< Romarbrevet 9 >

1 Jag säger sanningen i Christo, och ljuger icke; som mitt samvete bär mig der vittne till i dem Helga Anda;
Ina faɗin gaskiya a cikin Kiristi ba ƙarya nake yi ba, lamirina ya tabbatar da wannan a cikin Ruhu Mai Tsarki.
2 Att jag hafver ena stora sorg, och idkeliga pino i mitt hjerta.
Ina da baƙin ciki mai yawa da kuma rashin kwanciyar rai marar ƙarewa a zuciyata.
3 Ty jag hafver sjelfver önskat mig bortkastad ifrå Christo, för mina bröders skull, som mig köttsliga skylde äro;
Gama da so na ne, sai a la’anta ni a kuma raba ni da Kiristi saboda’yan’uwana, waɗannan na kabilata,
4 Hvilke äro af Israel, hvilkom barnaskapet tillhörer, och härligheten, och förbundet, och lagen, och Gudstjensten, och löften;
mutanen Isra’ila. Su ne Allah ya mai da su’ya’yansa, ya bayyana musu ɗaukakarsa, ya ba su alkawarinsa da Dokarsa, ya nuna musu hanyar sujada ta gaske, ya kuma ba su sauran alkawura.
5 Hvilkas äro fäderna, der Christus af födder är, på köttsens vägnar; hvilken är Gud öfver all ting, lofvad evinnerliga. Amen. (aiōn g165)
Kakannin-kakannin nan kuma nasu ne, Kiristi kuma, ta wurin zamansa mutum, na kabilarsu ne. Yabo ya tabbata ga Allah har abada, shi da yake bisa kome! Amin. (aiōn g165)
6 Detta säger jag icke fördenskull, att Guds ord äro omintet vorden; ty de äro icke alle Israeliter, som äro af Israel;
Ba cewa maganar Allah ta kāsa ba ne. Gama ba duk waɗanda suke zuriyar Isra’ila ne suke Isra’ila na gaske ba.
7 Icke äro de heller alle söner, att de äro Abrahams säd; utan i Isaac skall dig kallas säden;
Ba kuwa don su zuriyarsa ne dukansu suka zama’ya’yan Ibrahim ba. A maimako, “Ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.”
8 Det är: Icke äro de Guds barn, som äro barn efter köttet, utan de som äro barn efter löftet, de varda räknade för säd.
Ana iya cewa zaman zuriyar Ibrahim, ba shi ne zama’ya’yan Allah ba, a’a, zuriya ta alkawarin nan su ne ake lasaftawa zuriyar Ibrahim.
9 Ty detta är löftesordet: Jag skall komma i denna tiden; och Sara skall hafva en son.
Ga yadda aka yi alkawarin nan, “A ƙayyadadden lokaci zan dawo, Saratu kuma za tă haifi ɗa.”
10 Och icke allenast det; utan ock Rebecka vardt en gång hafvandes af Isaac, vårom fader.
Ba ma haka kaɗai ba,’ya’yan Rifkatu suna da mahaifi guda ne, wato, mahaifinmu Ishaku.
11 Ty förr än barnen voro född, och hade hvarken godt eller ondt gjort (på det Guds uppsåt skulle blifva ståndandes efter utkorelsen, icke för gerningarnas skull, utan af kallarens nåde),
Duk da haka, tun ba a haifi tagwayen nan ba, balle su yi wani abu mai kyau ko marar kyau don nufin Allah bisa ga zaɓensa ya tabbata, ba ga aikin lada ba, sai dai ga kiransa,
12 Vardt denne sagdt: Den större skall tjena dem mindre;
ba ta wurin ayyuka ba sai dai ta wurin shi wanda ya kira, aka faɗa mata cewa, “Babban zai bauta wa ƙaramin.”
13 Såsom skrifvet är: Jacob älskade jag men Esau hatade jag.
Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Yaƙub ne na so, amma Isuwa ne na ƙi.”
14 Hvad vilje vi då säga? Är Gud orättfärdig? Bort det.
Me za mu ce ke nan? Allah marar adalci ne? Sam, ko kaɗan!
15 Ty han säger till Mosen: Hvilkom jag är nådelig, honom är jag nådelig; och öfver hvilken jag förbarmar mig, öfver honom förbarmar jag mig.
Gama ya ce wa Musa, “Zan nuna jinƙai ga wanda zan nuna jinƙai, zan kuma ji tausayin wanda zan ji tausayi.”
16 Så står det nu icke till någors mans vilja eller lopp, utan till Guds barmhertighet.
Saboda haka, bai danganta ga sha’awar mutum ko ƙoƙarinsa ba, sai dai ga jinƙan Allah.
17 Ty Skriften säger till Pharao: Dertill hafver jag uppväckt dig, att jag skall bevisa mina magt på dig; och att mitt Namn skall varda förkunnadt i all land.
Gama Nassi ya ce wa Fir’auna, “Na ɗaga ka saboda wannan manufa, saboda in nuna ikona a cikinka domin kuma a shaida sunana a duniya duka.”
18 Så förbarmar han nu sig öfver hvem han vill, och hvem han vill, förhärdar han.
Saboda haka Allah yana nuna jinƙai ga wanda yake so, yana kuma taurara zuciyar wanda yake so.
