirlettiler.
Sun kafa gumakansu na banƙyama a cikin haikalina wanda ake kira da sunana, sun kuwa ƙazantar da shi.
35 Ben-Hinnom Vadisi'nde ilah Molek'e sunu olarak oğullarını, kızlarını ateşte kurban etmek için Baal'ın tapınma yerlerini kurdular. Böyle iğrenç şeyler yaparak Yahuda'yı günaha sürüklemelerini ne buyurdum, ne de aklımdan geçirdim.
Sun gina masujadai kan tudu wa Ba’al a Kwarin Ben Hinnom don su miƙa’ya’yansu maza da mata hadaya ga Molek, ko da yake ban taɓa umarce su ba, bai kuma zo mini cewa su yi abin banƙyama irin wannan ba ta haka suka sa Yahuda ya yi zunubi.
36 “Siz bu kent için, ‘Kılıçla, kıtlıkla, salgın hastalıkla Babil Kralı'nın eline veriliyor’ diyorsunuz. Ama şimdi İsrail'in Tanrısı RAB diyor ki:
“Kana cewa game da wannan birni, ‘Ta wurin takobi, yunwa da annoba za a ba da shi ga sarkin Babilon’; amma ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa
37 Kızgınlıkla, gazapla, büyük öfkeyle onları sürdüğüm ülkelerden hepsini toplayacağım. Onları buraya geri getirip güvenlik içinde yaşamalarını sağlayacağım.
tabbatacce zan tattara su daga dukan ƙasashen da na kore su zuwa cikin fushina da hasalata mai girma; zan komo da su wurin nan in sa su zauna lafiya.
38 Onlar benim halkım olacak, ben de onların Tanrısı olacağım.
Za su zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnsu.
39 Tek bir yürek, tek bir yaşam tarzı vereceğim onlara; gerek kendilerinin gerekse çocuklarının iyiliği için benden hep korksunlar.
Zan ba su zuciya ɗaya da aiki ɗaya, don kullum su ji tsorona domin amfaninsu da kuma amfanin’ya’yansu a bayansu.
40 Onlarla kalıcı bir antlaşma yapacağım: Onlara iyilik etmekten vazgeçmeyecek, benden hiç ayrılmasınlar diye yüreklerine Tanrı korkusu salacağım.
Zan yi madawwamin alkawari da su. Ba zan taɓa barin aikata musu alheri ba, zan kuma iza su su ji tsorona, don kada su ƙara juya daga gare ni.
41 Onlara iyilik etmekten sevinç duyacağım; gerçekten bütün yüreğimle, bütün canımla onları bu ülkede dikeceğim.
Zan yi farin ciki a yin musu alheri, tabbatacce zan su dasa a wannan ƙasa da dukan zuciyata da dukan raina.
42 “RAB diyor ki: Bu halkın başına bütün bu büyük felaketleri nasıl getirdiysem, onlara söz verdiğim bütün iyilikleri de öyle sağlayacağım.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, yadda na kawo dukan wannan masifa a kan wannan mutane, haka zan ba su wadatar da na yi musu alkawari.
43 Sizlerin, ‘Viran olmuş, insansız, hayvansız, Kildaniler'in eline verilmiş’ dediğiniz bu ülkede yine tarlalar satın alınacak.
Za a sāke sayi filaye a wannan ƙasa da kuka ce, ‘Kango ce, ba mutane ko dabbobi, gama an ba da ita ga Babiloniyawa.’
44 Benyamin bölgesinde, Yeruşalim çevresindeki köylerde, Yahuda kentlerinde, dağlık bölgenin, Şefela'nın ve Negev'in kentlerinde gümüşle tarlalar satın alınacak, satış belgeleri tanıkların önünde imzalanıp mühürlenecek. Çünkü eski gönençlerine kavuşturacağım onları” diyor RAB.
Za a sayi filaye da azurfa, a kuma sa hannu a takardan ciniki, a liƙe a kuma shaida a yankin Benyamin, a ƙauyukan kewayen Urushalima, a garuruwan Yahuda da kuma a garuruwan ƙasar tudu, na yammancin gindin dutse da na Negeb, domin zan maido da wadatarsu, in ji Ubangiji.”

< Yeremya 32 >