< Yeşaya 65 >

1 “Beni sormayanlara göründüm, Aramayanlar beni buldu. Adımla anılmayan bir ulusa, ‘Buradayım, buradayım’ dedim.
“Na bayyana kaina ga waɗanda ba su tambaye ni ba; ina samuwa ga waɗanda ba su neme ni ba. Ga al’ummar da ba tă kira bisa sunana ba, Na ce, ‘Ga ni, ga ni.’
2 Kötü yolda yürüyen, Kendi tasarılarının ardınca giden Asi bir halka Bütün gün ellerimi uzatıp durdum.
Dukan yini ina miƙa hannuwana ga mutane masu tayarwa, waɗanda suna tafiya a hanyoyin da ba su da kyau, suna bin tunaninsu,
3 O halk ki, bahçelerde kurban keserek, Tuğlalar üzerinde buhur yakarak Gözümün içine baka baka boyuna öfkelendirir beni.
mutanen da suna cin gaba da tsokanata a fuskata, suna miƙa hadayu a gonaki suna ƙone turare a bagadan tubali;
4 Mezarlıkta oturur, Gizli yerlerde geceler, Domuz eti yerler; Kaplarında haram et var.
suna zama a kaburbura su kwana suna yin asirtattun ayyuka; suna cin naman aladu, tukwanensu kuma sun cika da nama marar tsabta;
5 Birbirlerine, ‘Uzak dur, yaklaşma’ derler, ‘Çünkü ben senden daha kutsalım.’ Böyleleri burnumda duman, Bütün gün yanan ateştir.
suna cewa, ‘Ku tsaya a can; kada ku yi kusa da ni, gama na fi ku tsarki!’ Irin mutanen nan hayaƙi ne a hancina, wuta kuma da take cin gaba da ci dukan yini.
6 “Bakın, yanıt önümde yazılı duruyor. Susmayacak, suçlarının karşılığını vereceğim. Onların da atalarının da suçlarının cezasını Başlarına getireceğim” diyor RAB. “Çünkü dağların üzerinde buhur yaktılar, Tepelerin üzerinde beni aşağıladılar. Bu nedenle eskiden yaptıklarının karşılığını Başlarına getireceğim.”
“Ga shi, yana nan a rubuce a gabana cewa ba zan ƙyale ba, zan yi cikakken ramuwa; zan yi ramuwa a cinyoyinsu
7
saboda zunubanku da kuma zunuban kakanninku,” in ji Ubangiji. “Gama sun ƙone turare a kan duwatsu suka kuma ƙazantar da ni a kan tuddai, zan yi musu awo in zuba a cinyoyinsu cikakken ramuwa saboda ayyukansu na dā.”
8 RAB diyor ki, “Taneleri sulu salkımı görünce, Halk, ‘Salkımı yok etmeyin, bereket onda’ diyor. Kullarımın hatırı için ben de öyle yapacağım, Onların hepsini yok etmeyeceğim.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kamar sa’ad da ruwan’ya’yan itace yana samuwa a cikin tarin’ya’yan inabi mutane kuma su ce, ‘Kada a lalace shi, har yanzu akwai abu mai kyau a ciki,’ haka nan zan yi a madadin bayina; ba zan hallaka su duka ba.
9 Yakup soyunu sürdürecek, Dağlarımı miras alacak olanları Yahuda soyuna bırakacağım. Seçtiklerim oraları miras alacak, Kullarım orada yaşayacak.
Zan fitar da zuriyar Yaƙub, daga Yahuda kuma waɗanda za su mallaki duwatsuna; zaɓaɓɓun mutanena za su gāje su, a can kuma bayina za su zauna.
10 Şaron bana yönelen halkımın sürülerine ağıl, Akor Vadisi sığırlarına barınak olacak.
Sharon zai zama wurin kiwo don shanu, Kwarin Akor kuma wurin hutun garkuna, domin mutanena da suke nemana.
11 “Ama sizler, RAB'bi terk edenler, Kutsal dağımı unutanlar, Talih ilahına sofra kuranlar, Kısmet ilahına karışık şarap sunanlar,
“Amma game da ku waɗanda kuka yashe Ubangiji kuka manta da dutsena mai tsarki kuwa, ku da kuka shimfiɗa tebur don sa’a kuka kuma cika darunan ruwan inabin da aka dama don Ƙaddara,
12 Ben de sizi kılıca kısmet edeceğim, Boğazlanmak üzere eğileceksiniz hepiniz. Çünkü çağırdığımda yanıt vermediniz, Konuştuğumda dinlemediniz; Gözümde kötü olanı yaptınız, Hoşlanmadığımı seçtiniz.”
zan ƙaddara ku ga kaifin takobi, dukanku kuma za ku sunkuya wa mai yanka; gama na yi kira amma ba ku amsa ba, na yi magana amma ba ku saurara ba. Kuka aikata mugunta a gabana kuka kuma zaɓi abin da ba na jin daɗi.”