19 Så må du säga till mig: Hvad skyllar han då oss? Ho kan stå emot hans vilja?
Waninku zai iya ce mini, “To, don me har yanzu Allah yake ganin laifinmu? Gama wa zai iya tsayayya da nufinsa?”
20 O menniska, ho äst du som vill träta med Gud? Icke säger det ting, som gjordt är, till sin mästare: Hvi hafver du gjort mig sådana?
Amma wane ne kai, ya mutum, da za ka mayar wa Allah magana? “Ashe, abin da aka gina zai iya ce wa wanda ya gina shi, ‘Don me ka gina ni haka?’”
21 Hafver icke en pottomakare magt att göra af en klimp ett kar till heder, och det andra till vanheder?
Ashe, mai ginin tukwane ba shi da iko yin amfani da yumɓu guda yă gina tukunya domin ayyuka masu daraja da kuma waɗansu don ayyuka marasa daraja?
22 Derföre, då Gud ville låta se vredena, och kungöra sina magt, hafver han med stor tålsamhet lidit vredsens kar, som äro tillredd till fördömelse;
Haka ma aikin Allah yake. Ya so yă nuna fushinsa yă kuma sanar da ikonsa, ya yi haka cikin haƙuri ƙwarai ga waɗanda suka cancanci fushinsa, waɗanda aka shirya domin hallaka?
23 På det han skulle kungöra sina härlighets rikedom på barmhertighetenes kar, som han hafver tillredt till härlighet;
Haka kuma ya so yă sanar da wadatar ɗaukakarsa ga waɗanda suka cancanci jinƙansa, waɗanda ya shirya tun kafin lokaci don ɗaukaka
24 Hvilka han ock kallat hafver, nämliga oss, icke allenast af Judomen, utan ock af Hedningomen;
har da mu ma, mu da ya kira, ba daga cikin Yahudawa kaɗai ba amma har ma daga cikin Al’ummai?
25 Såsom han ock säger genom Oseas: Det som icke var mitt folk, det skall jag kalla mitt folk; och den mig intet kär var, skall jag kalla min kära.
Kamar yadda ya faɗa a Hosiya. “Zan kira su ‘mutanena,’ su da ba mutanena ba; zan kuma kira ta ‘ƙaunatacciyata,’ ita da ba ƙaunatacciyata ba,”
26 Och det skall ske, att der som hafver varit sagdt till dem: I ären icke mitt folk; der skola de varda kallade lefvandes Guds barn.
kuma, “Zai zama cewa a daidai inda aka ce musu, ‘Ku ba mutanena ba,’ za a ce da su, ‘’ya’yan Allah mai rai.’”
27 Men Esaias ropar för Israel: Om talet på Israels barn än vore som sanden i hafvet, så skola dock de igenlefde varda salige.
Ishaya ya ɗaga murya game da Isra’ila ya ce, “Ko da yake yawan Isra’ilawa yana kama da yashi a bakin teku, ragowa ce kaɗai za su sami ceto.
28 Ty han skall väl låta förderfva dem, och dock likväl stilla det förderfvet till rättfärdighet; ty Herren skall stilla förderfvet på jordene.
Gama Ubangiji zai zartar da hukuncinsa a bisan duniya da sauri kuma ba da ɓata lokaci ba.”
29 Och såsom Esaias sade tillförene: Hade icke Herren Zebaoth igenleft oss säd, då hade vi varit såsom Sodoma, och lika som Gomorra.
Yana nan kamar yadda Ishaya ya riga ya faɗa. “Da ba don Ubangiji Maɗaukaki ya bar mana zuriya ba, da mun zama kamar Sodom, da mun kuma zama kamar Gomorra.”
30 Hvad vilje vi då säga? Det säge vi: Hedningarna, som icke farit hafva efter rättfärdighetene, de hafva fått rättfärdigheten; den rättfärdighet menar jag, som af trone kommer.
Me za mu ce ke nan? Ai, Al’ummai da ba su nemi adalci ba, sun same shi, adalcin da yake ta wurin bangaskiya;
31 Men Israel, som for efter rättfärdighetenes lag, kom icke till rättfärdighetenes lag.
amma Isra’ila da suka yi ƙwazo wajen bin Dokar adalci, ba su same shi ba.
32 Hvarföre? Derföre att de icke sökte det af trone, utan såsom af lagsens gerningar; ty de stötte sig på förtörnelsestenen;
Don me? Domin sun yi ƙwazo wajen binta ba ta wurin bangaskiya ba sai dai ta wurin ayyuka. Sun yi tuntuɓe a kan “dutsen sa tuntuɓe.”
33 Såsom skrifvet är: Si, jag lägger i Zion en förtörnelsesten, och ena förargelseklippo: och hvar och en som tror på honom, skall icke komma på skam.
Kamar yadda yake a rubuce, “Ga shi, na sa dutse a Sihiyona da yake sa mutane yin tuntuɓe da kuma dutsen da yake sa su fāɗi wanda kuwa ya dogara gare shi ba zai taɓa shan kunya ba.”

< Romarbrevet 9 >