13 Bu yüzden Egemen RAB diyor ki, “Bakın, kullarım yemek yiyecek, Ama siz aç kalacaksınız. Kullarım içecek, Ama siz susuz kalacaksınız. Kullarım sevinecek, Ama sizin yüzünüz kızaracak.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Bayin za su ci, amma ku za ku ji yunwa; bayina za su sha, amma ku za ku ji ƙishi; bayina za su yi farin ciki amma ku za ku sha kunya.
14 Kullarım mutluluk içinde ezgiler söyleyecek, Ama siz yürek acısından feryat edecek, Ezik bir ruhla haykıracaksınız.
Bayina za su rera da farin cikin zukatansu, amma ku za ku yi kuka daga wahalar zuciya ku kuma yi kururuwa da karayar zuci.
15 Adınız seçtiklerimin ağzında ancak lanet olarak kalacak. Egemen RAB sizi öldürecek, Ama kullarına başka bir ad verecek.
Za ku bar sunanku ga zaɓaɓɓuna yă zama abin la’antarwa; Ubangiji Mai Iko Duka zai kashe ku, amma ga bayina zai ba su wani suna.
16 Öyle ki, ülkede kim bereket istese Sadık Tanrı'dan isteyecek; Ülkede kim ant içse, Sadık Tanrı üzerine ant içecek. Çünkü geçmiş sıkıntılar unutulup Gözümden saklanacak.”
Duk wanda zai roƙi albarka a cikin ƙasar zai yi haka da gaskiyar Allah; wanda zai yi rantsuwa a cikin ƙasar zai rantse da gaskiyar Allah. Gama za a manta da wahalolin baya a kuma ɓoye su daga idanuna.
17 “Çünkü bakın, yeni bir yeryüzü, Yeni bir gök yaratmak üzereyim; Geçmiştekiler anılmayacak, akla bile gelmeyecek.
“Ga shi, na halicci sabuwar sama da kuma sabuwar duniya. Abubuwa na dā za a manta da su, ba kuwa za a ƙara tuna da su ba.
18 Yaratacaklarımla sonsuza dek sevinip coşun; Çünkü Yeruşalim'i coşku, Halkını sevinç kaynağı olarak yaratacağım.
Amma ku yi murna ku kuma yi farin ciki har abada a abin da na halitta, gama zan halicci Urushalima ta zama abin murna mutanenta kuwa abin farin ciki.
19 Yeruşalim için sevinecek, Halkım için coşacağım. Orada ağlayış ve feryat duyulmayacak artık.
Zan yi farin ciki a kan Urushalima in kuma yi murna saboda mutanena; a can ba za a ƙara jin karar makoki da na kuka ba.
20 Orada birkaç gün yaşayıp ölen bebekler olmayacak, Yaşını başını almadan kimse ölümü tatmayacak. Yüz yaşında ölen genç, Yüz yaşına basmayan kişi lanetli sayılacak.
“A cikinta ba za a ƙara jin jariri ya rayu na’yan kwanaki kawai ba, ko kuwa wani tsohon da bai cika kwanakinsa ba; duk wanda ya mutu yana da shekaru ɗari za a ce ya mutu a kurciya ne kawai; duk wanda bai kai ɗari ba za a ɗauka la’antacce ne.
21 Evler yapıp içlerinde yaşayacak, Bağlar dikip meyvesini yiyecekler.
Za su gina gidaje su kuma zauna a cikinsu; za su yi shuki a gonakin inabi su kuma ci’ya’yansu.
22 Yaptıkları evlerde başkası oturmayacak, Diktikleri bağın meyvesini başkası yemeyecek. Çünkü halkım ağaçlar gibi uzun yaşayacak, Seçtiklerim, elleriyle ürettiklerinin tadını çıkaracaklar.
Ba za su ƙara gina gidaje waɗansu kuma su zauna a cikinsu ba, ko su yi shuki waɗansu kuma su ci ba. Gama kamar yadda kwanakin itace suke, haka kwanakin mutanena za su kasance; zaɓaɓɓuna za su daɗe suna jin daɗin ayyukan hannuwansu.
23 Emek vermeyecekler boş yere, Felakete uğrayan çocuklar doğurmayacaklar. Çünkü kendileri de çocukları da RAB'bin kutsadığı soy olacak.
Ba za su yi wahala a banza ba ko su haifi’ya’yan da aka ƙaddara da rashin sa’a; gama za su zama mutanen da Ubangiji ya yi wa albarka, su da zuriyarsu tare da su.
24 Onlar bana yakarmadan yanıt verecek, Daha konuşurlarken işiteceğim onları.
Kafin su yi kira zan amsa; yayinda suke cikin magana zan ji.
25 Kurtla kuzu birlikte otlayacak, Aslan sığır gibi saman yiyecek. Yılanın yiyeceğiyse toprak olacak. Kutsal dağımın hiçbir yerinde Kimse zarar vermeyecek, yok etmeyecek.” Böyle diyor RAB.
Kyarketai da’yan raguna za su ci abinci tare, zaki kuma zai ci buɗu kamar yadda shanu suke yi, amma ƙura ce za tă zama abincin maciji. Ba za su ƙara cuci ko su yi ɓarna a kan dukan dutsena mai tsarki ba,” in ji Ubangiji.

< Yeşaya 65 >